• English
  • Business News
Friday, November 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Damu Kan Bayyanar Mayakan Kungiyar Ansaru A Yankinmu — Mutanen Birnin Gwari

by Abubakar Abba
2 years ago
Ansaru

Mazauna  Kauyen Kuyello a karamar hukumar Birnin Gwari a jihar Kaduna, sun nuna damuwarsu kan bayyanar ‘yan ta’addar Ansaru a yankunansu. 

An ruwaito cewa, ziyarar bazata a ‘yan kwanan baya da ‘yan Ansarun suka kai akan baburansu a yankunan, hakan ya jefa fargaba a zukatan mazauna yankunan na karamar hukumar.

  • Matashin Dan Kwallon Barcelona Guiu Mai Shekaru 17 Ya Jefa Kwallon Farko A Kungiyar
  • Asalin Kungiyoyin Mayakan Hamas, Hizbullah Da Manufofinsu

Kazalika, an ruwaito cewa, wasu daga cikin mazauna yankunan sun gargadi ‘yan kungiyar ta Ansaru da su fice daga yankunan su.

Bugu da kari, rahotannin sun ce, “‘yan Ansaru na gudanar da ayyukansu a kauyukan Kazage, Unguwar Gwandu, Unguwar Gajere, da kuma tsohon garin Kuyello, inda suke jan ra’ayin matasa suna shiga cikin kungiyar ta Ansaru domin su kara yawan adadin ‘ya’yan kungiyar a karamar hukumar. ”

Wani babba daga cikin mazauna kauyen, Malam Muhammadu Kuyello, ya tabbatar da cewa, ‘yan Ansaru sun shiga cikin Kuyallo ta hanyar garin Dan Auta, inda suka wuce, ba tare da sun ce wa kowa uffan ba.

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Kazlika, ya sanar da cewa a yanzu haka, Ansaru sun dauki kimanin matasa 50 na tsohon garin Kuyallo a cikin kungiyarsu, inda kuma suka aurar da ‘yan mata bakwai.

A cewarsa, idan gwamantin jihar ta tura jami’an tsaro zuwa tsohon garin Kuyello, ‘yan kungiyar ba su da wani zabi illa su arce daga garin.

Bugu da kari, wani jagoran matasa a yankin  Baban yara Isa, ya ce, idan har mahukunta ba su kawo dauki ba, mazauna yankin za su yi artabu da ‘yan kungiyar da nufin fatattaksrsu daga yankin.

Ya ce, tuni masu fada aji a yankin suka sanar da mahukunta daban-daban da ke karamar hukumar akan lamarin, inda ya yi kira ga mahukuntan da su gaggauta daukar mataki.

Shi ma shugaban ci gaban masarautar Birnin Gwari (BEPU) Ishaq Kasai, ya tabbatar da lamarin.

Sai dai, kakakin rundunar ‘yansanda na jihar Kaduna ASP Mansir Hassan ya ce, bai da hurumin yin magana akan lamarin.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 
Manyan Labarai

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama
Manyan Labarai

Za Mu Ƙara Ƙaimi Wajen Kai Wa ‘Yan Bindiga Hare-Hare Ta Sama – Hafsan Sojin Sama

November 6, 2025
Next Post
Xi Ya Jaddada Jan Hankalin Ma’aikata Da Su Shiga Aikin Farfado Da Kasa

Xi Ya Jaddada Jan Hankalin Ma’aikata Da Su Shiga Aikin Farfado Da Kasa

LABARAI MASU NASABA

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

An Yi Taron Kaddamar Da Tsarin Kawancen Kafafen Watsa Labarun Kasashe Masu Tasowa Da Dandalin Yada Labarai Na Bidiyo Karo Na 13 A Xi’an

November 6, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

CMG Ya Kaddamar Da Wasu Tashoshin Talabijin Uku A Dandalin FAST

November 6, 2025
Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

Baje Kolin CIIE Ya Bayar Da Tabbaci Ga Duniya

November 6, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

Gwamnatin Tarayya Ta Amince da Gina Sabbin Gidaje Ga Alƙalai, Da Samar Da Ruwa A  FCT

November 6, 2025
Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

Manufofin Sin Na Yaki Da Sauyin Yanayi: Gani Ya Kori Ji

November 6, 2025
Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

Shugaba Xi Ya Jaddada Bukatar Gina Ingantaccen Yankin Ciniki Cikin ’Yanci Na Tashar Ruwa Ta Hainan

November 6, 2025
Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

Amurka Ta Yi Barazanar Ƙwace Kadarorin Ƙungiyoyin Makiyaya A Nijeriya 

November 6, 2025
A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

A Karon Farko An Gabatar Da Ka’idar Kasa Da Kasa Ta Fasahar 5G Mai Amfani Ga Masana’antu

November 6, 2025
Gwamnatin tarayya

Ta’addanci Ba Zai Yi Nasara Ba A Ƙasarmu — Tinubu

November 6, 2025
Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

Bikin Baje Kolin CIIE: Da Abokin Daka Ake Shan Gari

November 6, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.