• English
  • Business News
Thursday, June 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Damu Kan Bayyanar Mayakan Kungiyar Ansaru A Yankinmu — Mutanen Birnin Gwari

by Abubakar Abba
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Mun Damu Kan Bayyanar Mayakan Kungiyar Ansaru A Yankinmu — Mutanen Birnin Gwari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mazauna  Kauyen Kuyello a karamar hukumar Birnin Gwari a jihar Kaduna, sun nuna damuwarsu kan bayyanar ‘yan ta’addar Ansaru a yankunansu. 

An ruwaito cewa, ziyarar bazata a ‘yan kwanan baya da ‘yan Ansarun suka kai akan baburansu a yankunan, hakan ya jefa fargaba a zukatan mazauna yankunan na karamar hukumar.

  • Matashin Dan Kwallon Barcelona Guiu Mai Shekaru 17 Ya Jefa Kwallon Farko A Kungiyar
  • Asalin Kungiyoyin Mayakan Hamas, Hizbullah Da Manufofinsu

Kazalika, an ruwaito cewa, wasu daga cikin mazauna yankunan sun gargadi ‘yan kungiyar ta Ansaru da su fice daga yankunan su.

Bugu da kari, rahotannin sun ce, “‘yan Ansaru na gudanar da ayyukansu a kauyukan Kazage, Unguwar Gwandu, Unguwar Gajere, da kuma tsohon garin Kuyello, inda suke jan ra’ayin matasa suna shiga cikin kungiyar ta Ansaru domin su kara yawan adadin ‘ya’yan kungiyar a karamar hukumar. ”

Wani babba daga cikin mazauna kauyen, Malam Muhammadu Kuyello, ya tabbatar da cewa, ‘yan Ansaru sun shiga cikin Kuyallo ta hanyar garin Dan Auta, inda suka wuce, ba tare da sun ce wa kowa uffan ba.

Labarai Masu Nasaba

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

Kazlika, ya sanar da cewa a yanzu haka, Ansaru sun dauki kimanin matasa 50 na tsohon garin Kuyallo a cikin kungiyarsu, inda kuma suka aurar da ‘yan mata bakwai.

A cewarsa, idan gwamantin jihar ta tura jami’an tsaro zuwa tsohon garin Kuyello, ‘yan kungiyar ba su da wani zabi illa su arce daga garin.

Bugu da kari, wani jagoran matasa a yankin  Baban yara Isa, ya ce, idan har mahukunta ba su kawo dauki ba, mazauna yankin za su yi artabu da ‘yan kungiyar da nufin fatattaksrsu daga yankin.

Ya ce, tuni masu fada aji a yankin suka sanar da mahukunta daban-daban da ke karamar hukumar akan lamarin, inda ya yi kira ga mahukuntan da su gaggauta daukar mataki.

Shi ma shugaban ci gaban masarautar Birnin Gwari (BEPU) Ishaq Kasai, ya tabbatar da lamarin.

Sai dai, kakakin rundunar ‘yansanda na jihar Kaduna ASP Mansir Hassan ya ce, bai da hurumin yin magana akan lamarin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Boko HaramKungiyar AnsaruMayakan ISWAP
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kiran Da Kasar Sin Ta Yi Na Samar Da Zaman Lafiya Tsakanin Isra’ila Da Falasdinu Wani Buri Ne Na Duniya Baki Daya

Next Post

Xi Ya Jaddada Jan Hankalin Ma’aikata Da Su Shiga Aikin Farfado Da Kasa

Related

Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

46 minutes ago
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 
Manyan Labarai

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

6 hours ago
An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja
Manyan Labarai

An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

7 hours ago
Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa
Manyan Labarai

Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

9 hours ago
Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa
Manyan Labarai

Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa

9 hours ago
Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano
Manyan Labarai

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

20 hours ago
Next Post
Xi Ya Jaddada Jan Hankalin Ma’aikata Da Su Shiga Aikin Farfado Da Kasa

Xi Ya Jaddada Jan Hankalin Ma’aikata Da Su Shiga Aikin Farfado Da Kasa

LABARAI MASU NASABA

Hukumar kashe gobara

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

June 5, 2025
Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus

Gwamnatin Tarayya Za Ta Tallafa Wa Yekuwar Rigakafin Cutar Ƙyandar Jamus

June 5, 2025
Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno

Sojoji Sun Daƙile Harin Ƴan Ta’adda, Sun Kashe Wasu Da Yawa A Borno

June 5, 2025
Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 2 Sun Sace 2 A Wurin Haƙar Ma’adanai

Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutum 2 Sun Sace 2 A Wurin Haƙar Ma’adanai

June 5, 2025
Trump Ya Umarci A Bincika Lafiyar Ƙwaƙwalwar Tsohon Shugaban Ƙasa Biden Yayin Mulkinsa

Trump Ya Umarci A Bincika Lafiyar Ƙwaƙwalwar Tsohon Shugaban Ƙasa Biden Yayin Mulkinsa

June 5, 2025
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

June 5, 2025
An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

June 5, 2025
Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

June 5, 2025
Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa

Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa

June 5, 2025
Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Muhammadu Iliyasu Bashir A Matsayin Sarkin Gwandu

Kotun Ƙoli Ta Tabbatar Da Muhammadu Iliyasu Bashir A Matsayin Sarkin Gwandu

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.