• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Dana Wa Wasu Gwamnoni 3 Tarko Kan Wasu Makudan Kudade – EFCC 

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Mun Dana Wa Wasu Gwamnoni 3 Tarko Kan Wasu Makudan Kudade – EFCC 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnonin Jihohi uku da ke kan karagar mulki sun shiga komar EFCC kan yunkurin karkatar da kudade ta hanyar biyan albashin ma’aikatan jihohinsu.

Shugaban Hukumar Yaki da Yi wa Tattalin Arziki Ta’annati, Abdulrasheed Bawa, ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis.

  • Sabon Ci Gaban Sin Ya Samar Wa Afirka Sabuwar Dama
  • Gwamnatin Kano Ta Gargadi Masu Sayen Fili A Jikin BUK

Bawa, wanda bai bayyana sunayen gwamnonin ba, ya ce biyu daga cikinsu ‘yan Arewa ne, yayin da na ukun ya fito ne daga kudancin kasar nan.

Ya ce bayanan da hukumar ta samu sun nuna cewa gwamnonin uku sun kammala shirye-shiryen shigar da kudaden a cikin tsarin biyan albashin ma’aikatan jiharsu.

“Bari na fada muku wani abu; bayanin da nake da shi jiya kuma zan so ku dauki wannan abu da muhimmanci. Tuni dai wasu gwamnonin jihohin suna da wasu makudan kudaden da aka boye a gidaje daban-daban, sauran kuma suna kokarin biyan kudin cikin tsarin albashi a jiharsu,”

Labarai Masu Nasaba

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

kamar yadda ya shaida wa Daily Trust.

Da aka yi masa tambayoyi kan ko hukumar za ta gayyaci gwamnonin, Bawa ya ce suna sa ido sosai a kan su.

“Ban san yadda suke son cimma hakan ba amma dole ne mu hana su yin hakan. Muna aiki, har yanzu ba su biya albashin da tsabar kudi ba amma abu ne mai matukar mamaki,” in ji shi, inda ya ce matakin ya sabawa sashe na 2 na dokar hana barnar kudade.

“Dokar ta fito karara game da hada-hadar kudi. Duk wanda zai ci gaba da duk wata mu’amalar kudi a matsayinsa na mutum, idan ba ta hanyar hada-hadar kudi ba, to bai kamata ya wuce miliyan 5 ba, kuma idan ya kai sama da haka ya zama laifi a gare ku.

“Eh, na yarda albashin bai kai haka ba amma me ya sa kwatsam suka koma biyan mutane albashi ta ta hannu a maimakon asusun ajiyarsu na banki?

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da Babban Bankin Nijeriya ke yunkurin sake fasalin takardun kudi na N200, N500 da N1000.

A ranar 26 ga watan Oktoba ne CBN ya sanar da cewa za a sake fasalin kudin kasar nan don magance matsaloli da dama da ke da illa ga tattalin arzikin Nijeriya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BawaCBNEFCCGwamnoniSauya Fasalin Naira
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sabon Ci Gaban Sin Ya Samar Wa Afirka Sabuwar Dama

Next Post

Ambaliya: Tallafin NEDC Ya Zo A Kan Gaba A Arewa Maso Gabas

Related

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram
Manyan Labarai

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

12 hours ago
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce
Manyan Labarai

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

13 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Tinubu Zai Ziyarci Jos Domin Halartar Jana’izar Mahaifiyar Shugaban Jam’iyyar APC Na Ƙasa

1 day ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

PENGASSAN Ta Yi Watsi Da Tayin Dangote Na Biyan Ma’aikata Albashin Shekaru 5 Ba Tare Da Yin Aiki Ba

2 days ago
NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja
Manyan Labarai

NAFDAC Ta Rufe Manyan Shaguna 2 Na Ƴan China A Abuja

2 days ago
Nijeriya A Shekara 65: Kwan-gaba Kwan-baya A Sha’anin Tsaro Da Siyasa Da Zamantakewa
Manyan Labarai

Nijeriya A Shekara 65: Kwan-gaba Kwan-baya A Sha’anin Tsaro Da Siyasa Da Zamantakewa

2 days ago
Next Post
Ambaliya: Tallafin NEDC Ya Zo A Kan Gaba A Arewa Maso Gabas

Ambaliya: Tallafin NEDC Ya Zo A Kan Gaba A Arewa Maso Gabas

LABARAI MASU NASABA

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

Me Yarjejeniyar Kawo Karshen Yakin Gaza Da Amurka Ta Tsara Ta Kunsa?

October 4, 2025
Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

Firaministan Pakistan: Shugaba Xi Jinping Shugaba Ne Mai Hangen Nesa

October 4, 2025
Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

Kokarin Da ‘Yan Wasan Nijeriya Suka Yi Wajen Lashe Kyautar Ballon d’Or

October 4, 2025
Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

Jonathan Ya Ƙaryata Batun Danganta Buhari Da Boko Haram

October 4, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

Sin Ta Yi Kira Ga Kasa Da Kasa Su Ki Amincewa Da Takunkumin Bangare Daya

October 4, 2025
Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

Kasar Sin Ta Soki Matakan Harajin Amurka “Na Ramuwa” A WTO

October 4, 2025
Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

Jami’ar Nsukka Ta Ce Shaidar Digirin Ministan Fasaha, Uche Nnaji, Ta Bogi Ce

October 4, 2025
Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

Jami’in MDD: Shawarar GGI Za Ta Jagoranci Duniya Zuwa Samun Kyakkyawar Makoma Mai Cike Da Adalci

October 4, 2025
Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

Nijeriya Ta Samu Kwarin Gwiwar Zuwa Kofin Duniya

October 4, 2025
Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

Bayan Janyewar Sojojin Kamaru, Boko Haram Sun Dawo Kashe-Kashe A Borno

October 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.