• English
  • Business News
Tuesday, October 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Dana Wa Wasu Gwamnoni 3 Tarko Kan Wasu Makudan Kudade – EFCC 

by Sadiq
3 years ago
EFCC

Gwamnonin Jihohi uku da ke kan karagar mulki sun shiga komar EFCC kan yunkurin karkatar da kudade ta hanyar biyan albashin ma’aikatan jihohinsu.

Shugaban Hukumar Yaki da Yi wa Tattalin Arziki Ta’annati, Abdulrasheed Bawa, ne ya bayyana hakan a ranar Alhamis.

  • Sabon Ci Gaban Sin Ya Samar Wa Afirka Sabuwar Dama
  • Gwamnatin Kano Ta Gargadi Masu Sayen Fili A Jikin BUK

Bawa, wanda bai bayyana sunayen gwamnonin ba, ya ce biyu daga cikinsu ‘yan Arewa ne, yayin da na ukun ya fito ne daga kudancin kasar nan.

Ya ce bayanan da hukumar ta samu sun nuna cewa gwamnonin uku sun kammala shirye-shiryen shigar da kudaden a cikin tsarin biyan albashin ma’aikatan jiharsu.

“Bari na fada muku wani abu; bayanin da nake da shi jiya kuma zan so ku dauki wannan abu da muhimmanci. Tuni dai wasu gwamnonin jihohin suna da wasu makudan kudaden da aka boye a gidaje daban-daban, sauran kuma suna kokarin biyan kudin cikin tsarin albashi a jiharsu,”

LABARAI MASU NASABA

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

kamar yadda ya shaida wa Daily Trust.

Da aka yi masa tambayoyi kan ko hukumar za ta gayyaci gwamnonin, Bawa ya ce suna sa ido sosai a kan su.

“Ban san yadda suke son cimma hakan ba amma dole ne mu hana su yin hakan. Muna aiki, har yanzu ba su biya albashin da tsabar kudi ba amma abu ne mai matukar mamaki,” in ji shi, inda ya ce matakin ya sabawa sashe na 2 na dokar hana barnar kudade.

“Dokar ta fito karara game da hada-hadar kudi. Duk wanda zai ci gaba da duk wata mu’amalar kudi a matsayinsa na mutum, idan ba ta hanyar hada-hadar kudi ba, to bai kamata ya wuce miliyan 5 ba, kuma idan ya kai sama da haka ya zama laifi a gare ku.

“Eh, na yarda albashin bai kai haka ba amma me ya sa kwatsam suka koma biyan mutane albashi ta ta hannu a maimakon asusun ajiyarsu na banki?

Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da Babban Bankin Nijeriya ke yunkurin sake fasalin takardun kudi na N200, N500 da N1000.

A ranar 26 ga watan Oktoba ne CBN ya sanar da cewa za a sake fasalin kudin kasar nan don magance matsaloli da dama da ke da illa ga tattalin arzikin Nijeriya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato
Manyan Labarai

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

October 28, 2025
EFCC
Manyan Labarai

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
Next Post
Ambaliya: Tallafin NEDC Ya Zo A Kan Gaba A Arewa Maso Gabas

Ambaliya: Tallafin NEDC Ya Zo A Kan Gaba A Arewa Maso Gabas

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

Tsohon Kwamishina Ya Zargi Gwamnatin Kano Da Sayar Da Filin Makaranta Kan Miliyan 100

October 28, 2025
An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

’Yansanda Sun Ƙaryata Rahoton Ƙone Gidan Shugaban Jam’iyyar PDP A Bauchi

October 28, 2025
Mutum 18 Sun Mutu, 40 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kebbi 

An Kashe Mutum 10 A Harin Ramuwar Gayya A Jihar Kebbi

October 28, 2025
Ganduje Na Kara Shan Matsin Lamba A Kan Ya Sauka

Zargin Almundahana: An Ɗage Shari’ar  Ganduje Da Matarsa Saboda Rashin Miƙa Takardu

October 28, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

Sojoji Sun Kashe Masu Yi Wa ISWAP 4 Safarar Makamai A Borno

October 28, 2025
EFCC

APC Ta Yi Barazanar Dakatar Duk Kwamishinan Da Bai Sanya Irin Hular Tinubu Ba

October 27, 2025
An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

An Yi Taron Tattaunawa Tsakanin Kasa Da Kasa A Amurka

October 27, 2025
Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

Wakilan Sin Da Na Amurka Sun Yi Tattaunawa Mai Ma’ana Da Zurfi Da Kuma Amfani

October 27, 2025
Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

Ribar Manyan Masana’antun Kasar Sin Ta Karu Da Kashi 3.2 Cikin Dari A Watanni Tara Na Farkon Bana

October 27, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.