• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Kusa Janye Yajin Aikin Watanni 8 – ASUU 

bySadiq
3 years ago
ASUU

Shugaban kungiyar malaman jami’o’i (ASUU), Farfesa Emmanuel Osodeke, ya ce nan ba da dadewa ba kungiyar za ta janye yajin aikin da ta kwashe watanni takwas tana yi. 

Osodeke ya bayyana haka ne a wani taro da suka yi da shugabannin majalisar wakilai a ranar Litinin a Abuja.

  • Ka’idar Sin Daya Tilo A Duniya Ke Tabbatar Da Kwanciyar Hankali A Mashigin Tekun Taiwan
  • Yawan Jama’ar Sin Na Ci Gaba Da Karuwa Kana Yanayin Aikin Yi Bai Sauya Ba

Ya ce daga abin da kungiyar ta gani a wurin taron “akwai alamun nasara. ”

“A wannan karon ana fatan ba za a samu wasu mutane ko kungiya da za su haifar da al’amuran da za su sa kungiyar ta shiga cikin wani mawuyacin hali,” in ji shi.

Ya kuma yi fatan cewa shiga tsakani da shugabannin majalisar za su yi shi ne na karshe saboda dalibai, inda ya kara da cewa fafutukar da ASUU ta yi na neman tsarin ilimi da jami’o’i ne a kasar nan.

LABARAI MASU NASABA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

“Muna fatan nan da ‘yan kwanaki masu zuwa za mu kawo karshen wannan yajin aikin.

Osodeke ya ce “Muna son samun tsarin da sake lissafin ya isa ya jawo malamai a duk duniya zuwa jami’o’inmu.”

Ya ce ya kamata kuma a rika biyan jami’o’in Nojeriya da kudi mai tsoka domin jawo hankalin daliban kasashen waje, yayin da ya nuna damuwa kan wasu nagartattun malamai da ke barin kasar.

“Mu ne manyan Afirka kuma dole ne mu rayu tare da wannan.

Ya ci gaba da cewa, “Muna godiya ga shugaban majalisar kan wannan shiga tsakani kuma dole ne mu hada kai domin kowane dan Nijeriya ya yi alfahari da jami’o’in da muke da su.”

Ya ce bai kamata yajin aikin ya wuce makonni biyu ba, “da majalisar dokokin kasar ta sa baki kafin yanzu”.

Kakakin majalisar wakilai Femi Gbajabiamila, ya ce tsoma bakin da shugabannin majalisar suka yi ya yi tasiri.

Gbajabiamila ya kuma ce ganawar da suka yi da shugaban kasa Muhammadu Buhari ta yi nisa.

Ya ce za a sanar da mataki da aka yanke ga kungiyar da jama’a a ranar 11 ga Oktoba.

Ya ce shugabannin majalisar sun samu damar tabbatar da cewa an samar da dukkan bukatun ASUU na farfado da albashi da sauransu a kasafin kudin 2023.

Ya ce an saka Naira biliyan 470 a cikin kasafin kudin 2023 don biyan bukatar ASUU.

“An warware matsalar UTA kamar yadda gwamnati da ASUU suka amince kuma dukkansu za su zauna su amince da sanya duk wasu abubuwan da ASUU ke bukata a tsarin biyan kudin IPPIS.

“Na yi imani mun rufe kasa, kuma shi ne ainihin abin da muka amince da shi.

“Muna ASUU ta janye yajin aikin yau da fatan nan da kwanaki biyu masu zuwa.

“Muna gode wa ASUU saboda amsa kira a duk lokacin da muka kira su.

“Mun hadu a ofishina don tattaunawa. Mun yi haka ne don kare bukatar dalibanmu,” in ji shi.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi
Manyan Labarai

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Next Post
Kwastam Ta Kama Haramtattun Kayayyaki Na Sama Da Naira Miliyan 200 A Bauchi 

Kwastam Ta Kama Haramtattun Kayayyaki Na Sama Da Naira Miliyan 200 A Bauchi 

LABARAI MASU NASABA

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version