• English
  • Business News
Wednesday, July 2, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Kusa Janye Yajin Aikin Watanni 8 – ASUU 

by Sadiq
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Mun Kusa Janye Yajin Aikin Watanni 8 – ASUU 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kungiyar malaman jami’o’i (ASUU), Farfesa Emmanuel Osodeke, ya ce nan ba da dadewa ba kungiyar za ta janye yajin aikin da ta kwashe watanni takwas tana yi. 

Osodeke ya bayyana haka ne a wani taro da suka yi da shugabannin majalisar wakilai a ranar Litinin a Abuja.

  • Ka’idar Sin Daya Tilo A Duniya Ke Tabbatar Da Kwanciyar Hankali A Mashigin Tekun Taiwan
  • Yawan Jama’ar Sin Na Ci Gaba Da Karuwa Kana Yanayin Aikin Yi Bai Sauya Ba

Ya ce daga abin da kungiyar ta gani a wurin taron “akwai alamun nasara. ”

“A wannan karon ana fatan ba za a samu wasu mutane ko kungiya da za su haifar da al’amuran da za su sa kungiyar ta shiga cikin wani mawuyacin hali,” in ji shi.

Ya kuma yi fatan cewa shiga tsakani da shugabannin majalisar za su yi shi ne na karshe saboda dalibai, inda ya kara da cewa fafutukar da ASUU ta yi na neman tsarin ilimi da jami’o’i ne a kasar nan.

Labarai Masu Nasaba

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara

“Muna fatan nan da ‘yan kwanaki masu zuwa za mu kawo karshen wannan yajin aikin.

Osodeke ya ce “Muna son samun tsarin da sake lissafin ya isa ya jawo malamai a duk duniya zuwa jami’o’inmu.”

Ya ce ya kamata kuma a rika biyan jami’o’in Nojeriya da kudi mai tsoka domin jawo hankalin daliban kasashen waje, yayin da ya nuna damuwa kan wasu nagartattun malamai da ke barin kasar.

“Mu ne manyan Afirka kuma dole ne mu rayu tare da wannan.

Ya ci gaba da cewa, “Muna godiya ga shugaban majalisar kan wannan shiga tsakani kuma dole ne mu hada kai domin kowane dan Nijeriya ya yi alfahari da jami’o’in da muke da su.”

Ya ce bai kamata yajin aikin ya wuce makonni biyu ba, “da majalisar dokokin kasar ta sa baki kafin yanzu”.

Kakakin majalisar wakilai Femi Gbajabiamila, ya ce tsoma bakin da shugabannin majalisar suka yi ya yi tasiri.

Gbajabiamila ya kuma ce ganawar da suka yi da shugaban kasa Muhammadu Buhari ta yi nisa.

Ya ce za a sanar da mataki da aka yanke ga kungiyar da jama’a a ranar 11 ga Oktoba.

Ya ce shugabannin majalisar sun samu damar tabbatar da cewa an samar da dukkan bukatun ASUU na farfado da albashi da sauransu a kasafin kudin 2023.

Ya ce an saka Naira biliyan 470 a cikin kasafin kudin 2023 don biyan bukatar ASUU.

“An warware matsalar UTA kamar yadda gwamnati da ASUU suka amince kuma dukkansu za su zauna su amince da sanya duk wasu abubuwan da ASUU ke bukata a tsarin biyan kudin IPPIS.

“Na yi imani mun rufe kasa, kuma shi ne ainihin abin da muka amince da shi.

“Muna ASUU ta janye yajin aikin yau da fatan nan da kwanaki biyu masu zuwa.

“Muna gode wa ASUU saboda amsa kira a duk lokacin da muka kira su.

“Mun hadu a ofishina don tattaunawa. Mun yi haka ne don kare bukatar dalibanmu,” in ji shi.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ASUUDalibaiMalamaiWatanni 8Yajin Aiki
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ka’idar Sin Daya Tilo A Duniya Ke Tabbatar Da Kwanciyar Hankali A Mashigin Tekun Taiwan

Next Post

Kwastam Ta Kama Haramtattun Kayayyaki Na Sama Da Naira Miliyan 200 A Bauchi 

Related

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano
Manyan Labarai

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

9 hours ago
Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Ta’adda Yellow Danbokolo A Zamfara

14 hours ago
Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata
Manyan Labarai

Barau, Ganduje Da Wasu Sun Isa Madina Don Halartar Jana’izar Aminu Dantata

18 hours ago
Duk Da Farfadowar Darajar Naira, Tsadar Kaya Na Ci Gaba Da Lulawa Sama
Manyan Labarai

Faɗuwar Darajar Naira Ta Sa Bashin Nijeriya Ya Ƙaru Zuwa Naira Tiriliyan 149

20 hours ago
Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC
Manyan Labarai

Haɗakar Jam’iyyun Adawa Ba Ya Ɗaga Mana Hankali – Sabon Shugaban APC

21 hours ago
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa
Manyan Labarai

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

1 day ago
Next Post
Kwastam Ta Kama Haramtattun Kayayyaki Na Sama Da Naira Miliyan 200 A Bauchi 

Kwastam Ta Kama Haramtattun Kayayyaki Na Sama Da Naira Miliyan 200 A Bauchi 

LABARAI MASU NASABA

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

An Dakatar Da Shugaban APC Na Jihar Nasarawa

July 1, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

Tawagar Gwamnatin Tarayya Da Ɗangote Sun Halarci Jana’izar Aminu Ɗantata A Saudiyya

July 1, 2025
An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

An Gudanar Da Bikin Daga Tuta Da Bikin Murnar Cika Shekaru 28 Da Dawowar Yankin HK Karkashin Kasar Sin

July 1, 2025
Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

Ɗantata: Majalisar Dattawa Ta Ɗage Taron Jin Ra’ayin Jama’a A Arewa maso Yamma

July 1, 2025
Kayan Aro Baya Rufe Katara

Kayan Aro Baya Rufe Katara

July 1, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Askarawan Zamfara Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Bindiga, Kacalla Ɗanbokolo Ubangidan Turji

July 1, 2025
Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

Tawagar Likitoci Ta Sin Ta Ba Da Horon Fasahar Likitancin Gargajiya Ta Sin A Nijar

July 1, 2025
Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

Farfesa Haruna Musa Ya Lashe Zaɓen Shugabancin Jami’ar Bayero Ta Kano

July 1, 2025
Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

Fahimtar Sabon Tunani: Yadda Sin Ta Samu Bunkasa A Tarihi Ta Hanyar Juyin Juya Halin Da Take Yi Wa Kanta 

July 1, 2025
An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

An Yi Bikin Kade-Kade Don Taya Murnar Cika Shekaru 104 Da Kafuwar JKS

July 1, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.