ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Kusa Janye Yajin Aikin Watanni 8 – ASUU 

by Sadiq
4 years ago
ASUU

Shugaban kungiyar malaman jami’o’i (ASUU), Farfesa Emmanuel Osodeke, ya ce nan ba da dadewa ba kungiyar za ta janye yajin aikin da ta kwashe watanni takwas tana yi. 

Osodeke ya bayyana haka ne a wani taro da suka yi da shugabannin majalisar wakilai a ranar Litinin a Abuja.

  • Ka’idar Sin Daya Tilo A Duniya Ke Tabbatar Da Kwanciyar Hankali A Mashigin Tekun Taiwan
  • Yawan Jama’ar Sin Na Ci Gaba Da Karuwa Kana Yanayin Aikin Yi Bai Sauya Ba

Ya ce daga abin da kungiyar ta gani a wurin taron “akwai alamun nasara. ”

ADVERTISEMENT

“A wannan karon ana fatan ba za a samu wasu mutane ko kungiya da za su haifar da al’amuran da za su sa kungiyar ta shiga cikin wani mawuyacin hali,” in ji shi.

Ya kuma yi fatan cewa shiga tsakani da shugabannin majalisar za su yi shi ne na karshe saboda dalibai, inda ya kara da cewa fafutukar da ASUU ta yi na neman tsarin ilimi da jami’o’i ne a kasar nan.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

“Muna fatan nan da ‘yan kwanaki masu zuwa za mu kawo karshen wannan yajin aikin.

Osodeke ya ce “Muna son samun tsarin da sake lissafin ya isa ya jawo malamai a duk duniya zuwa jami’o’inmu.”

Ya ce ya kamata kuma a rika biyan jami’o’in Nojeriya da kudi mai tsoka domin jawo hankalin daliban kasashen waje, yayin da ya nuna damuwa kan wasu nagartattun malamai da ke barin kasar.

“Mu ne manyan Afirka kuma dole ne mu rayu tare da wannan.

Ya ci gaba da cewa, “Muna godiya ga shugaban majalisar kan wannan shiga tsakani kuma dole ne mu hada kai domin kowane dan Nijeriya ya yi alfahari da jami’o’in da muke da su.”

Ya ce bai kamata yajin aikin ya wuce makonni biyu ba, “da majalisar dokokin kasar ta sa baki kafin yanzu”.

Kakakin majalisar wakilai Femi Gbajabiamila, ya ce tsoma bakin da shugabannin majalisar suka yi ya yi tasiri.

Gbajabiamila ya kuma ce ganawar da suka yi da shugaban kasa Muhammadu Buhari ta yi nisa.

Ya ce za a sanar da mataki da aka yanke ga kungiyar da jama’a a ranar 11 ga Oktoba.

Ya ce shugabannin majalisar sun samu damar tabbatar da cewa an samar da dukkan bukatun ASUU na farfado da albashi da sauransu a kasafin kudin 2023.

Ya ce an saka Naira biliyan 470 a cikin kasafin kudin 2023 don biyan bukatar ASUU.

“An warware matsalar UTA kamar yadda gwamnati da ASUU suka amince kuma dukkansu za su zauna su amince da sanya duk wasu abubuwan da ASUU ke bukata a tsarin biyan kudin IPPIS.

“Na yi imani mun rufe kasa, kuma shi ne ainihin abin da muka amince da shi.

“Muna ASUU ta janye yajin aikin yau da fatan nan da kwanaki biyu masu zuwa.

“Muna gode wa ASUU saboda amsa kira a duk lokacin da muka kira su.

“Mun hadu a ofishina don tattaunawa. Mun yi haka ne don kare bukatar dalibanmu,” in ji shi.

MASU ALAKA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Next Post
Kwastam Ta Kama Haramtattun Kayayyaki Na Sama Da Naira Miliyan 200 A Bauchi 

Kwastam Ta Kama Haramtattun Kayayyaki Na Sama Da Naira Miliyan 200 A Bauchi 

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.