ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, June 5, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Kusa Janye Yajin Aikin Watanni 8 – ASUU 

by Sadiq
4 years ago
ASUU

Shugaban kungiyar malaman jami’o’i (ASUU), Farfesa Emmanuel Osodeke, ya ce nan ba da dadewa ba kungiyar za ta janye yajin aikin da ta kwashe watanni takwas tana yi. 

Osodeke ya bayyana haka ne a wani taro da suka yi da shugabannin majalisar wakilai a ranar Litinin a Abuja.

  • Ka’idar Sin Daya Tilo A Duniya Ke Tabbatar Da Kwanciyar Hankali A Mashigin Tekun Taiwan
  • Yawan Jama’ar Sin Na Ci Gaba Da Karuwa Kana Yanayin Aikin Yi Bai Sauya Ba

Ya ce daga abin da kungiyar ta gani a wurin taron “akwai alamun nasara. ”

ADVERTISEMENT

“A wannan karon ana fatan ba za a samu wasu mutane ko kungiya da za su haifar da al’amuran da za su sa kungiyar ta shiga cikin wani mawuyacin hali,” in ji shi.

Ya kuma yi fatan cewa shiga tsakani da shugabannin majalisar za su yi shi ne na karshe saboda dalibai, inda ya kara da cewa fafutukar da ASUU ta yi na neman tsarin ilimi da jami’o’i ne a kasar nan.

LABARAI MASU NASABA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

“Muna fatan nan da ‘yan kwanaki masu zuwa za mu kawo karshen wannan yajin aikin.

Osodeke ya ce “Muna son samun tsarin da sake lissafin ya isa ya jawo malamai a duk duniya zuwa jami’o’inmu.”

Ya ce ya kamata kuma a rika biyan jami’o’in Nojeriya da kudi mai tsoka domin jawo hankalin daliban kasashen waje, yayin da ya nuna damuwa kan wasu nagartattun malamai da ke barin kasar.

“Mu ne manyan Afirka kuma dole ne mu rayu tare da wannan.

Ya ci gaba da cewa, “Muna godiya ga shugaban majalisar kan wannan shiga tsakani kuma dole ne mu hada kai domin kowane dan Nijeriya ya yi alfahari da jami’o’in da muke da su.”

Ya ce bai kamata yajin aikin ya wuce makonni biyu ba, “da majalisar dokokin kasar ta sa baki kafin yanzu”.

Kakakin majalisar wakilai Femi Gbajabiamila, ya ce tsoma bakin da shugabannin majalisar suka yi ya yi tasiri.

Gbajabiamila ya kuma ce ganawar da suka yi da shugaban kasa Muhammadu Buhari ta yi nisa.

Ya ce za a sanar da mataki da aka yanke ga kungiyar da jama’a a ranar 11 ga Oktoba.

Ya ce shugabannin majalisar sun samu damar tabbatar da cewa an samar da dukkan bukatun ASUU na farfado da albashi da sauransu a kasafin kudin 2023.

Ya ce an saka Naira biliyan 470 a cikin kasafin kudin 2023 don biyan bukatar ASUU.

“An warware matsalar UTA kamar yadda gwamnati da ASUU suka amince kuma dukkansu za su zauna su amince da sanya duk wasu abubuwan da ASUU ke bukata a tsarin biyan kudin IPPIS.

“Na yi imani mun rufe kasa, kuma shi ne ainihin abin da muka amince da shi.

“Muna ASUU ta janye yajin aikin yau da fatan nan da kwanaki biyu masu zuwa.

“Muna gode wa ASUU saboda amsa kira a duk lokacin da muka kira su.

“Mun hadu a ofishina don tattaunawa. Mun yi haka ne don kare bukatar dalibanmu,” in ji shi.

MASU ALAKA

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi
Manyan Labarai

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Next Post
Kwastam Ta Kama Haramtattun Kayayyaki Na Sama Da Naira Miliyan 200 A Bauchi 

Kwastam Ta Kama Haramtattun Kayayyaki Na Sama Da Naira Miliyan 200 A Bauchi 

LABARAI MASU NASABA

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

Matatar Dangote Ta Ƙara Yawan Man Da Take Tacewa Zuwa Ganga 700,000

June 4, 2026
Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

Ƴansanda Sun Daƙile Harin Ƴan Bindiga, Sun Kwato Shanu 25 A Sakkwato

June 4, 2026
Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

Takunkumin Amurka Ya Haifar Da Mummunan Tasiri Ga Tsarin Samar Da Kayan Latironi Na Duniya

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Kashe Mutane 7, Ya Jikkata 6 A Bauchi

June 4, 2026
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Sanadin Mutuwar Mutane 7 A Bauchi

June 4, 2026
Mun Kaɗu Matuƙa Kan Labarin Mutuwar ‘Yan Mauludi A Hanyar Saminaka – Gwamnan Kaduna

Gwamna Sani Ya Kashe Sama Da Naira Biliyan Ɗaya Kan Tallafin Ɗalibai A Kaduna – Kwamishina

June 4, 2026
Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

Sin Ta Ware Kudi Har Yuan Biliyan 99.9 Domin Tallafawa Kula Da Lafiyar Yara A 2026

June 4, 2026
Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.