ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, November 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mun Samu ‘Yan Takara Masu Tu’ammali Da Miyagun Kwayoyi – Hukumar Zaben Kaduna 

by Shehu Yahaya
1 year ago
Takara

Hukumar zabe mai zaman kanta a Jihar Kaduna (KAD-SECOM) ta bayyana cewa daga cikin ‘yan takarar shugabancin kananan hukumomin da suka tantance akwai masu tuma’ali da miyagun kwayoyi.

Bayanin hakan ya fito ne daga bakin shugabar hukumar, Hajiya Hajara Mohammed, a zantawarta da manema labarai jim kadan bayan kammala tantance ‘yan takarar da suka shiga cikin zaben da za a gudanar ranar 19 ga Wotan Oktobar 2024.

  • Bangaren Sin Ya Yi Kira Ga Bangarori Biyu Dake Rikici A Sudan Da Su Yayyafawa Rikicin Kasar Ruwa
  • Kwalara: Kwara Ta Rufe Gine-gine 14 Saboda Rashin Banɗaki, Ta Gargaɗi Masu Gidaje

Ta ce sun tantance ‘yan takara guda 76 da suka fito daga cikin jam’iyyu 10, tana mai cewa jam’iyyun siyasa 19 hukumar ta yi wa rajista domin shiga zaben, amma guda 10 ne kadai suka tsayar da ‘yan takara.

ADVERTISEMENT

Shugabar ta ce hukumar ta tsayar da ranar 26 ga wannan watan domin fitar da sakamakon sunayen ‘yan takarar da suka tantancewa. Tana mai cewa sun gudanar tantancewar ne bisa sanya ido daga jami’an ‘yansanda da na hukumar shige da fice ta kasa da hukumar sha da fataucin muyagun kwayoyi da hukumar tara kudaden haraja ta Jihar kaduna.

Hajiya Hajara ta kara da cewa da zarar sun kammala nazari kan takardun ‘yan takarar, za su sanar da wadanda suka samu nasarar tsayawa takarar shugabancin kananan hukumomin jihar.

LABARAI MASU NASABA

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

Ta ce hukumar ta kammala duk wasu shirye-shiryen da suka kamata domin gudanar da zaben kananan hukumomin Jihar Kaduna.

Ta kuma bukaci ‘yan siyasa da su gudanar harkokin yakin neman zabensu cikin lumana da bin dokokin kasa domin samun damar gudanar da zaben cikin nasara kamar yadda aka tsare.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya
Tambarin Dimokuradiyya

Abin Da APC Za Ta Yi Da Rinjayen Kashi Biyu Bisa Uku A Majalisar Tarayya

November 7, 2025
Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta
Tambarin Dimokuradiyya

Manyan Kalubalen Da Sabon Shugaban INEC Zai Fuskanta

October 17, 2025
peter
Tambarin Dimokuradiyya

2027: Peter Obi Ya Shiga Rudani Kan Jam’iyyar Da Zai Tsaya Takara

October 17, 2025
Next Post
An Rubuta Ra’ayin “Kwayar Zarra Ta Atom Ta Kawo Alheri Ga Kasashe Masu Tasowa” Na Sin A Cikin Kudurin Hukumar IAEA

An Rubuta Ra’ayin “Kwayar Zarra Ta Atom Ta Kawo Alheri Ga Kasashe Masu Tasowa” Na Sin A Cikin Kudurin Hukumar IAEA

LABARAI MASU NASABA

Majalisar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Bisa Zargin Rashin Ɗa’a

Majalisar Jihar Kogi Ta Dakatar Da Shugaban Ƙaramar Hukuma Kan Laifin Rashin Ɗa’a

November 12, 2025
Xi Ya Gana Da Sarkin Sifaniya A Birnin Beijing

Xi Ya Gana Da Sarkin Sifaniya A Birnin Beijing

November 12, 2025
Bikin Baje Koli CIIE, Bikin Zaburar Da Manoman Afirka

Bikin Baje Koli CIIE, Bikin Zaburar Da Manoman Afirka

November 12, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

An Kama Direban Gwamnati Da Hannu A Satar Motar Ofishin Mataimakin Gwamnan Kano

November 12, 2025
Sin Ta Yi Kira Da A Inganta Mika Mulki Cikin Kwanciyar Hankali A Sudan Ta Kudu

Sin Ta Yi Kira Da A Inganta Mika Mulki Cikin Kwanciyar Hankali A Sudan Ta Kudu

November 12, 2025
Za Mu Kare Sojojin Da Ke Bakin Aiki — Ministan Tsaro

Za Mu Kare Sojojin Da Ke Bakin Aiki — Ministan Tsaro

November 12, 2025
‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3 Tare Da Sace Babur A Nasarawa

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 3 Tare Da Sace Babur A Nasarawa

November 12, 2025
‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi Sama Da 200 A Katsina

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi Sama Da 200 A Katsina

November 12, 2025
Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP

Injiniya Sagir Ibrahim Ƙoƙi Ya Fice Daga Jam’iyyar NNPP

November 12, 2025
Bayanan Da Muka Samu Sun Nuna An Fara Samun Tsaro A Nijeriya – Hafsan Sojin Ƙasa

Bayanan Da Muka Samu Sun Nuna An Fara Samun Tsaro A Nijeriya – Hafsan Sojin Ƙasa

November 12, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.