• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muna Bukatar Gudunmawar Addu’o’in ‘Yan Nijeriya Don Yaki Da Matsalar Tsaro — Badaru

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Muna Bukatar Gudunmawar Addu’o’in ‘Yan Nijeriya Don Yaki Da Matsalar Tsaro — Badaru
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan tsaro, Abubakar Badaru, ya roki ‘yan Nijeriya da su yi wa Allah su yi wa Annabi su ci gaba da taimaka wa gwamnati mai ci da tarin addu’o’i na musamman a bangaren tsaron kasa.

Badaru, wanda ya yi wannan rokon a Abuja yayin da ya karbi bakuncin wakilai daga jiharsa ta Jigawa karkashin jagorancin gwamna, Malam Umar Namadi, ya ce, duba da matsalar tsaro da ke addabar Nijeriya, akwai bukatar addu’o’i domin samun nasara a kan matsalar.

  • Badaru Na Da Kwarewar Jagorantar Ma’aikatar Tsaro – ANA
  • Kungiya Ta Jinjina Wa Tinubu Kan Nada Badaru Ministan Tsaro

A cewarsa, aikin da ke gabansu aiki ne jawur, don haka sun dukufa wajen shawo kan matsalolin kuma akwai bukatar gudunmawa da goyon bayan al’umar Nijeriya ta kowace fuska, ciki har da addu’o’i domin tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a fadin kasar.

Da ya ke magana tun da farko, gwamnan jihar Jigawa, Malam Umar Namadi, da ya jagoranci tawagar sarakuna, shugabannin addinai, ‘Yan kasuwa, ma’aikata da masu ruwa da tsaki daga jihar don kai ziyarar, ya ce, sun kawo ziyarar ne domin taya ministan murna tare da ba shi tabbacin goyon bayansu dari bisa dari a kowane lokaci.

“Ba fa iya zallar mu taya murna ne muka zo ba, a’a mun kuma zo ne domin mu yi maka addu’a. Mun san irin nasarorin da ka cimma a jiharmu, muna maka addu’ar za ka cimma irin wanan nasarar a wannan sabon matsayi da kake kai na ministan tsaro.” Cewar Namadi.

Labarai Masu Nasaba

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Gwamna Namadi ya tunatar da ministan irin tsammani da fatan da ‘Yan Nijeriya ke yi a kansa na cewa zai yi aiki tukuru domin shawo kan matsalolin tsaron da suke kasar nan, “Muddin ka cimma nasara a wannan bangaren, to kuwa ka taba kowani bangare a fadin kasar.”

“Mun yi nasara kuma mun ci sa’ar samun zaman lafiya da kwanciyar hankali a jiharmu ta Jigawa, hakan ba wai kuma yana nufin ba mu bukatar gudunmawarka ba ne, muna neman taimakonku da gudunmawarka domin ci gaban sauran jihohin kasarmu baki daya,” In ji Gwamnan Jigawa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BadaruJigawaMinistan TsaroTsaroUmar NamadiZiyara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wakilai Daga Kasashe Sama Da 90 Za Su Halarci Babban Dandalin Tattaunawa Na Hadin-Gwiwar Kasa Da Kasa Kan Shawarar “Ziri Daya Da Hanya Daya” Karo Na 3

Next Post

Mutum 30 Sun Halaka Tare Da Sace Mutum 19 A Abuja

Related

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

3 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

12 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

14 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

15 hours ago
Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano
Manyan Labarai

Gobara Ta Ƙone Wani Sashe Na Kasuwar Waya A Kano

16 hours ago
Next Post
Mutum 30 Sun Halaka Tare Da Sace Mutum 19 A Abuja

Mutum 30 Sun Halaka Tare Da Sace Mutum 19 A Abuja

LABARAI MASU NASABA

Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

Alkaluman Adana Kaya Na Sin Sun Fadada Cikin Watanni 7 Da Suka Gabata

June 6, 2025
Wutar lantarki

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

June 6, 2025
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.