ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, September 10, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Badaru Na Da Kwarewar Jagorantar Ma’aikatar Tsaro – ANA

by Maryam Rabiu, Abuja
3 years ago
Badaru

Wata kungiyar siyasa da zamantakewa mai suna Arewa New Agenda (ANA), ta bayyana goyon bayanta ga sabon ministan tsaro da aka nada, Mohammed Badaru Abubakar, inda ta ce masu sukar nadin nasa ba su da masaniya kan kwarewar da yake da ita.

Shugaban kungiyar Sanata Ahmad Abubakar MoAllahyidi ne, ya bayyana haka a wani taron manema labarai a Abuja ranar Alhamis.

  • Ana Zargin Gwamnatin Jihar Katsina Da Yin Rufa-Rufa Da Kudaden Ƙananan Hukumomi
  • Rushewar Gini: Wike Ya Umarci A Cafko Mamallakin Ginin Cikin Gaggawa

LEADERDHIP ta ruwaito cewa, ANA ta yi hasashen yadda yankin Arewa zai ci gaba da habaka.

ADVERTISEMENT

Yayin da sabbin ministocin suka shiga zama a ofisoshinsu, ANA ta nuna rashin jin dadinta kan abin da ta kira sukar rashin adalci da ake yi wa wasu Ministocin, wadanda wasu suka fake da rigar Addini da kabilanci wajen sukarsu.

MoAllahyidi ya ce: “Mohammed Abubakar Badaru, sabon ministan tsaro da aka nada, an ware shi ana sukarsa ba komai ba ne face rashin adalci.

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

“Shekaru takwas da Badaru ya yi a matsayin Gwamnan Jihar Jigawa abin koyi ne na tabbatar da tsaro, zaman lafiya, da zaman tare duk da raunin da jihar ke fama da shi.

“Duk da kasancewar jihar Jigawa makwabciyar kasashe da jihohi masu fama da rashin tsaro, jihar na daya daga cikin jahohin Arewa da ba su taba fuskantar matsalar rashin tsaro ba.

“Kungiyar ta ga ya dace ya jagoranci ma’aikatar tsaro, idan aka yi la’akari da tarihinsa na kare martabar yankinsa.

“Nasarar da Badaru ya samu a fagen jama’a da kuma na sirri ya nuna kwarewarsa kan wannan fage.”

ANA ta jaddada wajibcin samun goyon baya da mutunta shugabanci, inda ta yi watsi da duk wani kira na sauya Badaru daga mukamin ministan tsaro

MoAllahyidi ya kara da cewa: “ANA ta kuduri aniyar samar da zaman lafiya yayin da Najeriya ke ci gaba da kokarin inganta kasa.

“Babu shakka, Nijeriya tana cikin wani yanayi. Bukatar ministocin masu tunani da za su iya amfani da albarkatun dan Adam da na kayan aiki don inganta rayuwar ‘yan kasa.”

ANA ta taya ministoci 45 da aka rantsar a baya-bayan nan murna, sannan ta bukace su da su yi kokari wajen samar da bambamci, yana mai cewa nadin nasu ya ba da wata sabuwar dama ta ciyar al’umma gaba.

Sai dai ANA ta yi kira ga ministocin yankin Arewa da su yi aiki tukuru domin ci gaban Arewa da ma Nijeriya baki daya.

Kungiyar ta jaddada bukatar fifita hangen nesa fiye da bukatun kashin kai, inda ta bayyana manyan manufofin da shugaban kasa ya gindaya.

ANA ta jaddada muhimmancin ministocin da su yi hulda da jama’a don fahimtar bukatunsu tare da shigar da su cikin ajandar gwamnatin Shugaba Tinubu.

Badaru
Maryam Rabiu, Abuja
+ postsBio
  • Maryam Rabiu, Abuja
    https://hausa.leadership.ng/author/maryam-rabiu-abuja/
    Tabbas Zai Yiwu A Kawo Ƙarshen Tashin Hankalin Da Ke Tagayyara Yara – Rahoton MDD
  • Maryam Rabiu, Abuja
    https://hausa.leadership.ng/author/maryam-rabiu-abuja/
    MƊD Ta Ƙaddamar Da Shirin “Muryoyi Daga Sahel” Karo Na Biyu
  • Maryam Rabiu, Abuja
    https://hausa.leadership.ng/author/maryam-rabiu-abuja/
    OP-ED: Mahangata A Kan Taron Ƙoli Don Inganta Ci Gaban Duniya – Antonio Guterres
  • Maryam Rabiu, Abuja
    https://hausa.leadership.ng/author/maryam-rabiu-abuja/
    Yadda Ake Shirin Babban Taron Majalisar Dinkin Duniya Kan Iganta Ci Gaba A Amurka

MASU ALAKA

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya
Labarai

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato
Manyan Labarai

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa
Labarai

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Next Post
BRICS Na Taka Rawar Gani Ga Ci Gaban Nahiyar Afirka

BRICS Na Taka Rawar Gani Ga Ci Gaban Nahiyar Afirka

LABARAI MASU NASABA

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

’Yansanda Sun Kama Wadda Ta Yaɗa Labarin OPay Zai Daina Aiki A Nijeriya

September 10, 2026
2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

2027: ’Yansanda Sun Gargaɗi Jam’iyyun Siyasa Kan Haifar Da Rikici A Sakkwato

September 10, 2026
Zabe: Gwamnatin Kano Ta Taƙaita Zirga-zirgar Mutane Da Ababen Hawa

Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu

September 10, 2026
Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

Sin Na Fatan Amurka Za Ta Dakatar Da Furta Karairayi Da Nufin Bata Mata Suna

September 9, 2026
An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

An Kashe Shahararren Mai Sharhin Siyasar Kano, Ibrahim Dan Shagamu

September 9, 2026
Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

Sin Ba Ta Taba Janyewa Wata Kasa Tsani Ba

September 9, 2026
Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

Xi Ya Aike Da Gaisuwa Albarkacin Ranar Malamai Yana Mai Kira Da A Samar Da Matasa Masu Hazaka Domin Kara Farfado Da Kasa

September 9, 2026
Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

Ku Daure Ku Sake Zaɓar Mijina A 2027 – Remi Tinubu

September 9, 2026
Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

Renon Matasa A Kan Kyakkyawar Turba Ginshiki Ne Na Gina KasaBy

September 9, 2026
Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

Bikin CIFTIS Zai Ingiza Bude Kofa A Kasar Sin

September 9, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.