• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muna Bukatar Karin Sojoji Don Magance Matsalolin Tsaro A Jihar Katsina – Hon. Aliyu

by El-Zaharadeen Umar
2 years ago
in Labarai
0
Muna Bukatar Karin Sojoji Don Magance Matsalolin Tsaro A Jihar Katsina – Hon. Aliyu
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Dan Majalisar wakilai ta tarayya mai wakiltar Kananan hukumomin Musawa da Matazu Hon. Abdullahi Aliyu (Talban Musawa) ya yi kira ga shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu da ya turo karin sojoji jihar Katsina domin magance matsalolin tsaro da jihar ke fuskanta.

Abdullahi Aliyu ya yi wannan kiran ne a lokacin da yake maida martani akan wata zanga-zanga da mutanen da yake wakilta suka yi dangane da sace wasu manoma wanda ya ce karin sojoji zai taimaka matuka gaya.

  • SEMA Ta Raba Kayayyakin Gini Na Miliyan N50 Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Jihar Katsina

Haka kuma ya cigaba da cewa shugaban kasa da duk wani mai ruwa da tsaki akan sha’anin tsaro suna da rawar da zai taka wajan magance wannan matsala da manoma ke fuskanta a wannan lokaci mai tsada

A cewar sa matakan da ake dauka akan sha’anin tsaro a yanzu ba za su wadatar ba, saboda haka yana ganin akwai bukatar a tallafi masu karamin karfi domin farfadowa da tattalin arzikin su na yau da kullum

Haka kuma ya nuna damuwarsa akan yadda mutanen kananan hukumomin Musawa da Matazu sun gagara yin barci da idanu biyu saboda wannan matsala, balantana kuma su je gonakin su da harkokin kasuwancin su na yau da kullum..

Labarai Masu Nasaba

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Ya kara da cewa matsalar tsaro ta zama wata babar barazana ga manoman kananan hukumomin Musawa da Matazu wanda ya ce kwana nan ya bada gudunmawar taki tirela biyu ga manoman amma matsalar tsaro ta hana su zuwa gonakin su

Kazalika Hon. Abdullahi Aliyu ya yi Allah wadai da sake bullar kashe-kashe da lalata duniyoyin jama’ar jihar Katsina musamman mutanen kananan hukumomin Musawa da kuma Matazu wanda ya ce hakan ba zai ba su damar cigaba da harkokin kasuwanci ba saboda ayyukan ‘yan ta’adda

A daidai wannan gaba na ke kara kira ga shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu da cewa an zo gabar da ake da bukatar karin yawan jami’an tsaron da ke jihar Katsina domin su kawo karshen salwantar da rayukan al’umma da duniyoyin su.

“Ina san shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu da ya duba wani kyakkyawan tsari akan sha’anin tsaro da zai dawo da martabar tsaron Nijeriya musamman a wannan lokaci da abubuwa suka koma baya wanda ake bukatar kawo dangantaka mai kyau tsakanin jami’an tsaro da kuma al’umma.” Inji shi

Haka kuma dan majalisar ya bayyana cewa shugaban kasa na da ikon lalubo hanyoyin daukaka darajar hukumomin tsaro ta hanyar maida hankali akan sha’anin tattalin arziki da bayar da tsari da zai kawo karshen ‘yan ta’adda da gungun barayi .

Hon. Abdullahi Aliyu ya kara da cewa yanzu haka suna yin aiki tare da dan Majalisar dattawa na shiryar Funtua da shugaban ‘yan sandan Nijeriya domin ganin an tura jami’an tsaro 600 a shiryar Funtua baki daya.

Talban na Musawa ya yi alkawarin yin duk mai yiwuwa wajan ganin an samu hanyar kawo karshen ta’adanci da ‘yan ta’adda da suka adabin kananan hukumomi Musawa da Matazu ganin cewa yanki da ake yin noma.

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: KatsinaMatsalar TsaroNejaZamfara
ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Al’adu Nagari Ke Rainon Sinawa 

Next Post

Zulum Ya Amince Da Ba Dalibai Tallafin Karatu Na N308m

Related

Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC
Labarai

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

5 hours ago
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa
Labarai

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

6 hours ago
Sojoji
Labarai

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

7 hours ago
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya
Labarai

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

8 hours ago
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano
Manyan Labarai

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

10 hours ago
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci
Ra'ayi Riga

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

11 hours ago
Next Post
Zulum Ya Amince Da Ba Dalibai Tallafin Karatu Na N308m

Zulum Ya Amince Da Ba Dalibai Tallafin Karatu Na N308m

LABARAI MASU NASABA

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.