• English
  • Business News
Sunday, September 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muna Fata Masu Talla A Kafafen Sada Zumunta Su Fadakar Kan Shirye-shiryen Tinubu Na Habaka Tattalin Arziki 

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Yajin aiki
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan Yaɗa Labarai Da Wayar Da Kai, Alhaji Mohammed Idris, ya yi kira ga ƙungiyar masu saka tallace-tallace a kafafen yaɗa labarai da sada zumunta su mayar da hankali wajen faɗakar da ‘yan Nijeriya kan sababbin tsare-tsaren tattalin arziki waɗanda gwamnatin Tinubu ta zo da su, waɗanda burinsu shi ne haifar da cigaban ƙasa ta fuskar tattalin arziki.

Idris ya yi kiran ne a ranar Alhamis a Abuja a lokacin buɗe babban Taron Masu Tallace-tallace na Ƙasa mai taken “Sadarwar Talla a Matsayin Mai Kawo Nagartaccen Sauyi Ga Ƙasa”.

  • Yadda Kasar Sin Ke Ba Da Gudummawar Tinkarar Sauyin Yanayi A Duniya
  • Sojojin Somaliya Sun Kashe Mayakan Al-Shabab 60 A Yankin Tsakiyar Kasar

A cewar hadimin musamman na ministan kan yaɗa labarai, Malam Rabi’u Ibrahim a wata sanarwa da ya fitar, inda yace, ministan ya samu wakilcin Darakta-Janar na Hukumar Wayar Da Kai ta Ƙasa (NOA), Mista Lanre Issa-Onilu, ya yi la’akari da muhimmiyar rawar da ƙwararrun masu sana’ar tallace-tallace a kafafen yaɗa labarai ke takawa wajen yaɗa labaran da za su yi tasiri a wajen jama’a.

Ya ce su na kan cikakken matsayin da za su iya jan akalar samun sauyi a tsarin tattalin arziki da zamantakewar Nijeriya ta hanyar yi wa jama’a yekuwar yadda za su ci moriyar sababbin tsare-tsaren da gwamnatin ke aiwatarwa.

Ministan ya ce Gwamnatin Tarayya ta ƙaddamar da shirin tallafa wa ƙananan sana’o’i, da Shirin Shugaban Ƙasa na Bada Rance Bisa Ƙa’idoji da shirye-shiryen rage raɗaɗin rayuwa, waɗanda aka yi domin ‘yan kasuwa, masu aikatau, masu sufuri, ‘yan talla, da masu ayyukan fasaha da bada ƙananan rance.

Labarai Masu Nasaba

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

“Sana’o’i mafi ƙanƙanta a ƙasar nan su miliyan 1 za su ci moriyar rancen kuɗi N50,000 kowannen su, yayin da manyan sana’o’i za su ci moriyar rance daga Asusun Naira Biliyan 75 da aka tanadar.”

Ministan ya ƙara da cewa waɗannan shirye-shiryen ɗori ne a kan waɗanda da ma can an bayyana su kuma ana aiwatar da su, misali samar da motocin safa-safa masu aiki da hasken rana da gwamnatocin jihohi za su ƙaddamar, domin rage wahalar da cire tallafin man fetur ya janyo.

Ya ce duk waɗannan tsare-tsaren ba wai an yi su da ka ba ne, a’a, sai da aka tsara su a tsanake cikin Ajandar Sabuwar Fata ta Shugaban Ƙasa, wadda ta haɗa da sauya fasalin tattalin arziki don a samar da cigaba mai ɗorewa; ƙarfafa tsarin tsaro don samar da kwanciyar hankali da arziki; haɓaka aikin gona don wadata ƙasa da abinci; buɗe hanyoyin makamashi da ma’adinai don samun cigaba mai ɗorewa da kuma bunƙasa hanyoyi da gine-gine a matsayin su na turakun kawo cigaba.

Sauran su ne: bada muhimmanci ga harkokin ilimi, kiwon lafiya, da taimakon jama’a a matsayin muhimman ginshiƙan cigaban ƙasa da gaggauta faɗaɗar hanyoyin tattalin arziki ta hanyar masana’antu, aiki da komfuta, fasahohin zamani, ƙere-ƙere, da ƙirƙire-ƙirƙire.

Ministan ya ce wannan gwamnatin ta sadaukar da kan ta ne ga samar da bayanai a kan lokaci kuma ta nagartacciyar hanya, kuma ya bada tabbacin cewa zai gudanar da aikin da aka ɗora masa a buɗe kuma a mutunce.

Ya ce: “A yayin da mu ke bada bayani ba tare da ɓoye komai ba kuma a cikin nagarta, ina kira a gare ku a matsayin ku na ƙwararru da ku tattaro ƙwan ku da kwarkwatar ku ku taimaka mana domin mu isar da bayani dalla-dalla ga jama’a ba tare da wata hargowa ko sauya shi ba.”


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AmurkaMinista
ShareTweetSendShare
Previous Post

Nijeriya Ta Koma Ta 44 A Fagen Kwallon Kafa A Duniya

Next Post

Sana’ar Kitso Ta Yi Min Komai – Safiya Yakubu

Related

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri
Labarai

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

3 hours ago
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro
Manyan Labarai

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

4 hours ago
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas
Labarai

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

5 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Dawowa Hutu Ya Tayar Da Hankalin Iyaye Saboda Ƙarin Kuɗin Makaranta

6 hours ago
Likitoci
Manyan Labarai

NARD Ta Janye Yajin Aikin Gargaɗi Da Ta Fara

7 hours ago
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Manyan Labarai

Rushewar Masa’antu Ya Jefa Al’umma Da Dama Cikin Ƙangin Talauci A Arewacin Nijeriya

11 hours ago
Next Post
Sana’ar Kitso Ta Yi Min Komai – Safiya Yakubu

Sana'ar Kitso Ta Yi Min Komai - Safiya Yakubu

LABARAI MASU NASABA

Me Ya Sa Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Ta Samu Goyon Baya Daga Sassan Kasa Da Kasa

Me Ya Sa Shawarar Tsarin Shugabancin Duniya Ta Samu Goyon Baya Daga Sassan Kasa Da Kasa

September 14, 2025
Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

Sama Da Fam Biliyan Uku Aka Kashe A Firimiyar Ingila Wajen Sayen Ƴan Wasa

September 14, 2025
Me Ya Sa Bayern Liverkusen Ta Kori Erik Ten Hag Bayan Wasanni Biyu?

Me Ya Sa Bayern Liverkusen Ta Kori Erik Ten Hag Bayan Wasanni Biyu?

September 14, 2025
An Karrama Fitattun Fina-Finai A Bikin “Golden Panda” Da Ya Gudana A Lardin Sichuan Na Kasar Sin

An Karrama Fitattun Fina-Finai A Bikin “Golden Panda” Da Ya Gudana A Lardin Sichuan Na Kasar Sin

September 14, 2025
Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

Matashi Ya Rasa Ransa A Yunƙurin Satar Kyabul Ɗin Taransifoma A Maiduguri

September 14, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Wani Sojan Gona Ɗauke Da Bindiga A Katsina

September 14, 2025
Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina

NPA Ta Fara Aiki Da Sabon Tsarin ETO A Tashar Apapa

September 14, 2025
Sojojin Nijeriya Sun Kashe ‘Yan Ta’adda 139, Sun Cafke 132 A Cikin Sati 2 —Hedikwatar Tsaro

Sojoji Sun Ceto Mutane 30 Da Aka Yi Garkuwa Da Su, Sun Kashe ‘Yan Ta’adda Da Dama

September 14, 2025
Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

Ɗalibai 750 Sun Amfana Da Bashin Karatu Na Naira Milyan 32.14 A Jihar Gombe

September 14, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: ‘Yansanda Sun Tarwatsa Masu Zanga-zangar Adawa Da Dokar Ta-ɓaci A Ribas

‘Yansanda Sun Ceto Yara 5 Da Aka Sace A Adamawa

September 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.