• English
  • Business News
Wednesday, May 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muna Zargin Masallatai Da Coci-coci Da Hannu A Satar Mai –Kyari

by Sulaiman
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Muna Zargin Masallatai Da Coci-coci Da Hannu A Satar Mai –Kyari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kamfanin mai na kasa (NNPCL) Mele Kyari, ya bayyana cewa coci-coci da masallatai da jami’an tsaro da kuma al’ummomin da bututun mai ya bi ta yankinsu, duk suna da hannu wajen fasa bututun mai domin sacewa.

Ya ce: “Kamar yadda ku ma kun sani, akwai munanan ayyukan masu fasa manyan bututun mu tun daga Atlas Cobe har zuwa Ibadan, sannan da kuma duk wasu dakunan ajiya (Depot) guda 37 da muke da su a fadin kasar nan.

  • Jami’an KAROTA Sun Cafke Tirela Makare Da Giya A Kano
  • Sin Ta Yi Watsi Da Rahoton MDD Game Da Batun Kare Hakkin Bil Adama A Xinjiang

Dukkansu babu wanda za a iya tura mai ta cikinsa ayau. “Kuma kowa ya san me ya sa ba ma turawa, yau shekara 15 kenan, Bututunmu na Warri zuwa Benin ba mu yi amfani da shi ba.

Kowanne digon Mai daya muka tura sai ya bace. Kuma ba shakka, za ku tuna abin bakin ciki da lamarin gobara ya afku a kusa da Warri, kusa da Sapele wanda ya kashe mutane da dama.

“Akwanakin baya, a wani yanki a Legas, Lokacin da gobara ta tashi a daya daga cikin bututunmu, mun gano cewa ana satar man daga cikin gidaje da Masallatai da Coci-coci.

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Kano Ta Hana Tallace-tallacen Magungunan Gargajiya A Fina-finai Da Kan Tituna

Yanzu-yanzu: Tukunyar Gas Ta Fashe A Harabar Filin Wasannin Na Kasa Da Ke Gudana A Ogun

“Hakan yana nufin kowa yana sane da satar man. Babu yadda za a yi a kwashi mai cikin Tanka a cikin unguwannin Jama’a amma ace ba a gani ba.”

Sai dai kuma, da suke mayar da martani kan zargin na shugaban NNPC, wasu malaman addinin Kirista sun kalubalance shi da ya fallasa wuraren ibadar da ake zargi da satar man.

Tsohon Daraktan Harkokin Shari’a na Kungiyar Kiristoci ta Kasa, Ebangelist Kwakur ya musanta lamarin tare da bayyana cewa, “Ba na tunanin yana da wata kwakkwarar shaida a kan haka.

 Idan kuma yana da ita ya fallasa kowa ya gani. Akwai yiwuwar za a iya samun wani gari da ake da masallaci da coci kuma a samu barayi a cikinsa.

Kuma mu a matsayinmu na shugabannin addini ba za mu iya daukar nauyin laifukan da daidakun jama’a ke yi ba.”

Haka shi ma a martaninsa, Babban Limamin Masallacin Al-Habibiyya da ke Abuja, Imam Fuad Adeyemi ya bukaci gwamnati ta hukunta duk wani malamin da aka samu yana da hannu a kan badakalar ta satar mai.

Ya ce ya amince da batun na Kyari cewa akwai wasu coci-coci da masallatai da suke taimakon cin hanci da rashawa saboda limamansu suna kasuwanci ne da addini.

Hakazalika, Mele Kyari ya bayyana cewa Nijeriya za ta dakatar da sayo man fetur daga kasashen waje daga tsakiyar badi idan Allah ya kai mu.

Kyari ya bayyana haka ne a ranar Talata, yayin gudanar da taron manema labarai na ma’aikatu da ake yi mako-mako wanda kwamitin yada labarai na fadar shugaban kasa ke shiryawa a fadar shugaban kasa. Ya nunar da cewa man da za a rika tacewa daga matatar mai ta Dangote da sauran matatun main a gwamnati da kananan da ake da sun a ‘yan kasuwa zai kawo kawo karshen sayo man daga waje har ma kasar ta fara fitarwa ita ma.

Ya ce sabo karuwar yawan ‘Yan Nijeriya masu matsakaitan karfi, adadin man da ake da amfani da shi ya karu ainun amma duk da haka za a samu wadatar man da ake sarrafawa a cikin gida har ma a rika fitarwa zuwa waje.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CociKyariMaiMan feturMasallatai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Keta Ka’idojin Fitar Da Kayayyaki

Next Post

Pogba Ya Ce Barayi Suna Yi Masa Barazana

Related

Gwamnatin Kano Ta Hana Tallace-tallacen Magungunan Gargajiya A Fina-finai Da Kan Tituna
Manyan Labarai

Gwamnatin Kano Ta Hana Tallace-tallacen Magungunan Gargajiya A Fina-finai Da Kan Tituna

4 hours ago
Yanzu-yanzu: Tukunyar Gas Ta Fashe A Harabar Filin Wasannin Na Kasa Da Ke Gudana A Ogun
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: Tukunyar Gas Ta Fashe A Harabar Filin Wasannin Na Kasa Da Ke Gudana A Ogun

7 hours ago
Ana Zargin ‘Yansanda Da Keta Haddin Dan Jarida A Kano
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Fashi, Sun Kama Wasu 7 A Abuja

13 hours ago
An Kama Mata Da Mahaifiyar Ƙasurgumin Ɗan Bindiga Ado Aliero A Saudiyya
Da ɗumi-ɗuminsa

An Kama Mata Da Mahaifiyar Ƙasurgumin Ɗan Bindiga Ado Aliero A Saudiyya

13 hours ago
Gwamnatin Rikon Kwarya: Shirin DSS Ne Na Damke Atiku Da Peter Obi Kafin Rantsar Da Tinubu
Manyan Labarai

DSS Ta Cafke Ɗan Bindiga Yayin Da Yake Shirin Tafiya Aikin Hajji A Sakkwato 

14 hours ago
Hajjin Bana: NAHCON Ta Samar Da Biza 73,310, Tare Da Kai Alhazai 46,000 Kasar Saudiyya
Manyan Labarai

Hajji: Kawo Yanzu An Kammala Jigilar Maniyyatan Jihohi 12 A Nijeriya – NAHCON

18 hours ago
Next Post
Pogba Ya Ce Barayi Suna Yi Masa Barazana

Pogba Ya Ce Barayi Suna Yi Masa Barazana

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Kano Ta Hana Tallace-tallacen Magungunan Gargajiya A Fina-finai Da Kan Tituna

Gwamnatin Kano Ta Hana Tallace-tallacen Magungunan Gargajiya A Fina-finai Da Kan Tituna

May 20, 2025
Xi Ya Jaddada Kwarin Gwiwa Kan Ci Gaba Mai Inganci A Kasar Yayin Ziyararsa A Henan 

Xi Ya Jaddada Kwarin Gwiwa Kan Ci Gaba Mai Inganci A Kasar Yayin Ziyararsa A Henan 

May 20, 2025
EFCC Ta Miƙa Gidaje 750 Na Emefiele Da Ta Ƙwace Ga Ministan Gidaje

EFCC Ta Miƙa Gidaje 750 Na Emefiele Da Ta Ƙwace Ga Ministan Gidaje

May 20, 2025
Yanzu-yanzu: Tukunyar Gas Ta Fashe A Harabar Filin Wasannin Na Kasa Da Ke Gudana A Ogun

Yanzu-yanzu: Tukunyar Gas Ta Fashe A Harabar Filin Wasannin Na Kasa Da Ke Gudana A Ogun

May 20, 2025
Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Dandalin SCO Na 2025

Xi Ya Aike Da Wasikar Taya Murna Ga Dandalin SCO Na 2025

May 20, 2025
Gwamna Bala Ya Yi Alhinin Rasuwar Yariman Bauchi, Garba Muhammad Sambo

Gwamna Bala Ya Yi Alhinin Rasuwar Yariman Bauchi, Garba Muhammad Sambo

May 20, 2025
Raya Kasa Na Bukatar Bin Daidaitacciyar Hanya

Raya Kasa Na Bukatar Bin Daidaitacciyar Hanya

May 20, 2025
Jami’in Tsaro Ya Mayar da Dala 505 Da Riyal 30 Da Ya Tsinta A Yola

Jami’in Tsaro Ya Mayar da Dala 505 Da Riyal 30 Da Ya Tsinta A Yola

May 20, 2025
Ana Zargin ‘Yansanda Da Keta Haddin Dan Jarida A Kano

‘Yansanda Sun Kashe Riƙaƙƙen Ɗan Fashi, Sun Kama Wasu 7 A Abuja

May 20, 2025
An Kama Mata Da Mahaifiyar Ƙasurgumin Ɗan Bindiga Ado Aliero A Saudiyya

An Kama Mata Da Mahaifiyar Ƙasurgumin Ɗan Bindiga Ado Aliero A Saudiyya

May 20, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.