• English
  • Business News
Saturday, August 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muna Zargin Masallatai Da Coci-coci Da Hannu A Satar Mai –Kyari

by Sulaiman
3 years ago
in Manyan Labarai
0
Muna Zargin Masallatai Da Coci-coci Da Hannu A Satar Mai –Kyari
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban kamfanin mai na kasa (NNPCL) Mele Kyari, ya bayyana cewa coci-coci da masallatai da jami’an tsaro da kuma al’ummomin da bututun mai ya bi ta yankinsu, duk suna da hannu wajen fasa bututun mai domin sacewa.

Ya ce: “Kamar yadda ku ma kun sani, akwai munanan ayyukan masu fasa manyan bututun mu tun daga Atlas Cobe har zuwa Ibadan, sannan da kuma duk wasu dakunan ajiya (Depot) guda 37 da muke da su a fadin kasar nan.

  • Jami’an KAROTA Sun Cafke Tirela Makare Da Giya A Kano
  • Sin Ta Yi Watsi Da Rahoton MDD Game Da Batun Kare Hakkin Bil Adama A Xinjiang

Dukkansu babu wanda za a iya tura mai ta cikinsa ayau. “Kuma kowa ya san me ya sa ba ma turawa, yau shekara 15 kenan, Bututunmu na Warri zuwa Benin ba mu yi amfani da shi ba.

Kowanne digon Mai daya muka tura sai ya bace. Kuma ba shakka, za ku tuna abin bakin ciki da lamarin gobara ya afku a kusa da Warri, kusa da Sapele wanda ya kashe mutane da dama.

“Akwanakin baya, a wani yanki a Legas, Lokacin da gobara ta tashi a daya daga cikin bututunmu, mun gano cewa ana satar man daga cikin gidaje da Masallatai da Coci-coci.

Labarai Masu Nasaba

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

‘Yansanda Sun Kama Mutane 302, Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace A Katsina

“Hakan yana nufin kowa yana sane da satar man. Babu yadda za a yi a kwashi mai cikin Tanka a cikin unguwannin Jama’a amma ace ba a gani ba.”

Sai dai kuma, da suke mayar da martani kan zargin na shugaban NNPC, wasu malaman addinin Kirista sun kalubalance shi da ya fallasa wuraren ibadar da ake zargi da satar man.

Tsohon Daraktan Harkokin Shari’a na Kungiyar Kiristoci ta Kasa, Ebangelist Kwakur ya musanta lamarin tare da bayyana cewa, “Ba na tunanin yana da wata kwakkwarar shaida a kan haka.

 Idan kuma yana da ita ya fallasa kowa ya gani. Akwai yiwuwar za a iya samun wani gari da ake da masallaci da coci kuma a samu barayi a cikinsa.

Kuma mu a matsayinmu na shugabannin addini ba za mu iya daukar nauyin laifukan da daidakun jama’a ke yi ba.”

Haka shi ma a martaninsa, Babban Limamin Masallacin Al-Habibiyya da ke Abuja, Imam Fuad Adeyemi ya bukaci gwamnati ta hukunta duk wani malamin da aka samu yana da hannu a kan badakalar ta satar mai.

Ya ce ya amince da batun na Kyari cewa akwai wasu coci-coci da masallatai da suke taimakon cin hanci da rashawa saboda limamansu suna kasuwanci ne da addini.

Hakazalika, Mele Kyari ya bayyana cewa Nijeriya za ta dakatar da sayo man fetur daga kasashen waje daga tsakiyar badi idan Allah ya kai mu.

Kyari ya bayyana haka ne a ranar Talata, yayin gudanar da taron manema labarai na ma’aikatu da ake yi mako-mako wanda kwamitin yada labarai na fadar shugaban kasa ke shiryawa a fadar shugaban kasa. Ya nunar da cewa man da za a rika tacewa daga matatar mai ta Dangote da sauran matatun main a gwamnati da kananan da ake da sun a ‘yan kasuwa zai kawo kawo karshen sayo man daga waje har ma kasar ta fara fitarwa ita ma.

Ya ce sabo karuwar yawan ‘Yan Nijeriya masu matsakaitan karfi, adadin man da ake da amfani da shi ya karu ainun amma duk da haka za a samu wadatar man da ake sarrafawa a cikin gida har ma a rika fitarwa zuwa waje.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: CociKyariMaiMan feturMasallatai
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Na Adawa Da Matakin Amurka Na Keta Ka’idojin Fitar Da Kayayyaki

Next Post

Pogba Ya Ce Barayi Suna Yi Masa Barazana

Related

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja
Manyan Labarai

An Naɗa Farfesa Adamu Muƙamin Mataimakin Shugaban Jami’ar Yakubu Gowon, Abuja

8 hours ago
‘Yansanda Sun Kama Barayi 15, Sun Kwato Motocin Sata 20 A Kano
Manyan Labarai

‘Yansanda Sun Kama Mutane 302, Sun Ceto Mutum 50 Da Aka Sace A Katsina

1 day ago
Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara
Manyan Labarai

Kauyuka 30 Sun Yi Zanga-zanga Kan Ta’addancin ‘Yan Bindiga A Zamfara

2 days ago
Gwamnan Kano Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Gentle, Ya Bada Umarnin Zakulo Masu Laifin
Manyan Labarai

Gwamnan Kano Ya Yi Ta’aziyyar Rasuwar Gentle, Ya Bada Umarnin Zakulo Masu Laifin

2 days ago
Masu Ƙwacen Waya Sun Kashe Ɗalibin BUK A Kano
Manyan Labarai

Masu Ƙwacen Waya Sun Kashe Ɗalibin BUK A Kano

2 days ago
Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi
Manyan Labarai

Jami’an Tsaro Sun Daƙile Harin ‘Yan Bindiga A Zamfara, Sun Ƙwato Bindigogi

3 days ago
Next Post
Pogba Ya Ce Barayi Suna Yi Masa Barazana

Pogba Ya Ce Barayi Suna Yi Masa Barazana

LABARAI MASU NASABA

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

Abubuwan Da Suka Ja Hankalin Gwamnatin Tarayya Ta Ƙaddamar Da Tsarin Noman Waken Soya

August 9, 2025
Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

Philippines Za Ta Girbi Sakamakon Rura Wutar Rikici Kan Taiwan

August 9, 2025
Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

Cacar Baki Ta Ɓarke Tsakanin el-Rufai Da APC Kan Tazarcen Tinubu A 2027

August 9, 2025
Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

Jakadan Kasar Sin A Najeriya Ya Gana Da Ministar Kula Da Masana’antu Da Cinikayya Da Zuba Jari Ta Kasar

August 9, 2025
Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

Sanatocin Da Ba Su Kawo Ƙudiri Ba Tun Bayan Ƙaddamar Da Majalisar Dattawa Ta 10

August 9, 2025
Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

Andrei Okounkov: Sinawa Na Daukar Koyon Abubuwa Da Muhimmanci 

August 9, 2025
Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

Mutum 2,838 Suka Mutu A Haɗarin Mota Cikin Wata Shida A Nijeriya – Rahoto

August 9, 2025
Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

Kayayyakin Sin Sun Samu Karbuwa Yayin Bikin Nune-nunen Kayayyakin Abinci Na Afrika

August 9, 2025
An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

An Ɗaura Auren Rahma Sadau A Kaduna

August 9, 2025
Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

Kasar Duniyar Wata Da Kasar Sin Ta Samo Ta Samar Da Sakamakon Nazari Fiye Da 150

August 9, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.