ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Muna Zargin Masallatai Da Coci-coci Da Hannu A Satar Mai –Kyari

by Sulaiman
4 years ago
Kyari

Shugaban kamfanin mai na kasa (NNPCL) Mele Kyari, ya bayyana cewa coci-coci da masallatai da jami’an tsaro da kuma al’ummomin da bututun mai ya bi ta yankinsu, duk suna da hannu wajen fasa bututun mai domin sacewa.

Ya ce: “Kamar yadda ku ma kun sani, akwai munanan ayyukan masu fasa manyan bututun mu tun daga Atlas Cobe har zuwa Ibadan, sannan da kuma duk wasu dakunan ajiya (Depot) guda 37 da muke da su a fadin kasar nan.

  • Jami’an KAROTA Sun Cafke Tirela Makare Da Giya A Kano
  • Sin Ta Yi Watsi Da Rahoton MDD Game Da Batun Kare Hakkin Bil Adama A Xinjiang

Dukkansu babu wanda za a iya tura mai ta cikinsa ayau. “Kuma kowa ya san me ya sa ba ma turawa, yau shekara 15 kenan, Bututunmu na Warri zuwa Benin ba mu yi amfani da shi ba.

ADVERTISEMENT

Kowanne digon Mai daya muka tura sai ya bace. Kuma ba shakka, za ku tuna abin bakin ciki da lamarin gobara ya afku a kusa da Warri, kusa da Sapele wanda ya kashe mutane da dama.

“Akwanakin baya, a wani yanki a Legas, Lokacin da gobara ta tashi a daya daga cikin bututunmu, mun gano cewa ana satar man daga cikin gidaje da Masallatai da Coci-coci.

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

“Hakan yana nufin kowa yana sane da satar man. Babu yadda za a yi a kwashi mai cikin Tanka a cikin unguwannin Jama’a amma ace ba a gani ba.”

Sai dai kuma, da suke mayar da martani kan zargin na shugaban NNPC, wasu malaman addinin Kirista sun kalubalance shi da ya fallasa wuraren ibadar da ake zargi da satar man.

Tsohon Daraktan Harkokin Shari’a na Kungiyar Kiristoci ta Kasa, Ebangelist Kwakur ya musanta lamarin tare da bayyana cewa, “Ba na tunanin yana da wata kwakkwarar shaida a kan haka.

 Idan kuma yana da ita ya fallasa kowa ya gani. Akwai yiwuwar za a iya samun wani gari da ake da masallaci da coci kuma a samu barayi a cikinsa.

Kuma mu a matsayinmu na shugabannin addini ba za mu iya daukar nauyin laifukan da daidakun jama’a ke yi ba.”

Haka shi ma a martaninsa, Babban Limamin Masallacin Al-Habibiyya da ke Abuja, Imam Fuad Adeyemi ya bukaci gwamnati ta hukunta duk wani malamin da aka samu yana da hannu a kan badakalar ta satar mai.

Ya ce ya amince da batun na Kyari cewa akwai wasu coci-coci da masallatai da suke taimakon cin hanci da rashawa saboda limamansu suna kasuwanci ne da addini.

Hakazalika, Mele Kyari ya bayyana cewa Nijeriya za ta dakatar da sayo man fetur daga kasashen waje daga tsakiyar badi idan Allah ya kai mu.

Kyari ya bayyana haka ne a ranar Talata, yayin gudanar da taron manema labarai na ma’aikatu da ake yi mako-mako wanda kwamitin yada labarai na fadar shugaban kasa ke shiryawa a fadar shugaban kasa. Ya nunar da cewa man da za a rika tacewa daga matatar mai ta Dangote da sauran matatun main a gwamnati da kananan da ake da sun a ‘yan kasuwa zai kawo kawo karshen sayo man daga waje har ma kasar ta fara fitarwa ita ma.

Ya ce sabo karuwar yawan ‘Yan Nijeriya masu matsakaitan karfi, adadin man da ake da amfani da shi ya karu ainun amma duk da haka za a samu wadatar man da ake sarrafawa a cikin gida har ma a rika fitarwa zuwa waje.

Kyari
Sulaiman
+ postsBio
  • Sulaiman
    Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
  • Sulaiman
    Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo
  • Sulaiman
    Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli
  • Sulaiman
    Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

MASU ALAKA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya
Manyan Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Shirya Tallafa Wa Mata Da Masu Ƙaramin Ƙarfi Fiye Da Miliyan Ɗaya

June 3, 2026
Next Post
Pogba Ya Ce Barayi Suna Yi Masa Barazana

Pogba Ya Ce Barayi Suna Yi Masa Barazana

LABARAI MASU NASABA

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026
Majalisa Ta Nemi Tinubu Ya Canza Dabarun Yaƙi Da Ta’addanci Don Kawo Ƙarshen Kashe-kashe

’Yan Majalisar Tarayya 3 Sun Fice Daga APC Zuwa ADC da PRP

June 3, 2026
An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

An Fara Watsa Shirye-Shirye Masu Taken “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” Da Sauran Fina-Finan Bayyana Labaran Sin A Kasar Laos

June 3, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

Gwamnatin Beijing Ta Amince Da Kafa Cibiyar Kirkire-Kirkiren Fasahar Lissafi Mai Nasaba Da Sararin Samaniya

June 3, 2026
Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

Za A Fara Buga Gasar Kofin Sarkin Gombe Bayan Masu Ruwa Da Tsaki Sun Cimma Matsaya

June 3, 2026
Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

Hada Kai Da ’Yan Awaren Yankin Taiwan Ba Zai Haifar Da Ɗa Mai Ido Ba

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.