• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Munafurci Dodo Ne Me Shi Ya Kan Ci

by Sulaiman and CGTN Hausa
10 months ago
in Daga Birnin Sin
0
Munafurci Dodo Ne Me Shi Ya Kan Ci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A baya bayan nan, wasu ’yan siyasar Amurka sun sake bullo da zarge zarge marasa asali kan kasar Sin, suna masu bayyana Sin din a matsayin mai tallafawa masana’antun kera makamai na kasar Rasha, har ma suna kira da a kara kakkabawa wasu sassa, da daidaikun jama’ar Sin takunkumai ba gaira ba dalili. A daya bangaren kuma, kungiyar tsaro ta NATO, bisa jagorancin Amurka ita ma ta zargi Sin da ingiza rikicin kasar Ukraine.

 

Ta hanyar shafawa kasar Sin kashin kaji don gane da rikicin na Ukraine, Amurka da NATO suna kokarin saukewa kan su alhakin ci gaba da rura wutar tashin hankalin da ya ki ci ya ki cinyewa, tare da nunawa sassan kasa da kasa su ne masu son wanzar da zaman lafiya da lumana.

  • Sin Ta Kashe Yuan Biliyan 300 A Aikin Gina Tituna A Xizang A Tsakanin Shekarar 1953-2023
  • Wakilin Sin: Dage Takunkumin Hana Shigo Da Makamai Zai Taimakawa Gwamnatocin Afirka Ta Tsakiya Wajen Kara Karfin Tsaro

To sai dai kuma, magana ta gaskiya ita ce Amurka da kungiyar NATO, na so ne su haifar da wani yanayi da zai sa a rika ganin baiken kyakkyawar dangantakar raya tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da Rasha, ta hanyar kitsa karairayi, cewa wai Sin na samarwa Rasha tallafin harkokin soji, duk da cewa ba su nuna wasu hujjoji na zahiri da za su tabbatar da zargi nasu ba.

 

Labarai Masu Nasaba

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Wasu alkaluma ma sun tabbatar da cewa, kaso sama da 60 bisa dari na kayayyakin ayyukan soji, da na ayyukan soji da farar hula da Rasha ke saya, tana sayen su ne daga Amurka da sauran kasashen Turai, yayin da kaso 95 bisa dari na daukacin kayayyakin aikin soji na kasar Rasha da Ukraine ta lalata sun fito ne daga kasashen yammacin duniya, kana kaso 72 bisa dari na sassan makaman da Rasha ke kerawa sun fito ne daga kamfanonin Amurka.

 

A matsayinta na kasa mai hangen nesa da mutunta doka, kasar Sin ba ta taba samar da makamai ga kowane bangare na rikicin Ukraine ba, tana kuma tantance, da takaita kayan ayyuka da ake iya amfani da su a aikin soji da na farar hula.

 

A daya hannun kuma, Sin da Rasha na gudanar da hada-hadar cinikayya da tattalin arziki a bude, tare da biyayya ga dokoki da ka’idojin kungiyar cinikayya ta duniya WTO. Yayin da a nasu bangare Amurka da ’yan koren ta, ke karya wadannan dokoki ta hanyar kakkabawa kamfanonin Sin takunkumi, da kuma nuna rashin sanin ya kamata wajen kitsa karairayi, da munafurci, da nufin shafawa kasar Sin bakin fenti, to amma dai bahaushe kan ce “Munafurci dodo ne mai shi ya kan ci”, kuma “Kowa zai gina ramin mugunta to ya gina shi gajere”, domin mai yiwuwa shi ne zai fada cikin sa!


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jami’o’i 8 Da Nijeriya Ta Amince Da Su A Kasashen Togo Da Benin

Next Post

Tura Ta Kai Bango, Zanga-Zanga Ta Kutsa Kai Har Gidan Buhari Da Sarkin Daura

Related

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile
Daga Birnin Sin

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

8 hours ago
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata
Daga Birnin Sin

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

9 hours ago
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa
Daga Birnin Sin

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

11 hours ago
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya
Daga Birnin Sin

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

12 hours ago
Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daidaita Harajin Fito Kan Hajojin Amurka Da Ake Shigarwa Kasar

19 hours ago
Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Da Uwar Gidan Shugaban Kasar Brazil Sun Ziyarci Babban Zauren Nuna Fasahohin Nishadantarwa Ta Kasar Sin

21 hours ago
Next Post
Miƙa Mulki Daga Buhari Zuwa Tinubu: Abubuwan Da Suka Fi Jan Hankali

Tura Ta Kai Bango, Zanga-Zanga Ta Kutsa Kai Har Gidan Buhari Da Sarkin Daura

LABARAI MASU NASABA

UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

Xi Jinping Ya Gana Da Takwarorinsa Na Kasashen Colombia Da Chile

May 14, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

Gwamnatin Tarayya Da Majalisar Dokoki Za Su Haɗa  Gwiwa Kan Sake Duba Dokar Laifukan Intanet — Minista

May 14, 2025
Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

Yadda Kasar Sin Ke Kokarin Gina Tashar Bincike A Sama Da Tubalin Kasar Duniyar Wata

May 14, 2025
gaza

Kasafin Kudi Na Naira Tiriliyan 1.78 Na Abuja Ya Tsallake Karatu Na Biyu A Majalisa

May 14, 2025
Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

Kasar Sin Za Ta Inganta Cikakken Tsarin Fitar Da Ma’adanai Zuwa Ketare Don Kiyaye Tsaron Kasa

May 14, 2025
Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

Tinubu Ya Yaba Wa Sule Lamiɗo A Taron Ƙaddamar Da Littafin Tarihin Rayuwasa

May 14, 2025
Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

Manyan Ayyuka Guda Biyar Za Su Raya Makomar Al’ummomin Kasar Sin Da kasashen Latin Amurka Da Caribbean Ta Bai Daya

May 14, 2025
Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

Yadda Aka Gina Ofishin ‘Yansanda Na Zamani A Abuja

May 14, 2025
JAMB Ta Amince Da Maki 140 Da 100 Mafi Karancin Maki Na Shiga Manyan Makarantu

JAMB: Tangarɗar Na’ura Ne Ya Haifar Da Gagarumar Koma Baya A Sakamakon UTME Na 2025

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.