• English
  • Business News
Tuesday, September 16, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Munafurci Dodo Ne Me Shi Ya Kan Ci

by Sulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
in Daga Birnin Sin
0
Munafurci Dodo Ne Me Shi Ya Kan Ci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A baya bayan nan, wasu ’yan siyasar Amurka sun sake bullo da zarge zarge marasa asali kan kasar Sin, suna masu bayyana Sin din a matsayin mai tallafawa masana’antun kera makamai na kasar Rasha, har ma suna kira da a kara kakkabawa wasu sassa, da daidaikun jama’ar Sin takunkumai ba gaira ba dalili. A daya bangaren kuma, kungiyar tsaro ta NATO, bisa jagorancin Amurka ita ma ta zargi Sin da ingiza rikicin kasar Ukraine.

 

Ta hanyar shafawa kasar Sin kashin kaji don gane da rikicin na Ukraine, Amurka da NATO suna kokarin saukewa kan su alhakin ci gaba da rura wutar tashin hankalin da ya ki ci ya ki cinyewa, tare da nunawa sassan kasa da kasa su ne masu son wanzar da zaman lafiya da lumana.

  • Sin Ta Kashe Yuan Biliyan 300 A Aikin Gina Tituna A Xizang A Tsakanin Shekarar 1953-2023
  • Wakilin Sin: Dage Takunkumin Hana Shigo Da Makamai Zai Taimakawa Gwamnatocin Afirka Ta Tsakiya Wajen Kara Karfin Tsaro

To sai dai kuma, magana ta gaskiya ita ce Amurka da kungiyar NATO, na so ne su haifar da wani yanayi da zai sa a rika ganin baiken kyakkyawar dangantakar raya tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da Rasha, ta hanyar kitsa karairayi, cewa wai Sin na samarwa Rasha tallafin harkokin soji, duk da cewa ba su nuna wasu hujjoji na zahiri da za su tabbatar da zargi nasu ba.

 

Labarai Masu Nasaba

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Wasu alkaluma ma sun tabbatar da cewa, kaso sama da 60 bisa dari na kayayyakin ayyukan soji, da na ayyukan soji da farar hula da Rasha ke saya, tana sayen su ne daga Amurka da sauran kasashen Turai, yayin da kaso 95 bisa dari na daukacin kayayyakin aikin soji na kasar Rasha da Ukraine ta lalata sun fito ne daga kasashen yammacin duniya, kana kaso 72 bisa dari na sassan makaman da Rasha ke kerawa sun fito ne daga kamfanonin Amurka.

 

A matsayinta na kasa mai hangen nesa da mutunta doka, kasar Sin ba ta taba samar da makamai ga kowane bangare na rikicin Ukraine ba, tana kuma tantance, da takaita kayan ayyuka da ake iya amfani da su a aikin soji da na farar hula.

 

A daya hannun kuma, Sin da Rasha na gudanar da hada-hadar cinikayya da tattalin arziki a bude, tare da biyayya ga dokoki da ka’idojin kungiyar cinikayya ta duniya WTO. Yayin da a nasu bangare Amurka da ’yan koren ta, ke karya wadannan dokoki ta hanyar kakkabawa kamfanonin Sin takunkumi, da kuma nuna rashin sanin ya kamata wajen kitsa karairayi, da munafurci, da nufin shafawa kasar Sin bakin fenti, to amma dai bahaushe kan ce “Munafurci dodo ne mai shi ya kan ci”, kuma “Kowa zai gina ramin mugunta to ya gina shi gajere”, domin mai yiwuwa shi ne zai fada cikin sa!


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Jami’o’i 8 Da Nijeriya Ta Amince Da Su A Kasashen Togo Da Benin

Next Post

Tura Ta Kai Bango, Zanga-Zanga Ta Kutsa Kai Har Gidan Buhari Da Sarkin Daura

Related

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi
Daga Birnin Sin

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

35 minutes ago
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire
Daga Birnin Sin

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

2 hours ago
Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne
Daga Birnin Sin

Hadin Gwiwar Raya Tattalin Arziki Da Cinikayya Da Makamashi Tsakanin Sin Da Rasha Ba Abun Zargi Ba Ne

21 hours ago
Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu
Daga Birnin Sin

Tawagogin Sin Da Na Amurka Sun Sake Tattaunawa Game Da Batutuwan Tattalin Arziki Da Cinikayya A Rana Ta Biyu

22 hours ago
Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”
Daga Birnin Sin

Sabunta Cinikin Ba Da Hidima, Masu Zuba Jari Na Waje Suna Ganin “Damar Da Kowa Ke Bukata A Kowane Lungu Na Sin”

23 hours ago
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Ta Dakatar Da Shuka Kiyayya Da Tashin-Tashina A Tekun Kudancin Sin

24 hours ago
Next Post
Miƙa Mulki Daga Buhari Zuwa Tinubu: Abubuwan Da Suka Fi Jan Hankali

Tura Ta Kai Bango, Zanga-Zanga Ta Kutsa Kai Har Gidan Buhari Da Sarkin Daura

LABARAI MASU NASABA

Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

NSCDC Za Ta Fara Sanyan Ido Kan Muhimman Abubuwan More Rayuwa A Jihar Kano

September 16, 2025
Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

Shawarar Inganta Jagorancin Duniya Ta Haifar Da Damar Wanzar Da Daidaito Da Adalci

September 16, 2025
DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

DSS Ta Maka Sowore, Facebook Da X A Kotu Kan Wallafa Rubutu Game Da Tinubu

September 16, 2025
Dan Sanda Ya Kashe Abokin Aikinsa Da Almakashi Har Lahira A Kebbi

Wata Ta Kashe ’Yar Uwarta Kan Bashin Naira 800 A Ondo

September 16, 2025
Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

Jigilar Mai: Me Ya Haddasa Rikicin Dangote Da Ƙungiyar NUPENG?

September 16, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

‘Yan Bindiga Sun Yi Wa Hakimi Yankan Rago A Zamfara

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.