• English
  • Business News
Tuesday, October 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Munafurci Dodo Ne Me Shi Ya Kan Ci

bySulaiman and CGTN Hausa
1 year ago
Dodo

A baya bayan nan, wasu ’yan siyasar Amurka sun sake bullo da zarge zarge marasa asali kan kasar Sin, suna masu bayyana Sin din a matsayin mai tallafawa masana’antun kera makamai na kasar Rasha, har ma suna kira da a kara kakkabawa wasu sassa, da daidaikun jama’ar Sin takunkumai ba gaira ba dalili. A daya bangaren kuma, kungiyar tsaro ta NATO, bisa jagorancin Amurka ita ma ta zargi Sin da ingiza rikicin kasar Ukraine.

 

Ta hanyar shafawa kasar Sin kashin kaji don gane da rikicin na Ukraine, Amurka da NATO suna kokarin saukewa kan su alhakin ci gaba da rura wutar tashin hankalin da ya ki ci ya ki cinyewa, tare da nunawa sassan kasa da kasa su ne masu son wanzar da zaman lafiya da lumana.

  • Sin Ta Kashe Yuan Biliyan 300 A Aikin Gina Tituna A Xizang A Tsakanin Shekarar 1953-2023
  • Wakilin Sin: Dage Takunkumin Hana Shigo Da Makamai Zai Taimakawa Gwamnatocin Afirka Ta Tsakiya Wajen Kara Karfin Tsaro

To sai dai kuma, magana ta gaskiya ita ce Amurka da kungiyar NATO, na so ne su haifar da wani yanayi da zai sa a rika ganin baiken kyakkyawar dangantakar raya tattalin arziki da cinikayya tsakanin Sin da Rasha, ta hanyar kitsa karairayi, cewa wai Sin na samarwa Rasha tallafin harkokin soji, duk da cewa ba su nuna wasu hujjoji na zahiri da za su tabbatar da zargi nasu ba.

 

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Zai Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Na Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Korea Ta Arewa

Habakar Yin Sayayya A Lokacin Hutu Ta Nuna Kirkira Da Irin Ci Gaban Da Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samu   

Wasu alkaluma ma sun tabbatar da cewa, kaso sama da 60 bisa dari na kayayyakin ayyukan soji, da na ayyukan soji da farar hula da Rasha ke saya, tana sayen su ne daga Amurka da sauran kasashen Turai, yayin da kaso 95 bisa dari na daukacin kayayyakin aikin soji na kasar Rasha da Ukraine ta lalata sun fito ne daga kasashen yammacin duniya, kana kaso 72 bisa dari na sassan makaman da Rasha ke kerawa sun fito ne daga kamfanonin Amurka.

 

A matsayinta na kasa mai hangen nesa da mutunta doka, kasar Sin ba ta taba samar da makamai ga kowane bangare na rikicin Ukraine ba, tana kuma tantance, da takaita kayan ayyuka da ake iya amfani da su a aikin soji da na farar hula.

 

A daya hannun kuma, Sin da Rasha na gudanar da hada-hadar cinikayya da tattalin arziki a bude, tare da biyayya ga dokoki da ka’idojin kungiyar cinikayya ta duniya WTO. Yayin da a nasu bangare Amurka da ’yan koren ta, ke karya wadannan dokoki ta hanyar kakkabawa kamfanonin Sin takunkumi, da kuma nuna rashin sanin ya kamata wajen kitsa karairayi, da munafurci, da nufin shafawa kasar Sin bakin fenti, to amma dai bahaushe kan ce “Munafurci dodo ne mai shi ya kan ci”, kuma “Kowa zai gina ramin mugunta to ya gina shi gajere”, domin mai yiwuwa shi ne zai fada cikin sa!

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Firaministan Sin Zai Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Na Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Korea Ta Arewa
Daga Birnin Sin

Firaministan Sin Zai Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Na Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Korea Ta Arewa

October 7, 2025
Habakar Yin Sayayya A Lokacin Hutu Ta Nuna Kirkira Da Irin Ci Gaban Da Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samu   
Daga Birnin Sin

Habakar Yin Sayayya A Lokacin Hutu Ta Nuna Kirkira Da Irin Ci Gaban Da Tattalin Arzikin Kasar Sin Ke Samu   

October 6, 2025
Karamin Ofishin Jakadancin Sin Da Ke Legas Ya Yi Bikin Bunkasa Al’adu Na Bikin Tsakiyar Kaka
Daga Birnin Sin

Karamin Ofishin Jakadancin Sin Da Ke Legas Ya Yi Bikin Bunkasa Al’adu Na Bikin Tsakiyar Kaka

October 6, 2025
Next Post
Miƙa Mulki Daga Buhari Zuwa Tinubu: Abubuwan Da Suka Fi Jan Hankali

Tura Ta Kai Bango, Zanga-Zanga Ta Kutsa Kai Har Gidan Buhari Da Sarkin Daura

LABARAI MASU NASABA

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

Cikar Wa’adin AGOA Ta Nuna Ra’ayin Amurka Kan Afirka

October 7, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

Da Ɗumi-ɗumi: Yakubu Ya Miƙa Ragamar INEC Ga Agbamuche-Mbu A Matsayin Shugabar Riƙo

October 7, 2025
Firaministan Sin Zai Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Na Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Korea Ta Arewa

Firaministan Sin Zai Halarci Bikin Cika Shekaru 80 Na Kafuwar Jam’iyyar WPK Ta Korea Ta Arewa

October 7, 2025
Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane

Ba Yanzu Zan Koma Gasar Firimiyar Ingila Ba – Harry Kane

October 7, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Wa Sarakuna Ba Zai Rage Musu Iko Ba A Shirinsa Na Ƙirƙirar Sabbin Masarautu

Gwamnan Bauchi Ya Tabbatar Wa Sarakuna Ba Zai Rage Musu Iko Ba A Shirinsa Na Ƙirƙirar Sabbin Masarautu

October 7, 2025
Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto

Isra’ila Ta Kashe Falasɗinawa Sama Da 66,000 A Gaza Cikin Shekaru 2 – Rahoto

October 7, 2025
Tsaro: Gwamnan Kogi Ya Ayyana Yaƙi Da Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ka’ida Ba Da ‘Yan Bindiga

Tsaro: Gwamnan Kogi Ya Ayyana Yaƙi Da Haƙar Ma’adinai Ba Bisa Ka’ida Ba Da ‘Yan Bindiga

October 7, 2025
Majalisar Wakilai Ta Kafa Kwamiti Da Zai Binciki Harkokin Kirifto Da POS A Nijeriya

Majalisar Wakilai Ta Kafa Kwamiti Da Zai Binciki Harkokin Kirifto Da POS A Nijeriya

October 7, 2025
Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa

Ya Kamata Nijeriya Ta Ayyana Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda — Tsohon Hafsan Sojin Ƙasa

October 7, 2025
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista

Tinubu Ya Bayar Da Umarnin Rage Kuɗin Aikin Hajjin 2026

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version