Magoya bayan tsohon gwamnan jihar Kano, Injiniya Rabi’u Musa Kwankwaso na shirin daukar mataki na gaba biyo bayan murabus din da abokin hamayyarsa, Dr. Umar Abdullahi Ganduje ya yi a matsayin shugaban jam’iyyar APC na kasa.
Tun hawansa karagar mulki, shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu, ya sha ganawa da Kwankwaso, inda suka tattauna batun sauya sheka daga jam’iyyar NNPP zuwa APC. Sai dai masana na ganin Kwankwaso ba zai iya shiga APC ba yayin da abokin hamayyarsa kuma tsohon mataimakinsa, Ganduje ne ke shugabantar jam’iyyar.
- Gwamna Yusuf Ya Jagoranci Tawagar Kano Zuwa Jana’izar Marigayi Aminu Dantata A Madina
- An Sauya Sunan Makarantar Wasanni Don Girmama Ƴan Kano Da Suka Yi Hatsari
A yanzu da Ganduje ya bar kujerar shugabancin jam’iyyar APC na kasa, magoya bayan Kwankwaso sun ce a shirye suke na bin wani mataki na gaba.
Magoya bayan Kwankwaso, wadanda aka fi sani da Kwankwasiyya, sun yi ikirarin cewa Ganduje ya bai wa mutanen Kano kunya, shi ya sa ya yi murabus.
Shugaban jam’iyyar NNPP na Kano, Hashimu Dungurawa, wanda ya yi magana a madadin magoya bayan Kwankwaso, ya bayyana murabus din Ganduje a matsayin kwaso abin kunya ga Kano.
Ya bayyana cewa, an sami Ganduje ne da son yin almundahana, musamman a lokacin zaben shugabannin jam’iyyar da aka kammala kwanan nan.
Dungurawa ya yi wannan ikirarin ne a ranar Lahadin da ta gabata yayin da yake amsa tambayoyi daga LEADERSHIP game da matakin da jam’iyyar za ta dauka na gaba bayan faruwar wannan lamari.
Ya ce, kafafen yada labarai sun rika yada cewa, Ganduje ya yi murabus ne saboda zargin karkatar da kudi, inda ya ce murabus din nasa ba na kashin kansa ba ne.
Sai dai ba zai iya cewa ko wannan lamarin zai iya sa jagoran tafiyar Kwankwasiyya, Rabiu Musa Kwankwaso sauya sheka zuwa APC ba.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp