• English
  • Business News
Wednesday, November 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutane 7 Sun Kone Kurmus A Wani Hatsarin Mota A Legas

by Muhammad
3 years ago

Akalla fasinjoji bakwai ne aka tabbatar da mutuwarsu a ranar Lahadin da ta gabata, yayin da wasu biyar suka samu kone-kone daban-daban a lokacin da wata motar bas ta kasuwanci ta tashi da wuta a gefen Iyana Oworo na jihar Legas.

Fasinjojin bakwai sun mutu bayan da motar bas din ta kama wuta, inda suka kashe mata hudu, maza biyu da kuma yaro namiji.

  • Bene Ya Rufta Da Mutum Tara A Jihar Legas
  • Kasuwannin Jihar Legas Sun Bunkasa A Karkashin Jagorancinmu –Shehu Samfam

Wadanda suka shaida lamarin sun ce direban motar bas din mai lamba KJA 699 GY ya tsere da wasu kone-kone, sannan jami’an hukumar ba da agajin gaggawa ta jihar Legas (LASAMBUS) suka ba wani fasinja kulawa a wurin.

An bayyana cewa, an garzaya da wasu manya mata uku da jami’an agajin gaggawa suka ceto zuwa babban asibitin Gbagada yayain hadarin.

An ce motar bas din tana kan hanyar zuwa Iyana Oworonshoki ne, kwatsam ta samu matsalar wutar lantarki, nan take ta kama wuta.

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, babban sakataren hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Legas (LASEMA), Dakta Olufemi Oke-Osanyintolu, ya ce mutane bakwai ne suka mutu a hadarin.

A cewar Oke-Osanyintolu, an mika gawarwakin mamatan ga sashin kula da lafiyar muhalli na jihar (SEHMU) domin samun kulawar da ta dace a lokacin da iyalansu za su iya tantance su.

Ya ce, “Da isa wurin, an gano wata motar bas mai dauke da fasinjoji 14 Mazda mai lamba KJA 699 GY ta kone.

“Bincike da aka yi a wurin ya nuna cewa lamarin ya faru ne saboda rikon sakainar kashi da kuma wuce gona da iri da direban ya yi wanda ya yi sanadiyar tashin gobarar da fasinjoji 12 ta ritsa da su.

“An yi shiri da jami’an hukumar kula da zirga-zirgar ababen hawa ta Jihar Legas (LASTMA) a wurin da lamarin ya faru domin kwato motar da ta kone daga kan hanya.

“LRT tare da LRU Paramedics LASTMA, LASAMBUS, SEHMU, da kuma ‘yan sandan Nijeriya suka kai dauki a wurin. An bude wani bangare na hanyar don wucewar ababen hawa.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma
Labarai

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025
tinubu
Labarai

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025
Next Post
Buhari Ya Ci Alwashin Kawo Karshen Lalacewar Layin Samar Da Wutar Lantarki Na Kasa

Gwamnati Ta Ba Shugabannin Jami'o'i Umarnin Buɗe Makarantunsu Don Ci Gaba Da Karatu

LABARAI MASU NASABA

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

Ma’aikatar Yaɗa Labarai Da BoS Ta Kaduna Sun Ƙulla Yarjejeniyar Samar Da Sahihan Bayanai Ga Al’umma

November 4, 2025
Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

Sin Ta Kaddamar Da Kwas Din Horon Fasahar Gwaje-Gwaje A Cibiyar CDC Ta Afrika

November 4, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

‘Yansanda Sun Ceto Mutane 3 Da Aka Sace A Kwara

November 4, 2025
‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

‘Yan Sama Jannatin Kumbon Shenzhou-20 Za Su Dawo Doron Kasa A Gobe Laraba

November 4, 2025
tinubu

Tinubu Ya Umarci Ma’aikatar Ilimi Ta Kawo Ƙarshen Yajin Aikin ASUU

November 4, 2025
Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

Sin Na Goyon Bayan Najeriya Wajen Jagorantar Al’ummarta Zuwa Hawa Turbar Neman Ci Gaba Daidai Da Yanayin Kasar

November 4, 2025
2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

2027: Ko Kano Ta Zauna Lafiya Ko Ta Hautsine, Sai Mun Sauke Gwamna Abba — Shugaban APC

November 4, 2025
Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

Li Qiang Ya Zanta Da Kakakin Majalisar Wakilan Najeriya

November 4, 2025
Karancin Abinci: Kofar Ofishin Tinubu A Rufe Take, Har Wasu Ministoci Ba Su Iya Ganinsa – Ndume 

Zargin Kisan Kiyashi Ga Kiristoci: Trump Bai San Ƙalubalen Tsaron Da Najeriya Ke Ciki Ba — Ndume

November 4, 2025
Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

Tsohon Jami’in Diflomasiyyar Nijar: Baje Kolin CIIE Muhimmin Dandali Ne Na Bunkasa Hadin Gwiwa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa

November 4, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.