ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Saturday, September 12, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutane 7 Sun Kone Kurmus A Wani Hatsarin Mota A Legas

by Muhammad
4 years ago

Akalla fasinjoji bakwai ne aka tabbatar da mutuwarsu a ranar Lahadin da ta gabata, yayin da wasu biyar suka samu kone-kone daban-daban a lokacin da wata motar bas ta kasuwanci ta tashi da wuta a gefen Iyana Oworo na jihar Legas.

Fasinjojin bakwai sun mutu bayan da motar bas din ta kama wuta, inda suka kashe mata hudu, maza biyu da kuma yaro namiji.

  • Bene Ya Rufta Da Mutum Tara A Jihar Legas
  • Kasuwannin Jihar Legas Sun Bunkasa A Karkashin Jagorancinmu –Shehu Samfam

Wadanda suka shaida lamarin sun ce direban motar bas din mai lamba KJA 699 GY ya tsere da wasu kone-kone, sannan jami’an hukumar ba da agajin gaggawa ta jihar Legas (LASAMBUS) suka ba wani fasinja kulawa a wurin.

ADVERTISEMENT

An bayyana cewa, an garzaya da wasu manya mata uku da jami’an agajin gaggawa suka ceto zuwa babban asibitin Gbagada yayain hadarin.

An ce motar bas din tana kan hanyar zuwa Iyana Oworonshoki ne, kwatsam ta samu matsalar wutar lantarki, nan take ta kama wuta.

LABARAI MASU NASABA

Mutane 24 Sun Mutu Bayan Shan

Tsohon Shugaban PDP Na Ƙasa Bamanga Tukur Ya Rasu Yana Da Shekara 91

Da yake tabbatar da faruwar lamarin, babban sakataren hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Legas (LASEMA), Dakta Olufemi Oke-Osanyintolu, ya ce mutane bakwai ne suka mutu a hadarin.

A cewar Oke-Osanyintolu, an mika gawarwakin mamatan ga sashin kula da lafiyar muhalli na jihar (SEHMU) domin samun kulawar da ta dace a lokacin da iyalansu za su iya tantance su.

Ya ce, “Da isa wurin, an gano wata motar bas mai dauke da fasinjoji 14 Mazda mai lamba KJA 699 GY ta kone.

“Bincike da aka yi a wurin ya nuna cewa lamarin ya faru ne saboda rikon sakainar kashi da kuma wuce gona da iri da direban ya yi wanda ya yi sanadiyar tashin gobarar da fasinjoji 12 ta ritsa da su.

“An yi shiri da jami’an hukumar kula da zirga-zirgar ababen hawa ta Jihar Legas (LASTMA) a wurin da lamarin ya faru domin kwato motar da ta kone daga kan hanya.

“LRT tare da LRU Paramedics LASTMA, LASAMBUS, SEHMU, da kuma ‘yan sandan Nijeriya suka kai dauki a wurin. An bude wani bangare na hanyar don wucewar ababen hawa.”

Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Gwamna Yusuf Ya Umarci Jami’an Tsaro Su Gano Waɗanda Suka Kashe Danshagamu
  • Muhammad
    Yadda Na Tsira Daga Cutar Mashaƙo A Katsina: “Na Fara Da Tsartuwar Jini Tare Da Yawu”
  • Muhammad
    An Naɗa Yusuf Nasidi Nasir A Matsayin Talban Barayan Kano
  • Muhammad
    Wani Kamfani Ya Tallafa Wa Masu Sana’ar Shayi A Kano

MASU ALAKA

Mutane 24 Sun Mutu Bayan Shan
Labarai

Mutane 24 Sun Mutu Bayan Shan

September 12, 2026
Tsohon Shugaban PDP Na Ƙasa Bamanga Tukur Ya Rasu Yana Da Shekara 91
Manyan Labarai

Tsohon Shugaban PDP Na Ƙasa Bamanga Tukur Ya Rasu Yana Da Shekara 91

September 12, 2026
Gwamnatin Katsina
Labarai

Abinda Kasafin Gwamna Raɗɗa Na Shekarar 2027 Ya Ƙunsa

September 12, 2026
Next Post
Buhari Ya Ci Alwashin Kawo Karshen Lalacewar Layin Samar Da Wutar Lantarki Na Kasa

Gwamnati Ta Ba Shugabannin Jami'o'i Umarnin Buɗe Makarantunsu Don Ci Gaba Da Karatu

LABARAI MASU NASABA

Kwamitin Sulhu Na MDD Ya Bayyana Damuwa Game Da Yadda Yanayin Hare-haren Ta’addanci Ke Sauyawa

Kwamitin Sulhu Na MDD Ya Bayyana Damuwa Game Da Yadda Yanayin Hare-haren Ta’addanci Ke Sauyawa

September 12, 2026
Mutane 24 Sun Mutu Bayan Shan

Mutane 24 Sun Mutu Bayan Shan

September 12, 2026
Tsohon Shugaban PDP Na Ƙasa Bamanga Tukur Ya Rasu Yana Da Shekara 91

Tsohon Shugaban PDP Na Ƙasa Bamanga Tukur Ya Rasu Yana Da Shekara 91

September 12, 2026
Gwamnatin Katsina

Abinda Kasafin Gwamna Raɗɗa Na Shekarar 2027 Ya Ƙunsa

September 12, 2026
Ɗalibai Sun Yi Watsi Da Tallafin Data, Sun Nemi Wi-Fi Kyauta A Makarantu Daga Gwamnati

Ɗalibai Sun Yi Watsi Da Tallafin Data, Sun Nemi Wi-Fi Kyauta A Makarantu Daga Gwamnati

September 12, 2026
Yaƙin Amurka Da Iran Ya Janyo Asarar Fitar Da Ganga Biliyan 2.8 Na Mai

Yaƙin Amurka Da Iran Ya Janyo Asarar Fitar Da Ganga Biliyan 2.8 Na Mai

September 12, 2026
Zan Dawo Da Tallafin Mai Ne Don Rage Farashin Fetur Da Na Sufuri – Atiku

Zan Dawo Da Tallafin Mai Ne Don Rage Farashin Fetur Da Na Sufuri – Atiku

September 12, 2026
An Gargaɗi Mazauna Kusa Da Kogin Kaduna Kan Sako Ruwa Daga Shiroro

An Gargaɗi Mazauna Kusa Da Kogin Kaduna Kan Sako Ruwa Daga Shiroro

September 12, 2026
Shekaru 22 Bayan Rushewar Nigeria Airways, Gwamnati Ta Biya Ma’aikata 2,700 Biliyan 18

Shekaru 22 Bayan Rushewar Nigeria Airways, Gwamnati Ta Biya Ma’aikata 2,700 Biliyan 18

September 12, 2026
Kalaman Christopher Musa Game Da El-Rufa’i Na Ci Gaba Da Tayar Da Ƙura

Kalaman Christopher Musa Game Da El-Rufa’i Na Ci Gaba Da Tayar Da Ƙura

September 12, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.