• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutane Da Yawa Sun Jikkata Yayin Da Magoya Bayan PDP Da APC Suka Yi Arangama A Ribas

bySadiq
3 years ago
PDP

Mutane da dama sun samu raunuka a ranar Litinin yayin da magoya bayan jam’iyyar PDP da APC suka arangama a garin Fatakwal na Jihar Ribas.

Daya daga cikin wadanda suka jikkata shi ne dan takarar gwamna na jam’iyyar APC a zaben gwamnan da aka yi a ranar 18 ga watan Maris, Tonye Cole, wanda ya samu rauni a wuyansa.

  • Dubi Ga Sabbin Hanyoyin Kutse A Facebook, WhatsApp Da Asusun Ajiyar Banki
  • Farashin Danyen Mai Ya Tashi A Kasuwar Duniya

Tun da farko dai wasu ‘yan jam’iyyar PDP sun yi zanga-zanga a kofar ofishin hukumar zabe mai zaman kanta (INEC) da ke kan titin Aba a Fatakwal.

Masu zanga-zangar dai sun bukaci duba kayan zaben da dukkanin jam’iyyun siyasa suka yi.

Jam’iyyar APC a karkashin dan takararta na gwamna a ranar Juma’ar da ta gabata ta ce za ta mamaye ofishin INEC a ranar Litinin domin neman a fitar da sahihin sakamakon da aka yi amfani da su wajen zaben gwamna da aka yi a ranar 18 ga watan Maris domin bai wa jam’iyyar damar shigar da karar a kotun sauraren kararrakin zabe.

LABARAI MASU NASABA

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Wakilinmu da ke wurin, ya ruwaito cewa yayin da zanga-zangar ta PDP, Cole tare da shugaban jam’iyyar APC na jihar Emeka Beke da wasu jiga-jigan jam’iyyar sun hallara a ttitin Aba, inda suka nufi ofishin INE

Matasan da suka yi zanga-zangar sun garzaya zuwa wajensa, inda suka yi ta jifansa da duwatsu da ledar ruwa.

Nan take jami’an tsaro da ke tare da Cole suka yi masa garkuwa tare da saka shi cikin mota, amma duk da hakan masu zangar-zangar suka ci gaba da jifansa.

Cikin dakika kadan sojojin runduna ta 6 ta sojojin Nijeriya da jami’an ‘yan sanda da jami’an tsaron farin kaya da na Sibil Difens suka isa inda suka dinga harbi a iska domin tarwatsa masu zanga-zangar.

Wani ganau ya shaida wa wakilinmu cewa, daya daga cikin jami’an tsaron da ke aiki da Cole ne ya harbi daya daga cikin masu zanga-zanagr.

Mutumin ya zubar da jini sosai sakamakon harbin da aka yi masa a kafarsa.

 Daga baya abokansa sun kai shi asibiti.

Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, al’amura bas u daidaita a yankin ba.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu
Siyasa

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya
Manyan Labarai

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Next Post
Cibiyar Kananan Kayayyaki Ta Sin Ta Yi Cinikayyar Sama Da RMB Biliyan 1 Ta Yanar Gizo

Cibiyar Kananan Kayayyaki Ta Sin Ta Yi Cinikayyar Sama Da RMB Biliyan 1 Ta Yanar Gizo

LABARAI MASU NASABA

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

Kofin Duniya U-20: Argentina Ta Lallasa Nijeriya Da Ci 4-0

October 9, 2025
Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

Ni Ne Ɗan Siyasa Mafi Shahara A Kudu Maso Gabas, Ba Peter Obi Ba – Orji Kalu

October 9, 2025
HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

HOTUNA: Yadda Obasanjo Ya Ƙaddamar Da Sabuwar Cibiyar Taron Ƙasa Da Ƙasa A Bauchi

October 9, 2025
Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

Tattalin Arziƙin Nijeriya Ya Ƙaru Da Kashi 3.9 – Bankin Duniya

October 9, 2025
Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version