• English
  • Business News
Sunday, August 24, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutane Da Yawa Sun Jikkata Yayin Da Magoya Bayan PDP Da APC Suka Yi Arangama A Ribas

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Mutane Da Yawa Sun Jikkata Yayin Da Magoya Bayan PDP Da APC Suka Yi Arangama A Ribas
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mutane da dama sun samu raunuka a ranar Litinin yayin da magoya bayan jam’iyyar PDP da APC suka arangama a garin Fatakwal na Jihar Ribas.

Daya daga cikin wadanda suka jikkata shi ne dan takarar gwamna na jam’iyyar APC a zaben gwamnan da aka yi a ranar 18 ga watan Maris, Tonye Cole, wanda ya samu rauni a wuyansa.

  • Dubi Ga Sabbin Hanyoyin Kutse A Facebook, WhatsApp Da Asusun Ajiyar Banki
  • Farashin Danyen Mai Ya Tashi A Kasuwar Duniya

Tun da farko dai wasu ‘yan jam’iyyar PDP sun yi zanga-zanga a kofar ofishin hukumar zabe mai zaman kanta (INEC) da ke kan titin Aba a Fatakwal.

Masu zanga-zangar dai sun bukaci duba kayan zaben da dukkanin jam’iyyun siyasa suka yi.

Jam’iyyar APC a karkashin dan takararta na gwamna a ranar Juma’ar da ta gabata ta ce za ta mamaye ofishin INEC a ranar Litinin domin neman a fitar da sahihin sakamakon da aka yi amfani da su wajen zaben gwamna da aka yi a ranar 18 ga watan Maris domin bai wa jam’iyyar damar shigar da karar a kotun sauraren kararrakin zabe.

Labarai Masu Nasaba

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Wakilinmu da ke wurin, ya ruwaito cewa yayin da zanga-zangar ta PDP, Cole tare da shugaban jam’iyyar APC na jihar Emeka Beke da wasu jiga-jigan jam’iyyar sun hallara a ttitin Aba, inda suka nufi ofishin INE

Matasan da suka yi zanga-zangar sun garzaya zuwa wajensa, inda suka yi ta jifansa da duwatsu da ledar ruwa.

Nan take jami’an tsaro da ke tare da Cole suka yi masa garkuwa tare da saka shi cikin mota, amma duk da hakan masu zangar-zangar suka ci gaba da jifansa.

Cikin dakika kadan sojojin runduna ta 6 ta sojojin Nijeriya da jami’an ‘yan sanda da jami’an tsaron farin kaya da na Sibil Difens suka isa inda suka dinga harbi a iska domin tarwatsa masu zanga-zangar.

Wani ganau ya shaida wa wakilinmu cewa, daya daga cikin jami’an tsaron da ke aiki da Cole ne ya harbi daya daga cikin masu zanga-zanagr.

Mutumin ya zubar da jini sosai sakamakon harbin da aka yi masa a kafarsa.

 Daga baya abokansa sun kai shi asibiti.

Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, al’amura bas u daidaita a yankin ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCArangamaPDPRibas
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Amsa Wasikar Da Wakilan Masu Fasaha Na Larabawa Suka Rubuta Masa

Next Post

Cibiyar Kananan Kayayyaki Ta Sin Ta Yi Cinikayyar Sama Da RMB Biliyan 1 Ta Yanar Gizo

Related

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru
Manyan Labarai

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

8 hours ago
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu
Ilimi

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

14 hours ago
NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano
Manyan Labarai

NDLEA Ta Kama Matashi Da Tabar Wiwi Ta Naira Miliyan 10 A Kano

18 hours ago
Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

2 days ago
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja
Manyan Labarai

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

2 days ago
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?
Manyan Labarai

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

2 days ago
Next Post
Cibiyar Kananan Kayayyaki Ta Sin Ta Yi Cinikayyar Sama Da RMB Biliyan 1 Ta Yanar Gizo

Cibiyar Kananan Kayayyaki Ta Sin Ta Yi Cinikayyar Sama Da RMB Biliyan 1 Ta Yanar Gizo

LABARAI MASU NASABA

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

NAF Ta Kashe ’Yan Ta’adda 35 A Iyakar Nijeriya Da Kamaru

August 23, 2025
Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

Amfani Da Rashin Amfanin Auren Jari

August 23, 2025
CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

CMG Ya Yi Bikin Cudanyar Al’adu Mai Taken “Sautin Zaman Lafiya” A Hadaddiyar Daular Larabawa Da Koriya Ta Kudu

August 23, 2025
Yadda Ake Alale

Yadda Ake Alale

August 23, 2025
Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

Babban Sakataren SCO: Sin Na Taka Rawar Gani A Matsayin Kasar Da Ke Shugabancin SCO

August 23, 2025
Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

Matsalar Al’ada Da Ciwon Mara Ga Mata

August 23, 2025
CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

CMG Ya Kaddamar Da Gangamin Tattara Fina-Finai Da Talabijin Da Aka Samar Bisa AI A Los Angeles

August 23, 2025
Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

Taron Kare Hakkin Dan Adam Na Sin Da Afirka Na Farko Ya Nemi Hada Karfi Don Tabbatar Da ‘Yancin Samun Ci Gaba

August 23, 2025
Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

Bangaren Kasuwancin “E-Commerce” Na Kasar Sin Ya Karu Sosai A Watanni 7 Na Farkon Bana

August 23, 2025
Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

Yajin Aiki: Kungiyar ASUP Ta Ba Gwamntin Tarayya Wa’adin Kwana 21 Ta Biya Masu Bukatu

August 23, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.