ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutane Da Yawa Sun Jikkata Yayin Da Magoya Bayan PDP Da APC Suka Yi Arangama A Ribas

by Sadiq
3 years ago
PDP

Mutane da dama sun samu raunuka a ranar Litinin yayin da magoya bayan jam’iyyar PDP da APC suka arangama a garin Fatakwal na Jihar Ribas.

Daya daga cikin wadanda suka jikkata shi ne dan takarar gwamna na jam’iyyar APC a zaben gwamnan da aka yi a ranar 18 ga watan Maris, Tonye Cole, wanda ya samu rauni a wuyansa.

  • Dubi Ga Sabbin Hanyoyin Kutse A Facebook, WhatsApp Da Asusun Ajiyar Banki
  • Farashin Danyen Mai Ya Tashi A Kasuwar Duniya

Tun da farko dai wasu ‘yan jam’iyyar PDP sun yi zanga-zanga a kofar ofishin hukumar zabe mai zaman kanta (INEC) da ke kan titin Aba a Fatakwal.

ADVERTISEMENT

Masu zanga-zangar dai sun bukaci duba kayan zaben da dukkanin jam’iyyun siyasa suka yi.

Jam’iyyar APC a karkashin dan takararta na gwamna a ranar Juma’ar da ta gabata ta ce za ta mamaye ofishin INEC a ranar Litinin domin neman a fitar da sahihin sakamakon da aka yi amfani da su wajen zaben gwamna da aka yi a ranar 18 ga watan Maris domin bai wa jam’iyyar damar shigar da karar a kotun sauraren kararrakin zabe.

LABARAI MASU NASABA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

Wakilinmu da ke wurin, ya ruwaito cewa yayin da zanga-zangar ta PDP, Cole tare da shugaban jam’iyyar APC na jihar Emeka Beke da wasu jiga-jigan jam’iyyar sun hallara a ttitin Aba, inda suka nufi ofishin INE

Matasan da suka yi zanga-zangar sun garzaya zuwa wajensa, inda suka yi ta jifansa da duwatsu da ledar ruwa.

Nan take jami’an tsaro da ke tare da Cole suka yi masa garkuwa tare da saka shi cikin mota, amma duk da hakan masu zangar-zangar suka ci gaba da jifansa.

Cikin dakika kadan sojojin runduna ta 6 ta sojojin Nijeriya da jami’an ‘yan sanda da jami’an tsaron farin kaya da na Sibil Difens suka isa inda suka dinga harbi a iska domin tarwatsa masu zanga-zangar.

Wani ganau ya shaida wa wakilinmu cewa, daya daga cikin jami’an tsaron da ke aiki da Cole ne ya harbi daya daga cikin masu zanga-zanagr.

Mutumin ya zubar da jini sosai sakamakon harbin da aka yi masa a kafarsa.

 Daga baya abokansa sun kai shi asibiti.

Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, al’amura bas u daidaita a yankin ba.

MASU ALAKA

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan
Manyan Labarai

‘Yan Ƙasar Turkiyya Sun Nuna Jarumta Da Kare Dimokuraɗiyya Mafi Girma A Tarihi – Erdoğan

July 15, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Lalata Da Ƙaramar Yarinya: Kotu Ta Yanke Wa Tsoho Mai Shekara 75 Hukuncin Ɗaurin Shekara 10 A Ribas

July 15, 2026
‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sace Shugaban Makaranta, Jami’in NECO Da Ɗalibai A Kogi

July 15, 2026
Next Post
Cibiyar Kananan Kayayyaki Ta Sin Ta Yi Cinikayyar Sama Da RMB Biliyan 1 Ta Yanar Gizo

Cibiyar Kananan Kayayyaki Ta Sin Ta Yi Cinikayyar Sama Da RMB Biliyan 1 Ta Yanar Gizo

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.