• English
  • Business News
Sunday, July 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutane Da Yawa Sun Jikkata Yayin Da Magoya Bayan PDP Da APC Suka Yi Arangama A Ribas

by Sadiq
2 years ago
in Manyan Labarai
0
Mutane Da Yawa Sun Jikkata Yayin Da Magoya Bayan PDP Da APC Suka Yi Arangama A Ribas
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Mutane da dama sun samu raunuka a ranar Litinin yayin da magoya bayan jam’iyyar PDP da APC suka arangama a garin Fatakwal na Jihar Ribas.

Daya daga cikin wadanda suka jikkata shi ne dan takarar gwamna na jam’iyyar APC a zaben gwamnan da aka yi a ranar 18 ga watan Maris, Tonye Cole, wanda ya samu rauni a wuyansa.

  • Dubi Ga Sabbin Hanyoyin Kutse A Facebook, WhatsApp Da Asusun Ajiyar Banki
  • Farashin Danyen Mai Ya Tashi A Kasuwar Duniya

Tun da farko dai wasu ‘yan jam’iyyar PDP sun yi zanga-zanga a kofar ofishin hukumar zabe mai zaman kanta (INEC) da ke kan titin Aba a Fatakwal.

Masu zanga-zangar dai sun bukaci duba kayan zaben da dukkanin jam’iyyun siyasa suka yi.

Jam’iyyar APC a karkashin dan takararta na gwamna a ranar Juma’ar da ta gabata ta ce za ta mamaye ofishin INEC a ranar Litinin domin neman a fitar da sahihin sakamakon da aka yi amfani da su wajen zaben gwamna da aka yi a ranar 18 ga watan Maris domin bai wa jam’iyyar damar shigar da karar a kotun sauraren kararrakin zabe.

Labarai Masu Nasaba

2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu

Shettima Ya Ziyarci Buhari A Landan Cikin Sirri Don Duba Lafiyarsa

Wakilinmu da ke wurin, ya ruwaito cewa yayin da zanga-zangar ta PDP, Cole tare da shugaban jam’iyyar APC na jihar Emeka Beke da wasu jiga-jigan jam’iyyar sun hallara a ttitin Aba, inda suka nufi ofishin INE

Matasan da suka yi zanga-zangar sun garzaya zuwa wajensa, inda suka yi ta jifansa da duwatsu da ledar ruwa.

Nan take jami’an tsaro da ke tare da Cole suka yi masa garkuwa tare da saka shi cikin mota, amma duk da hakan masu zangar-zangar suka ci gaba da jifansa.

Cikin dakika kadan sojojin runduna ta 6 ta sojojin Nijeriya da jami’an ‘yan sanda da jami’an tsaron farin kaya da na Sibil Difens suka isa inda suka dinga harbi a iska domin tarwatsa masu zanga-zangar.

Wani ganau ya shaida wa wakilinmu cewa, daya daga cikin jami’an tsaron da ke aiki da Cole ne ya harbi daya daga cikin masu zanga-zanagr.

Mutumin ya zubar da jini sosai sakamakon harbin da aka yi masa a kafarsa.

 Daga baya abokansa sun kai shi asibiti.

Har zuwa lokacin hada wannan rahoto, al’amura bas u daidaita a yankin ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCArangamaPDPRibas
ShareTweetSendShare
Previous Post

Xi Ya Amsa Wasikar Da Wakilan Masu Fasaha Na Larabawa Suka Rubuta Masa

Next Post

Cibiyar Kananan Kayayyaki Ta Sin Ta Yi Cinikayyar Sama Da RMB Biliyan 1 Ta Yanar Gizo

Related

2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu
Manyan Labarai

2027: Shugabannin Hamayya Sun Bazama Neman Goyon Baya A Yankunansu

17 hours ago
Fadar Shugaban Ƙasa Ta Ƙaryata Alaƙanta Shettima Da Kwatanta Jonathan Da Tinubu Kan Batun Tsige Gwamna
Labarai

Shettima Ya Ziyarci Buhari A Landan Cikin Sirri Don Duba Lafiyarsa

18 hours ago
Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa
Kotu Da Ɗansanda

Sojoji Sun Cafke Wani Soja Kan Mutuwar Mai Gyaran Waya A Adamawa

20 hours ago
Kotu Ta Umarci Majalisar Dattijan Nijeriya Da Ta Gaggauta Janye Dakatarwar Da Ta Yi Wa Natasha
Manyan Labarai

Lauyoyin Natasha Sun Buƙaci Ta Koma Majalisa Ranar Talata Bayan Miƙa Takardun Hukuncin Kotu

20 hours ago
Sojoji Sun Sake Ceto ‘Yan Matan Makarantar Chibok 2
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kama Mutum 2 Da AK-47 A Taraba

2 days ago
Shafin Yanar Gizo Na ADC Ya Tsaya Cak Saboda Ɗumbin Magoya Baya Masu Son Yin Rijista
Manyan Labarai

Shugabannin Jam’iyyar ADC Na Jihohi 36 Da Abuja Sun Bayyana Goyon Bayansu Ga David Mark

2 days ago
Next Post
Cibiyar Kananan Kayayyaki Ta Sin Ta Yi Cinikayyar Sama Da RMB Biliyan 1 Ta Yanar Gizo

Cibiyar Kananan Kayayyaki Ta Sin Ta Yi Cinikayyar Sama Da RMB Biliyan 1 Ta Yanar Gizo

LABARAI MASU NASABA

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

NAFDAC Da Masu Maganin Gargajiya Za Su Tsabtace Sana’ar Sayar Da Maganin Gargajiya A Nijeriya

July 12, 2025
Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

Shugaban Guinea Bissau Ya Bayyana Sin A Matsayin Abokiyar Hulda Ta Hakika

July 12, 2025
Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

Akwai Bukatar Manyan Jaruman Da Suka Yi Kudi Su Taimaki Na Baya -Barau Dadin Kowa

July 12, 2025
Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

Wang Yi Ya Yi Karin Haske Game Da Taron Ministocin Harkokin Wajen Sin Da Amurka 

July 12, 2025
Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

Yadda Iyaye Ke Rungumar Bokaye Don Samar Wa ‘Ya’yansu Mata Mazaje Masu Kudi

July 12, 2025
Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

Sin Ta Yi Kira Da A Karfafa Hadin Gwiwa A Fannin Tattalin Arziki Na Zamani

July 12, 2025
Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

Tinubu Ya Baro Brazil Bayan Halartar Taron BRICS Na 2025

July 12, 2025
Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

Shugaban Nauru: Ci Gaban Sin Darasi Ne Ga Nauru Da Duniya Baki Daya

July 12, 2025
Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

Tinubu Yana Goyon Bayan Ƙananan Hukumomi Su Ci Gashin Kan Su – Minista

July 12, 2025
Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

Danbun Shinkafa Da Nama Da Kifi

July 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.