• English
  • Business News
Wednesday, October 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutanen Da Suka Mutu A Harin Ƙunar Baƙin-Wake A Wajen Bikin Aure Ya Ƙaru Zuwa 18 A Borno

by Muhammad
1 year ago
Borno

A wani rahoto da Hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Borno, BOSEMA, ta fitar ta ce adadin wadanda suka mutu a sakamakon harin kunar bakin wake da aka kai a garin Gwoza da ke Karamar Hukumar Gwoza a ranar Asabar zuwa yanzu ya kai mutum 18, inda aka tabbatar da mutum 19 kuma sun samu raunuka.

LEADERSHIP HAUSA ta ce jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar, ASP Nahum Daso, a ranar Asabar ya tabbatar da mutuwar mutane 8 tare da wasu mutane 15 da suka samu raunuka a yayin harin kunar bakin waken.

  • Mutun 6 Sun Mutu Harin Ƙunar Ɓakin Wake a Borno
  • Boko Haram Sun Sace Wani Alkali Da Matarsa Tare Da Awon-Gaba Da Wasu Mutane A Borno

Kazalika, wani karin bayani da Darakta Janar na BOSEMA, Dr. Barkindo Saidu, ya fitar wanda aka rabawa manema labarai a ranar Lahadin ya bayyana cewa adadin wadanda suka mutu a daren ranar Asabar ya kai 18, yayin da 19 da suka samu raunuka daban-daban inda yanzu haka suna jinya a asibitocin Maiduguri.

Dr. Saidu, ya ce akan idonsa, da misalin karfe 3 na yammacin ranar Asabar, bam na farko ya tashi a Gwoza, wanda wata ‘yar kunar bakin wake ta tayar da bam a wajen bikin aure.

Ya kara da cewa sama da mutane 30 ne abin ya shafa tare da raunuka daban-daban inda wasu kuma suka mutu nan take.

LABARAI MASU NASABA

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

Majalisar Dattawa Ta Maido Da Ranar Tantance Sabbin Shugabannin Sojoji Zuwa Laraba

Dr. Saidu ya ce bayan ‘yan wasu mintoci, an sake samun fashewar wani abun fashewa a kusa da babban asibitin da ke garin.

A safiyar Lahadi, wata majiya daga BOSEMA da ta nemi bukaci a sakaya sunanta ta ce, adadin yawan mutanen suka mutu na iya zarce 18 idan aka yi la’akari da girman raunukan da suka samu.

A gefe guda kuma wata majiyar ta yi zargin cewa sama da gawar mutane 25 aka dauko daga wurare uku kafin sojoji su rufe hedikwatar karamar hukumar tare da sanya dokar hana fita da yammacin ranar Asabar.

Wakilinmu LEADERSHIP HAUSA ya ruwaito cewa, Gwoza na daya daga cikin kananan hukumomin da ‘yan ta’addar Boko Haram suka kwace a baya inda suka ayyana ta a matsayin mallakin su.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260
Manyan Labarai

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
gaza
Manyan Labarai

Majalisar Dattawa Ta Maido Da Ranar Tantance Sabbin Shugabannin Sojoji Zuwa Laraba

October 28, 2025
An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato
Manyan Labarai

An Matsa Min Sai Na Koma Jam’iyyar APC – Gwamnan Filato

October 28, 2025
Next Post
“Abin Da Ake Zargin Ɗan Jarida Shuaibu Mungadi Ba Gaskiya Ba Ne”

"Abin Da Ake Zargin Ɗan Jarida Shuaibu Mungadi Ba Gaskiya Ba Ne"

LABARAI MASU NASABA

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

Firaministan Sin Ya Yi Kira Da A Kara Bude Kofa Da Karfafa Daidaita Dabarun Samar Da Ci Gaba

October 28, 2025
JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

JIBWIS Ta Miƙa Takardar Koke Ga Gwamnatin Kaduna Kan Zargin Wasu Malamai Da Yunƙurin Tada Husuma

October 28, 2025
An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

An Gudanar Da Taron Musamman Na Tattaunawa Tsakanin Sassan Kasa Da Kasa A Afrika Da Kudu

October 28, 2025
Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

Zamfara Ta Fara Sauyawa Zuwa Jihar Fasahar Zamani, In ji Gwamna Lawal

October 28, 2025
Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

Masanan Kasar Sin Da Afirka Sun Hada Karfi Da Karfe Don Habaka Samun Wadatar Abinci Da Zamanantar Da Aikin Gona

October 28, 2025
Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

Rikicin Manoma Da Makiyaya Ya Yi Ajali Tare Da Jikkata Wasu A Gombe

October 28, 2025
Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

Kuri’un Jin Ra’ayin Jama’a Na CGTN Sun Nuna Gamsuwar Jama’a Ga Tsarin Jagoranci Na Sin

October 28, 2025
Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

Kano Ta Bai Wa Mata 5,200 Tallafin Naira Miliyan 260

October 28, 2025
An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

An Kusa Kammala Shirye-shiryen Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas

October 28, 2025
Gwamna Bago Ya Amince Da Biyan Karin Albashin Naira 20,000 Ga Ma’aikata 

Gwamnatin Neja Ta Bayar Da Hutun Kwanaki 2 Don Zaɓen Ƙananan Hukumomi

October 28, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.