ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutanen Da Suka Mutu A Harin Ƙunar Baƙin-Wake A Wajen Bikin Aure Ya Ƙaru Zuwa 18 A Borno

by Muhammad
2 years ago
Borno

A wani rahoto da Hukumar bayar da agajin gaggawa ta jihar Borno, BOSEMA, ta fitar ta ce adadin wadanda suka mutu a sakamakon harin kunar bakin wake da aka kai a garin Gwoza da ke Karamar Hukumar Gwoza a ranar Asabar zuwa yanzu ya kai mutum 18, inda aka tabbatar da mutum 19 kuma sun samu raunuka.

LEADERSHIP HAUSA ta ce jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yansandan jihar, ASP Nahum Daso, a ranar Asabar ya tabbatar da mutuwar mutane 8 tare da wasu mutane 15 da suka samu raunuka a yayin harin kunar bakin waken.

  • Mutun 6 Sun Mutu Harin Ƙunar Ɓakin Wake a Borno
  • Boko Haram Sun Sace Wani Alkali Da Matarsa Tare Da Awon-Gaba Da Wasu Mutane A Borno

Kazalika, wani karin bayani da Darakta Janar na BOSEMA, Dr. Barkindo Saidu, ya fitar wanda aka rabawa manema labarai a ranar Lahadin ya bayyana cewa adadin wadanda suka mutu a daren ranar Asabar ya kai 18, yayin da 19 da suka samu raunuka daban-daban inda yanzu haka suna jinya a asibitocin Maiduguri.

ADVERTISEMENT

Dr. Saidu, ya ce akan idonsa, da misalin karfe 3 na yammacin ranar Asabar, bam na farko ya tashi a Gwoza, wanda wata ‘yar kunar bakin wake ta tayar da bam a wajen bikin aure.

Ya kara da cewa sama da mutane 30 ne abin ya shafa tare da raunuka daban-daban inda wasu kuma suka mutu nan take.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Dr. Saidu ya ce bayan ‘yan wasu mintoci, an sake samun fashewar wani abun fashewa a kusa da babban asibitin da ke garin.

A safiyar Lahadi, wata majiya daga BOSEMA da ta nemi bukaci a sakaya sunanta ta ce, adadin yawan mutanen suka mutu na iya zarce 18 idan aka yi la’akari da girman raunukan da suka samu.

A gefe guda kuma wata majiyar ta yi zargin cewa sama da gawar mutane 25 aka dauko daga wurare uku kafin sojoji su rufe hedikwatar karamar hukumar tare da sanya dokar hana fita da yammacin ranar Asabar.

Wakilinmu LEADERSHIP HAUSA ya ruwaito cewa, Gwoza na daya daga cikin kananan hukumomin da ‘yan ta’addar Boko Haram suka kwace a baya inda suka ayyana ta a matsayin mallakin su.

Borno
Muhammad
+ postsBio
  • Muhammad
    Yadda Na Tsira Daga Cutar Mashaƙo A Katsina: “Na Fara Da Tsartuwar Jini Tare Da Yawu”
  • Muhammad
    An Naɗa Yusuf Nasidi Nasir A Matsayin Talban Barayan Kano
  • Muhammad
    Wani Kamfani Ya Tallafa Wa Masu Sana’ar Shayi A Kano
  • Muhammad
    Kosan Waka Ya Rasu, Gwamnan Kano Ya Jajanta Wa Iyalansa

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
“Abin Da Ake Zargin Ɗan Jarida Shuaibu Mungadi Ba Gaskiya Ba Ne”

"Abin Da Ake Zargin Ɗan Jarida Shuaibu Mungadi Ba Gaskiya Ba Ne"

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.