• English
  • Business News
Monday, October 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutum 18 Sun Kone Kurmus A Hatsarin Mota A Bauchi

by Khalid Idris Doya
3 years ago
hatsarin mota

Hukumar kiyaye aukuwar hadura ta kasa (FRSC) reshen jihar Bauchi ta tabbatar da cewa mutane goma sha takwas (18) ne suka kone kurmus har ma ba a iya tantance su a wani mummunar hatsarin mota da ya faru gaf da kauyen Nabardo da ke cikin karamar hukumar Toro a kan babbar hanyar Bauchi zuwa Jos. 

 

Hatsarin wanda ya kunshi motoci biyu motar kabu-kabu Toyota Hiace Bus mai lamba: FKE 688 YC da wata katuwar Tirela inda suka yi taho-mu-kara da juna.

  • 15 Sun Mutu, 5 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kogi – FRSC 

Da ya ke tabbatar da faruwar lamarin, Kwamandan shiyya na hukumar, Malam Yusuf Abdullahi, ya ce, hatsarin ya faru ne da yammacin ranar Laraba, ya ce mutum 21 ne hatsarin ya shafa da suka hada da manyan mutane Maza 18 da kuma yara uku.

 

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Gwamnan Jigawa, Lamido Ya Bayyana Aniyar Takarar Shugabancin Jam’iyyar PDP Na Ƙasa

Sojoji Sun Kashe ‘Yan ta’adda 10, Sun Ƙwato Makamai A Borno

Ya nuna matukar takaicinsa bisa faruwar hatsarin duk da kokarin da suke yi ba dare ko rana wajen wayar da kan direbobi wajen ganin sun kauce wa tukin ganganci da gudun wuce kima amma sun kasa bin matakan da ake son su bi.

 

“Abun bakin ciki da takaici ne gaskiya. Kullum sai mun shafe sama da awa biyu muna wayar wa direbobi kai kan tukin wuce kima amma ina ba su ji.

 

“Yanzu ka duba wannan hatsarin da ya faru direban Bas din da dukkanin fasinjojinsa sun kone sun zama toka ba a ma iya gane kowa a cikinsu.

 

“Abun bakin cikin da ya faru da yammacin ranar Laraba mutum 18 suka mutu a mummunar hatsarin da ya faru kasa da kilomita uku zuwa kauyen Nabardo da ke kan hanyar Bauchi zuwa Jos.”

 

Ya ce, hatsarin ya faru ne sakamakon kauye wa ka’idojin tuki, “Mun fahimci cewa direban Bas din ya rasa shawo kan ikon motar ne wanda hakan ya sanya ya fita daga kan layinsa inda ya doshi inda Tirela take suka kara kuma kun san wurin ajiyar Mai na Hummer na kusa da injinta ne.

 

“Lamarin ya janyo karawa a tsakanin motocin biyu. Hatsarin kuma ya faru ne a cikin daji babu mutane a wajen balle su kai aikin gaggawa garesu. Dukkanin mutanen cikin motar ‘Bas’ da fasinjojinsa sun kone kurmus,” ya shaida.

 

Shugaban ya kara da cewa ‘yan sanda da jami’an ma’aikatar kula da walwala da jin dadi za su kula da yi musu jana’izar bai-daya.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

hatsarin mota
Labarai

Tsohon Gwamnan Jigawa, Lamido Ya Bayyana Aniyar Takarar Shugabancin Jam’iyyar PDP Na Ƙasa

October 27, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan ta’adda 10, Sun Ƙwato Makamai A Borno
Manyan Labarai

Sojoji Sun Kashe ‘Yan ta’adda 10, Sun Ƙwato Makamai A Borno

October 27, 2025
Hatsarin Jiragen Ruwa
Labarai

Matasa 5 Sun Mutu A Hatsarin Jirgin Ruwa A Gombe

October 27, 2025
Next Post
NDLEA Ta Cafke Mutum 1,232 Da Miyagun Kwayoyi A Kaduna

NDLEA Ta Cafke Mutum 1,232 Da Miyagun Kwayoyi A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

hatsarin mota

Tsohon Gwamnan Jigawa, Lamido Ya Bayyana Aniyar Takarar Shugabancin Jam’iyyar PDP Na Ƙasa

October 27, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan ta’adda 10, Sun Ƙwato Makamai A Borno

Sojoji Sun Kashe ‘Yan ta’adda 10, Sun Ƙwato Makamai A Borno

October 27, 2025
Hatsarin Jiragen Ruwa

Matasa 5 Sun Mutu A Hatsarin Jirgin Ruwa A Gombe

October 27, 2025
Tunawa Da Dawowar Taiwan Kasar Sin Shekaru 80 Da Suka Wuce Yana Da Ma’ana Sosai

Tunawa Da Dawowar Taiwan Kasar Sin Shekaru 80 Da Suka Wuce Yana Da Ma’ana Sosai

October 26, 2025
Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

Matatar Dangote Za Ta Faɗaɗa Ƙarfin Aiki Zuwa Ganga Miliyan 1.4 Kullum

October 26, 2025
Kara Bude Kofofin Sin Zai Samar Da Karin Gajiya A Fannin Bunkasar Duniya

Kara Bude Kofofin Sin Zai Samar Da Karin Gajiya A Fannin Bunkasar Duniya

October 26, 2025
“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”

“Ba Gudu Ba Ja Da Baya Game Da Tsarin “Call-up system” A NPA”

October 26, 2025
Ya Zuwa Satumban Bana Adadin Lantarki Da Sin Ta Samar Ya Karu Da Kaso 17.5%

Ya Zuwa Satumban Bana Adadin Lantarki Da Sin Ta Samar Ya Karu Da Kaso 17.5%

October 26, 2025
Dalilin Da Suka Sa Hisbah Ta Dakatar Da Auren Ƴan TikTok A Kano

Dalilin Da Suka Sa Hisbah Ta Dakatar Da Auren Ƴan TikTok A Kano

October 26, 2025
Gwarzon Gwamnan 2025, Biodun Abayomi Oyebanji

Gwarzon Ma’aikacin Gwamnati Na Shekarar 2025, Dakta Zacch Adedeji

October 26, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.