• English
  • Business News
Sunday, October 5, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutum 18 Sun Kone Kurmus A Hatsarin Mota A Bauchi

by Khalid Idris Doya
3 years ago
in Labarai
0
Mutum 18 Sun Kone Kurmus A Hatsarin Mota A Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar kiyaye aukuwar hadura ta kasa (FRSC) reshen jihar Bauchi ta tabbatar da cewa mutane goma sha takwas (18) ne suka kone kurmus har ma ba a iya tantance su a wani mummunar hatsarin mota da ya faru gaf da kauyen Nabardo da ke cikin karamar hukumar Toro a kan babbar hanyar Bauchi zuwa Jos. 

 

Hatsarin wanda ya kunshi motoci biyu motar kabu-kabu Toyota Hiace Bus mai lamba: FKE 688 YC da wata katuwar Tirela inda suka yi taho-mu-kara da juna.

  • 15 Sun Mutu, 5 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kogi – FRSC 

Da ya ke tabbatar da faruwar lamarin, Kwamandan shiyya na hukumar, Malam Yusuf Abdullahi, ya ce, hatsarin ya faru ne da yammacin ranar Laraba, ya ce mutum 21 ne hatsarin ya shafa da suka hada da manyan mutane Maza 18 da kuma yara uku.

 

Labarai Masu Nasaba

NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridan Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

Ranar Malamai ta Duniya: Ƙungiyar NUT Ta Koka Kan Ƙarancin Malamai 194,000 A Nijeriya

Ya nuna matukar takaicinsa bisa faruwar hatsarin duk da kokarin da suke yi ba dare ko rana wajen wayar da kan direbobi wajen ganin sun kauce wa tukin ganganci da gudun wuce kima amma sun kasa bin matakan da ake son su bi.

 

“Abun bakin ciki da takaici ne gaskiya. Kullum sai mun shafe sama da awa biyu muna wayar wa direbobi kai kan tukin wuce kima amma ina ba su ji.

 

“Yanzu ka duba wannan hatsarin da ya faru direban Bas din da dukkanin fasinjojinsa sun kone sun zama toka ba a ma iya gane kowa a cikinsu.

 

“Abun bakin cikin da ya faru da yammacin ranar Laraba mutum 18 suka mutu a mummunar hatsarin da ya faru kasa da kilomita uku zuwa kauyen Nabardo da ke kan hanyar Bauchi zuwa Jos.”

 

Ya ce, hatsarin ya faru ne sakamakon kauye wa ka’idojin tuki, “Mun fahimci cewa direban Bas din ya rasa shawo kan ikon motar ne wanda hakan ya sanya ya fita daga kan layinsa inda ya doshi inda Tirela take suka kara kuma kun san wurin ajiyar Mai na Hummer na kusa da injinta ne.

 

“Lamarin ya janyo karawa a tsakanin motocin biyu. Hatsarin kuma ya faru ne a cikin daji babu mutane a wajen balle su kai aikin gaggawa garesu. Dukkanin mutanen cikin motar ‘Bas’ da fasinjojinsa sun kone kurmus,” ya shaida.

 

Shugaban ya kara da cewa ‘yan sanda da jami’an ma’aikatar kula da walwala da jin dadi za su kula da yi musu jana’izar bai-daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bayan Tube Wa Mahaifinta Rawani, Kwamishina Ta Yi Murabus A Bauchi

Next Post

NDLEA Ta Cafke Mutum 1,232 Da Miyagun Kwayoyi A Kaduna

Related

NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridan Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC
Labarai

NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridan Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

19 minutes ago
Ranar Malamai ta Duniya: Ƙungiyar NUT Ta Koka Kan Ƙarancin Malamai 194,000 A Nijeriya
Labarai

Ranar Malamai ta Duniya: Ƙungiyar NUT Ta Koka Kan Ƙarancin Malamai 194,000 A Nijeriya

3 hours ago
Sanata Ndume Ya Yaba Wa Gwamna Zulum Kan Shirinsa Na Tura Sojoji Kirawa
Labarai

Sanata Ndume Ya Yaba Wa Gwamna Zulum Kan Shirinsa Na Tura Sojoji Kirawa

4 hours ago
Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

6 hours ago
Ban Bar PDP Ba, Ina Gangamin Hadin Gwiwa Ne Don Tunkarar APC A 2027 – Atiku
Labarai

Atiku Ya Zargi Tinubu Da Fifita Ziyarar Siyasa A Maimaikon Ta Waɗanda Rashin Tsaro Ya Shafa 

7 hours ago
Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 
Labarai

Fitatccen Ɗan Jarida A Kano Aliyu Abubakar Getso Ya Rigamu Gidan Gaskiya 

7 hours ago
Next Post
NDLEA Ta Cafke Mutum 1,232 Da Miyagun Kwayoyi A Kaduna

NDLEA Ta Cafke Mutum 1,232 Da Miyagun Kwayoyi A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

Yawan Mutanen Da Suka Yi Zirga-zirga A Rabin Farkon Hutun Bikin Kafuwar PRC Da Bikin Zhongqiu Ya Kai Biliyan 1 Da Miliyan 243

October 5, 2025
NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridan Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

NUJ Ta Yi Maraba Da Sakin Ƴan Jaridan Da DSS Ta Kama A Jana’izar Mahaifiyar Shugaban APC

October 5, 2025
Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

Kamfanin Sin Ya Kaddamar Da Ginin Katafaren Wurin Shakatawa Na Zamani A Ghana

October 5, 2025
Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

Uwargidan Shugaban Ƙasa, Remi Tinubu, Ta Nuna Damuwa Kan Ƙarancin Malamai A Duniya

October 5, 2025
Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

Za A Gudanar Da Taron Motoci Masu Amfani Da Fasahohin Zamani Na Duniya Na Shekarar 2025 A Beijing

October 5, 2025
Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

Ministan Harkokin Wajen Sin Zai Ziyarci Italiya Da Switzerland

October 5, 2025
Ranar Malamai ta Duniya: Ƙungiyar NUT Ta Koka Kan Ƙarancin Malamai 194,000 A Nijeriya

Ranar Malamai ta Duniya: Ƙungiyar NUT Ta Koka Kan Ƙarancin Malamai 194,000 A Nijeriya

October 5, 2025
Sanata Ndume Ya Yaba Wa Gwamna Zulum Kan Shirinsa Na Tura Sojoji Kirawa

Sanata Ndume Ya Yaba Wa Gwamna Zulum Kan Shirinsa Na Tura Sojoji Kirawa

October 5, 2025
Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

Gwamna Dauda Lawal Ya Yi Alhinin Rasuwar Dattijo, Ambasada Jabbi Maradun

October 5, 2025
Ban Bar PDP Ba, Ina Gangamin Hadin Gwiwa Ne Don Tunkarar APC A 2027 – Atiku

Atiku Ya Zargi Tinubu Da Fifita Ziyarar Siyasa A Maimaikon Ta Waɗanda Rashin Tsaro Ya Shafa 

October 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.