• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutum 18 Sun Kone Kurmus A Hatsarin Mota A Bauchi

by Khalid Idris Doya
2 years ago
in Labarai
0
Mutum 18 Sun Kone Kurmus A Hatsarin Mota A Bauchi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar kiyaye aukuwar hadura ta kasa (FRSC) reshen jihar Bauchi ta tabbatar da cewa mutane goma sha takwas (18) ne suka kone kurmus har ma ba a iya tantance su a wani mummunar hatsarin mota da ya faru gaf da kauyen Nabardo da ke cikin karamar hukumar Toro a kan babbar hanyar Bauchi zuwa Jos. 

 

Hatsarin wanda ya kunshi motoci biyu motar kabu-kabu Toyota Hiace Bus mai lamba: FKE 688 YC da wata katuwar Tirela inda suka yi taho-mu-kara da juna.

  • 15 Sun Mutu, 5 Sun Jikkata A Hatsarin Mota A Kogi – FRSC 

Da ya ke tabbatar da faruwar lamarin, Kwamandan shiyya na hukumar, Malam Yusuf Abdullahi, ya ce, hatsarin ya faru ne da yammacin ranar Laraba, ya ce mutum 21 ne hatsarin ya shafa da suka hada da manyan mutane Maza 18 da kuma yara uku.

 

Labarai Masu Nasaba

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Ya nuna matukar takaicinsa bisa faruwar hatsarin duk da kokarin da suke yi ba dare ko rana wajen wayar da kan direbobi wajen ganin sun kauce wa tukin ganganci da gudun wuce kima amma sun kasa bin matakan da ake son su bi.

 

“Abun bakin ciki da takaici ne gaskiya. Kullum sai mun shafe sama da awa biyu muna wayar wa direbobi kai kan tukin wuce kima amma ina ba su ji.

 

“Yanzu ka duba wannan hatsarin da ya faru direban Bas din da dukkanin fasinjojinsa sun kone sun zama toka ba a ma iya gane kowa a cikinsu.

 

“Abun bakin cikin da ya faru da yammacin ranar Laraba mutum 18 suka mutu a mummunar hatsarin da ya faru kasa da kilomita uku zuwa kauyen Nabardo da ke kan hanyar Bauchi zuwa Jos.”

 

Ya ce, hatsarin ya faru ne sakamakon kauye wa ka’idojin tuki, “Mun fahimci cewa direban Bas din ya rasa shawo kan ikon motar ne wanda hakan ya sanya ya fita daga kan layinsa inda ya doshi inda Tirela take suka kara kuma kun san wurin ajiyar Mai na Hummer na kusa da injinta ne.

 

“Lamarin ya janyo karawa a tsakanin motocin biyu. Hatsarin kuma ya faru ne a cikin daji babu mutane a wajen balle su kai aikin gaggawa garesu. Dukkanin mutanen cikin motar ‘Bas’ da fasinjojinsa sun kone kurmus,” ya shaida.

 

Shugaban ya kara da cewa ‘yan sanda da jami’an ma’aikatar kula da walwala da jin dadi za su kula da yi musu jana’izar bai-daya.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Bayan Tube Wa Mahaifinta Rawani, Kwamishina Ta Yi Murabus A Bauchi

Next Post

NDLEA Ta Cafke Mutum 1,232 Da Miyagun Kwayoyi A Kaduna

Related

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa
Manyan Labarai

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

1 hour ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

2 hours ago
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara
Manyan Labarai

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

4 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

9 hours ago
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

10 hours ago
Ganduje Ba Zai Hana Kwankwaso Shiga APC Ba
Labarai

Murabus Ɗin Ganduje: ‘Yan Kwankwasiyya Na Shirin Ɗaukar Wani Mataki

11 hours ago
Next Post
NDLEA Ta Cafke Mutum 1,232 Da Miyagun Kwayoyi A Kaduna

NDLEA Ta Cafke Mutum 1,232 Da Miyagun Kwayoyi A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

Adadin Mambobin JKS Na Karuwa Yayin Da Rassanta A Matakin Farko Ke Karuwa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.