• English
  • Business News
Sunday, June 29, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutum 2,629,025 Ke Da Wuƙa Da Namar Zabo Sabon Gwamnan Edo -INEC 

by Yusuf Shuaibu
10 months ago
in Labarai, Siyasa
0
Mutum 2,629,025 Ke Da Wuƙa Da Namar Zabo Sabon Gwamnan Edo -INEC 
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta bayyana cewa masu kada kuri’a miliyan 2,629,025 ne za su zabi sabon gwamnan Jihar Edo, a zaben da za a yi a ranar 21 ga watan Satumba.

Kwamishiniyar INEC mai sa ido da ke kula da jihohin Edo, Delta da Kuros Riba, Farfesa Rhoda Gumus, ta bayyana haka a ofishin hukumar da ke Benin a wajen gabatar da rajistar masu kada kuri’a ga shugabanni da wakilan jam’iyyun siyasa 16 da suka shiga zaben.

  • Zaben Ondo: 20 Ga Mayu Ita Ce Ranar Mika Sunayen ‘Yan Takara Ta Karshe – INEC
  • Laifukan Zabe Barazana Ne Ga Samun Sahihan Zabuka A Nijeriya – INEC

Gumus ta ce, “A bisa dokar zabe ta 2022, tilas ne INEC ta gabatar da rajistar masu zabe ga shugabannin jam’iyyun siyasa nan da kwanaki 30 kafin zaben. Muna kokarin bin doka da oda tare da aiwatar da ayyuka 10 cikin 13 da aka shirya gudanarwa a zaben gwamnan Edo.”

Yayin da take jaddada bukatar a gudanar da zaben cikin lumana, Gumus ta ce, “Bai kamata zabe ya zama ko a mutu ko a yi rai ba. Idan ba ku ci nasara ba a yau, kuna iya yin nasara a gobe. Matsaloli kullum suna tashi a ranar zabe. ‘Yan siyasa da magoya bayansu a Jihar Edo su guji tashin hankali.

“INEC ta shirya tsaf domin gudanar da zaben gwamna a Jihar Edo. Muna son masu ruwa da tsaki su bai wa hukumar zabe hadin kai domin ganin ayyukan kafin zabe da lokacin zabe da kuma bayan zabe sun gudana yadda ake bukata. Ina ba da tabbacin cewa tare da goyon bayan jami’an tsaro za a gudanar da zaben cikin kwanciyar hankali da walwala.”

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Kwamishiniyar ta kasa mai sa ido kuma bukaci mazauna Edo da sauran ‘yan Nijeriya da su yi alfahari da kasarsu, kuma ka da su bari kabila ko harshe ya raba su.

Tun da farko kwamishinan zabe a Jihar Edo, Dakta Anugbum Onuoha, ya sake nanata cewa mutane 2,501,081 ne aka yi wa rajista a jihar domin zaben 2023, yayin da mutane 173,048 suka yi rajista a ci gaba da rajistar masu kada kuri’a daga ranar 27 ga watan Mayu zuwa 9 ga watan Yuni, 2024. Masu rajista 119,206, ciki har da wadanda suka sauya katin zabensu suka cancanta, wanda hakan ya kawo adadin masu kada kuri’a 2,501,081.

Onuoha ya ce za a dakatar da yakin neman zabe a ranar 19 ga watan Satumba, yayin da zaben gwamnan Edo zai gudana a ranar 21 ga watan Satumba.

Shugaban majalisar hadakan jam’iyyu a Edo, Greg Igbinomwanhia, wanda kuma shi ne shugaban jam’iyyar ‘Redemption’ na jihar, ya yaba wa INEC kan yadda ta ke kokarin gudanar da ayyukan zaben ba tare da tangarda ba.

Igbinomwanhia ya kara da cewa zaben gwamnan Jihar Edo da za a yi a ranar 21 ga watan Satumba ba dole ne ya kasance an yi shi cikin ‘yanci da adalci da kuma zaman lafiya.

Ya bukaci shugabanni da magoya bayan jam’iyyun siyasa da su guji tashin hankali domin a zabi magajin Gwamna Godwin Obaseki ba tare da nuna adawa ba.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: ElectionFilatoZabe
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wasu Barayin Shanu Da Hatsabiban ‘Yan Bindiga Sun Shiga Hannu

Next Post

An Cafke Mutumin Da Ake Zargi Da Garkuwa Da Almajirai 2 A Bauchi

Related

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100
Labarai

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

11 minutes ago
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki
Manyan Labarai

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

2 hours ago
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25
Labarai

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

17 hours ago
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa
Manyan Labarai

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

17 hours ago
Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)
Labarai

Tarihin Yadda Cinikin Bayi Ya Fara A Nahiyar Afirka (3)

18 hours ago
An Kai Wa Magoya Bayan Atiku Hari A Gombe
Manyan Labarai

Rasuwar Dantata Babban Rashi Ne Ga Afirka – Atiku

18 hours ago
Next Post
An Cafke Mutumin Da Ake Zargi Da Garkuwa Da Almajirai 2 A Bauchi

An Cafke Mutumin Da Ake Zargi Da Garkuwa Da Almajirai 2 A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

Babu Irin Arziƙin Da Babu A Masana’antar Kannywood – Bashir Maishadda

June 29, 2025
Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

Gwamnatin Zamfara Ta Tabbatar Da Kashe Manyan Mayakan Bello Turji Fiye Da 100

June 29, 2025
Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

Tinubu Ya Isa Saint Lucia Domin Ziyarar Aiki

June 29, 2025
Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

Kasar Sin Ta Sake Ware Yuan Miliyan 100 Domin Tallafawa Lardin Guizhou Dake Fama Da Ambaliya 

June 28, 2025
An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

An Kaddamar Da Aikin Hadin-Gwiwar Kafafen Yada Labaran Sin Da Kasashen Waje Wajen Watsa Labarai Game Da Jihar Xizang Ta Kasar Sin

June 28, 2025
Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

Jakadun Kasa Da Kasa Sun Bayyana Muhimmancin Hadin Gwiwa Wajen Amfani Da Makamashin Nukiliya Ta Hanyar Lumana

June 28, 2025
Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

Kokarin Zamanantar Da Sin Da Afrika Na Kara Karfafa

June 28, 2025
Bashin Da Ake Bin Nijeriya Ya Kai Tiriliyan 46.25

Za A Ci Gaba Da Tunawa Da Aminu Ɗantata A Ɓangaren Taimakon Jama’a — Buhari

June 28, 2025
Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

Har Yanzu Ba Mu San Inda Za A Binne Dantata Ba — Sakatarensa

June 28, 2025
Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

Hukumar NPA Na Son Tara Kuɗaɗen Shiga Naira Tiriliyan 1.2 A 2025

June 28, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.