ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutum 2,629,025 Ke Da Wuƙa Da Namar Zabo Sabon Gwamnan Edo -INEC 

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Edo

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta bayyana cewa masu kada kuri’a miliyan 2,629,025 ne za su zabi sabon gwamnan Jihar Edo, a zaben da za a yi a ranar 21 ga watan Satumba.

Kwamishiniyar INEC mai sa ido da ke kula da jihohin Edo, Delta da Kuros Riba, Farfesa Rhoda Gumus, ta bayyana haka a ofishin hukumar da ke Benin a wajen gabatar da rajistar masu kada kuri’a ga shugabanni da wakilan jam’iyyun siyasa 16 da suka shiga zaben.

  • Zaben Ondo: 20 Ga Mayu Ita Ce Ranar Mika Sunayen ‘Yan Takara Ta Karshe – INEC
  • Laifukan Zabe Barazana Ne Ga Samun Sahihan Zabuka A Nijeriya – INEC

Gumus ta ce, “A bisa dokar zabe ta 2022, tilas ne INEC ta gabatar da rajistar masu zabe ga shugabannin jam’iyyun siyasa nan da kwanaki 30 kafin zaben. Muna kokarin bin doka da oda tare da aiwatar da ayyuka 10 cikin 13 da aka shirya gudanarwa a zaben gwamnan Edo.”

ADVERTISEMENT

Yayin da take jaddada bukatar a gudanar da zaben cikin lumana, Gumus ta ce, “Bai kamata zabe ya zama ko a mutu ko a yi rai ba. Idan ba ku ci nasara ba a yau, kuna iya yin nasara a gobe. Matsaloli kullum suna tashi a ranar zabe. ‘Yan siyasa da magoya bayansu a Jihar Edo su guji tashin hankali.

“INEC ta shirya tsaf domin gudanar da zaben gwamna a Jihar Edo. Muna son masu ruwa da tsaki su bai wa hukumar zabe hadin kai domin ganin ayyukan kafin zabe da lokacin zabe da kuma bayan zabe sun gudana yadda ake bukata. Ina ba da tabbacin cewa tare da goyon bayan jami’an tsaro za a gudanar da zaben cikin kwanciyar hankali da walwala.”

LABARAI MASU NASABA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Kwamishiniyar ta kasa mai sa ido kuma bukaci mazauna Edo da sauran ‘yan Nijeriya da su yi alfahari da kasarsu, kuma ka da su bari kabila ko harshe ya raba su.

Tun da farko kwamishinan zabe a Jihar Edo, Dakta Anugbum Onuoha, ya sake nanata cewa mutane 2,501,081 ne aka yi wa rajista a jihar domin zaben 2023, yayin da mutane 173,048 suka yi rajista a ci gaba da rajistar masu kada kuri’a daga ranar 27 ga watan Mayu zuwa 9 ga watan Yuni, 2024. Masu rajista 119,206, ciki har da wadanda suka sauya katin zabensu suka cancanta, wanda hakan ya kawo adadin masu kada kuri’a 2,501,081.

Onuoha ya ce za a dakatar da yakin neman zabe a ranar 19 ga watan Satumba, yayin da zaben gwamnan Edo zai gudana a ranar 21 ga watan Satumba.

Shugaban majalisar hadakan jam’iyyu a Edo, Greg Igbinomwanhia, wanda kuma shi ne shugaban jam’iyyar ‘Redemption’ na jihar, ya yaba wa INEC kan yadda ta ke kokarin gudanar da ayyukan zaben ba tare da tangarda ba.

Igbinomwanhia ya kara da cewa zaben gwamnan Jihar Edo da za a yi a ranar 21 ga watan Satumba ba dole ne ya kasance an yi shi cikin ‘yanci da adalci da kuma zaman lafiya.

Ya bukaci shugabanni da magoya bayan jam’iyyun siyasa da su guji tashin hankali domin a zabi magajin Gwamna Godwin Obaseki ba tare da nuna adawa ba.

Edo
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100
Siyasa

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
Next Post
An Cafke Mutumin Da Ake Zargi Da Garkuwa Da Almajirai 2 A Bauchi

An Cafke Mutumin Da Ake Zargi Da Garkuwa Da Almajirai 2 A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026
Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

Masana Kandagarkin Cututtuka Na Sin Sun Tashi Zuwa Kasar Uganda Don Aikin Hadin Gwiwar Magance Cutar Ebola

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.