ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 25, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutum 2,629,025 Ke Da Wuƙa Da Namar Zabo Sabon Gwamnan Edo -INEC 

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Edo

Hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta bayyana cewa masu kada kuri’a miliyan 2,629,025 ne za su zabi sabon gwamnan Jihar Edo, a zaben da za a yi a ranar 21 ga watan Satumba.

Kwamishiniyar INEC mai sa ido da ke kula da jihohin Edo, Delta da Kuros Riba, Farfesa Rhoda Gumus, ta bayyana haka a ofishin hukumar da ke Benin a wajen gabatar da rajistar masu kada kuri’a ga shugabanni da wakilan jam’iyyun siyasa 16 da suka shiga zaben.

  • Zaben Ondo: 20 Ga Mayu Ita Ce Ranar Mika Sunayen ‘Yan Takara Ta Karshe – INEC
  • Laifukan Zabe Barazana Ne Ga Samun Sahihan Zabuka A Nijeriya – INEC

Gumus ta ce, “A bisa dokar zabe ta 2022, tilas ne INEC ta gabatar da rajistar masu zabe ga shugabannin jam’iyyun siyasa nan da kwanaki 30 kafin zaben. Muna kokarin bin doka da oda tare da aiwatar da ayyuka 10 cikin 13 da aka shirya gudanarwa a zaben gwamnan Edo.”

ADVERTISEMENT

Yayin da take jaddada bukatar a gudanar da zaben cikin lumana, Gumus ta ce, “Bai kamata zabe ya zama ko a mutu ko a yi rai ba. Idan ba ku ci nasara ba a yau, kuna iya yin nasara a gobe. Matsaloli kullum suna tashi a ranar zabe. ‘Yan siyasa da magoya bayansu a Jihar Edo su guji tashin hankali.

“INEC ta shirya tsaf domin gudanar da zaben gwamna a Jihar Edo. Muna son masu ruwa da tsaki su bai wa hukumar zabe hadin kai domin ganin ayyukan kafin zabe da lokacin zabe da kuma bayan zabe sun gudana yadda ake bukata. Ina ba da tabbacin cewa tare da goyon bayan jami’an tsaro za a gudanar da zaben cikin kwanciyar hankali da walwala.”

LABARAI MASU NASABA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

Kwamishiniyar ta kasa mai sa ido kuma bukaci mazauna Edo da sauran ‘yan Nijeriya da su yi alfahari da kasarsu, kuma ka da su bari kabila ko harshe ya raba su.

Tun da farko kwamishinan zabe a Jihar Edo, Dakta Anugbum Onuoha, ya sake nanata cewa mutane 2,501,081 ne aka yi wa rajista a jihar domin zaben 2023, yayin da mutane 173,048 suka yi rajista a ci gaba da rajistar masu kada kuri’a daga ranar 27 ga watan Mayu zuwa 9 ga watan Yuni, 2024. Masu rajista 119,206, ciki har da wadanda suka sauya katin zabensu suka cancanta, wanda hakan ya kawo adadin masu kada kuri’a 2,501,081.

Onuoha ya ce za a dakatar da yakin neman zabe a ranar 19 ga watan Satumba, yayin da zaben gwamnan Edo zai gudana a ranar 21 ga watan Satumba.

Shugaban majalisar hadakan jam’iyyu a Edo, Greg Igbinomwanhia, wanda kuma shi ne shugaban jam’iyyar ‘Redemption’ na jihar, ya yaba wa INEC kan yadda ta ke kokarin gudanar da ayyukan zaben ba tare da tangarda ba.

Igbinomwanhia ya kara da cewa zaben gwamnan Jihar Edo da za a yi a ranar 21 ga watan Satumba ba dole ne ya kasance an yi shi cikin ‘yanci da adalci da kuma zaman lafiya.

Ya bukaci shugabanni da magoya bayan jam’iyyun siyasa da su guji tashin hankali domin a zabi magajin Gwamna Godwin Obaseki ba tare da nuna adawa ba.

Edo
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Rashin Tsaro Na Barazana Ga Zaben 2027 —Rahotanni
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Yadda Matsin Lamba Ta Sa Amaechi Ya Amince Ya Zama Abokin Takarar Atiku
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    2027: Kallo Ya Koma Kan Yadda APC, ADC Da PDP Ke Neman Abokan Takarar Mataimakin Shugaban Kasa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ko INEC Na Da Hannu A Rikice-rikicen Jam’iyyun Siyasa A Nijeriya?

MASU ALAKA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi
Manyan Labarai

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53
Manyan Labarai

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya
Labarai

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Next Post
An Cafke Mutumin Da Ake Zargi Da Garkuwa Da Almajirai 2 A Bauchi

An Cafke Mutumin Da Ake Zargi Da Garkuwa Da Almajirai 2 A Bauchi

LABARAI MASU NASABA

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

Ndume Ya Bayyana Dalilin Da Ya Sa Yake Goyon Bayan Ƙudirin Kafa ‘Yansandan Jihohi

June 25, 2026
EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

EFCC Za Ta Gurfanar Da Shugaban Miyetti Allah Kan Zargin Almundahanar Dala Miliyan 2.53

June 25, 2026
Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

Maroko Ta Zama Ƙasa Ta Farko Daga Afirka Da Ta Tsallaka Zuwa Zagaye Na 32 A Gasar Kofin Duniya

June 25, 2026
Zan Ware 10bn Don Inganta Ilimin Matasa Idan Na Ci Zabe – Atiku

‘Yan Nijeriya Ba Sa Bukatar ‘Yan Jarida Su Faɗa Musu Suna Jin Yunwa — Atiku

June 25, 2026
Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

Dokar Sin Ta Gurfanar Da Masu Rajin Ballewar Kabilun Kasar Da Ke Kasashen Waje Ta Dace

June 24, 2026
’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

’Yan Kasuwa Na Kasashen Waje Sun Yaba Wa Yanayin Kasuwanci Na Sin

June 24, 2026
Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

Yadda Uba Sani Ya Farfaɗo Da Asibitin Da Aka Yi Watsi Da Shi Tsawon Shekaru 40 – Hakimin Makarfi

June 24, 2026
Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

Dandalin DAVOS Na Bana: Fage Ne Da “Kirkire-Kirkiren Sin” Ya Sadu Da “Kyakkyawan Fatan Afirka”

June 24, 2026
Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

Binciken CGTN: Amfanarwa A Aikace Shi Ne Nagartaccen Ma’aunin Tantance Ainihin Kimar Sabbin Fasahohi

June 24, 2026
Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

Kasar Sin Na Kara Zama Babban Ginshikin Ci Gaban Tattalin Arzikin Duniya Na Gaba

June 24, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.