• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutumin Da Ya Yi Yunkurin Sayar Da Dansa Kan Naira Miliyan 20 Ya Shiga Hannu

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Kotu Da Ɗansanda
0
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

Jami’an tsaron ta Cibil Defence da ke Babban Birnin Tarayya Abuja, sun cafke wani mutum da ke shirin sayar da dansa mai shekaru takwas a kan kudi Naira miliyan 20.

Da yake gabatar da wadanda ake zargi a rundunar, Kwamandan Babban Birnin Tarayya, Olusola Odumosu, ya ce an kama mahaifin dan, Chinana Tali, tare da Pius Aondoakaa a ranar 10 ga Janairu, 2024 saboda hada-hadar sayar da Ushafa Tali.

  • ‘Yan Bindiga Sanye Da Hijabi Sun Farmaki Ofishin ‘Yansanda A Katsina
  • Gazawar Gwamnati Ta Tsananta Fatara Da Rashin Tsaro A Nijeriya –Atiku

Da yake bayyana yadda aka kama wadanda ake zargin, Odumosu ya ce, “Jami’an hukumar a FCT da hazikan jami’an leken asiri a cikin shirin da suka yi a watan Janairun 2024, sun kama wani uba da suka hada baki da wani yaro kan sayar da dan shekara takwas wanda ya ce dansa ne. akan kudi Naira miliyan 20 a FCT, inda suke ambaton yaro a matsayin “dan akuya”.

“Bayan bayanan da aka samu, nan take aka sanya wa wadanda ake zargin ido. Daya daga cikin wadanda ake zargin, Pius Aondoakaa, a kokarin neman karin kudi, bayan ya ki amincewa da Naira miliyan 12, inda ya nemi sama da Naira miliyan 20 .

“Ya kuma bayar da “Akuya” (wato yarinya) akan Naira miliyan15. Pius ya yi ikirarin cewa yana da da na sayarwa kuma mahaifin yaron yana so ya yi amfani da kudin da aka sayar don kula da sauran ’ya’yansa.”

Da yake bayar da karin bayani, kwamandan ya kara da cewa, “A bisa ga haka ne jami’an leken asiri na Babban Birnin Tarayya Abuja suka kama asalin mahaifin yaron Mista China Telpesa Solomon Tali zuwa Abuja a Janairun 2024. akan sharudan saye da biyan kudi Naira miliyan 20.

“Ma’aikatan sirri ne suka tarbe shi a wani lambu tare da dan nasa. An kamalla cinikin ne akan kudi Naira miliyan 20 daga nan ne jami’an tsaro suka shiga suka kama mahaifin mai suna Mista Chinana Tali mai shekaru 42 a karamar hukumar Logo ta jihar Benue inda suka kwato karamin yaron mai suna Ushafa dan shekara takwas. Tali.

“Wanda ake zargin, Pius Aondoakaa, namiji, dan shekara 29, daga Karamar Hukumar Logo ta Jihar Binuwe, wanda suka hada baki da mahaifin yaron, an kuma kama shi a ranar 12 ga watan Junairu, 2024. Dukan wadanda ake zargin ‘yan kabilar Tib ne kuma daga wani kauye mai suna R.C.M. Abeda Mbadyul a Karamar Hukumar Logo.”

Odumosu ya mika wadanda ake zargin ga hukumar yaki da fataucin mutane ta kasa domin ci gaba da bincike, tare da gurfanar da shi gaban kuliya yayin da za a sada yaron da mahaifiyarsa.

Da yake magana da manema labarai, mahaifin yaron ya yi ikirarin cewa matsalar rayuwa ce ta sa ya yanke shawarar sayar da dansa na hudu a kan Naira miliyan 20 don ba shi ikon daukar nauyin sauran ‘ya’yan nasa.

Ya ce, “Matsalar wahala ce ta sa na amince in sayar da dana a kan wannan kudi domin samun sukunin kula da sauran biyar din.”

Wakiliyar Hukumar ta NAPTIP, Oseafiana Chineyere, yayin da yake karbar wadanda ake zargin, ta ce, “NAPTIP za ta binciki wannan lamarin kuma sakamakon zai kasance mai kyau.”

A wani labarin kuma, Hukumar NSCDC Babban Birnin Tarayya ta kama wani matashi dan shekara 23 mai suna Yakubu Mati a watan Junairu, 2024 bisa laifin lalata igiya mai sulke a kan layin dogo na Idu.

An kama shi da faratanya, zarto, da kuma cocilan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Ya Sace Katan 20 Na Alkur’ani Da Hadisai A Kwara

Next Post

An Cafke Wani Mutum Bisa Zargin Lalata Da ‘Yar Shekara 15

Related

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya
Kotu Da Ɗansanda

Zargin Shan Guba: ’Yan Nijeriya Biyu Sun Mutu A Libya

4 weeks ago
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta
Kotu Da Ɗansanda

Yadda Wani Mai Unguwa Ya Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyade A Gombe

4 weeks ago
Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji
Kotu Da Ɗansanda

Garkuwa Da Mutane: Wani Ba’indiye Da Ake Zargi Ya Nemi Shafa Wa ‘Yan Nijeriya Kashin Kaji

4 weeks ago
An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade
Kotu Da Ɗansanda

An Sake Daure Dan Nijeriya Shekara Biyar A Birtaniya Kan Laifin Fyade

1 month ago
Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara
Kotu Da Ɗansanda

Rashin Tsaro: Garuruwa Sama Da 30 Sun Gudanar Da Zanga-zanga A Zamfara

1 month ago
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Fashi Tare Da Kwato Makamai A Delta

1 month ago
Next Post
‘Yansanda Sun Cafke Dan Damfara Da Katin Cirar Kudi 10 A Adamawa 

An Cafke Wani Mutum Bisa Zargin Lalata Da ‘Yar Shekara 15

LABARAI MASU NASABA

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

Yanzu-yanzu: Shugaba Tinubu Ya Ɗage Dokar Ta-ɓaci A Jihar Ribas

September 17, 2025
Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

Guterres: Jerin Shawarwarin Da Sin Ta Gabatar Sun Cika Ka’idar Kundin Tsarin Majalisar Dinkin Duniya

September 17, 2025
NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

NECO Ta Saki Sakamakon Jarrabawar 2025

September 17, 2025
Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

Lakurawa Sun Hallaka Jami’in Kwastam A Jihar Kebbi

September 17, 2025
Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

Sojoji Sun Kashe Mayaƙan ISWAP 11 A Borno Da Adamawa

September 17, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri Da Ɓarayin Kifi A Jihar Neja

September 17, 2025
Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

Mataimakin Shugaban Jam’iyyar APC Na Nasarawa, Aliyu Barde, Ya Rasu

September 17, 2025
Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

Sowore Ya Maka DSS, Meta da X A Kotu Kan Take Masa Haƙƙi

September 17, 2025
Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

Saudiyya Ta Saki ‘Yan Nijeriya 3 Da Aka Yi Wa Sharrin Safarar Ƙwayoyi

September 17, 2025
Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.