• English
  • Business News
Wednesday, October 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutumin Da Ya Yi Yunkurin Sayar Da Dansa Kan Naira Miliyan 20 Ya Shiga Hannu

byRabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Naira

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

Jami’an tsaron ta Cibil Defence da ke Babban Birnin Tarayya Abuja, sun cafke wani mutum da ke shirin sayar da dansa mai shekaru takwas a kan kudi Naira miliyan 20.

Da yake gabatar da wadanda ake zargi a rundunar, Kwamandan Babban Birnin Tarayya, Olusola Odumosu, ya ce an kama mahaifin dan, Chinana Tali, tare da Pius Aondoakaa a ranar 10 ga Janairu, 2024 saboda hada-hadar sayar da Ushafa Tali.

  • ‘Yan Bindiga Sanye Da Hijabi Sun Farmaki Ofishin ‘Yansanda A Katsina
  • Gazawar Gwamnati Ta Tsananta Fatara Da Rashin Tsaro A Nijeriya –Atiku

Da yake bayyana yadda aka kama wadanda ake zargin, Odumosu ya ce, “Jami’an hukumar a FCT da hazikan jami’an leken asiri a cikin shirin da suka yi a watan Janairun 2024, sun kama wani uba da suka hada baki da wani yaro kan sayar da dan shekara takwas wanda ya ce dansa ne. akan kudi Naira miliyan 20 a FCT, inda suke ambaton yaro a matsayin “dan akuya”.

“Bayan bayanan da aka samu, nan take aka sanya wa wadanda ake zargin ido. Daya daga cikin wadanda ake zargin, Pius Aondoakaa, a kokarin neman karin kudi, bayan ya ki amincewa da Naira miliyan 12, inda ya nemi sama da Naira miliyan 20 .

“Ya kuma bayar da “Akuya” (wato yarinya) akan Naira miliyan15. Pius ya yi ikirarin cewa yana da da na sayarwa kuma mahaifin yaron yana so ya yi amfani da kudin da aka sayar don kula da sauran ’ya’yansa.”

Da yake bayar da karin bayani, kwamandan ya kara da cewa, “A bisa ga haka ne jami’an leken asiri na Babban Birnin Tarayya Abuja suka kama asalin mahaifin yaron Mista China Telpesa Solomon Tali zuwa Abuja a Janairun 2024. akan sharudan saye da biyan kudi Naira miliyan 20.

“Ma’aikatan sirri ne suka tarbe shi a wani lambu tare da dan nasa. An kamalla cinikin ne akan kudi Naira miliyan 20 daga nan ne jami’an tsaro suka shiga suka kama mahaifin mai suna Mista Chinana Tali mai shekaru 42 a karamar hukumar Logo ta jihar Benue inda suka kwato karamin yaron mai suna Ushafa dan shekara takwas. Tali.

“Wanda ake zargin, Pius Aondoakaa, namiji, dan shekara 29, daga Karamar Hukumar Logo ta Jihar Binuwe, wanda suka hada baki da mahaifin yaron, an kuma kama shi a ranar 12 ga watan Junairu, 2024. Dukan wadanda ake zargin ‘yan kabilar Tib ne kuma daga wani kauye mai suna R.C.M. Abeda Mbadyul a Karamar Hukumar Logo.”

Odumosu ya mika wadanda ake zargin ga hukumar yaki da fataucin mutane ta kasa domin ci gaba da bincike, tare da gurfanar da shi gaban kuliya yayin da za a sada yaron da mahaifiyarsa.

Da yake magana da manema labarai, mahaifin yaron ya yi ikirarin cewa matsalar rayuwa ce ta sa ya yanke shawarar sayar da dansa na hudu a kan Naira miliyan 20 don ba shi ikon daukar nauyin sauran ‘ya’yan nasa.

Ya ce, “Matsalar wahala ce ta sa na amince in sayar da dana a kan wannan kudi domin samun sukunin kula da sauran biyar din.”

Wakiliyar Hukumar ta NAPTIP, Oseafiana Chineyere, yayin da yake karbar wadanda ake zargin, ta ce, “NAPTIP za ta binciki wannan lamarin kuma sakamakon zai kasance mai kyau.”

A wani labarin kuma, Hukumar NSCDC Babban Birnin Tarayya ta kama wani matashi dan shekara 23 mai suna Yakubu Mati a watan Junairu, 2024 bisa laifin lalata igiya mai sulke a kan layin dogo na Idu.

An kama shi da faratanya, zarto, da kuma cocilan.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi
Kotu Da Ɗansanda

Jami’an Tsaro Sun Kwato Wayoyi 45 Daga Hannun Wata Kungiyar Barayi

October 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Hudu Da Ake Zargi Da Aikata Muggan Laifuka A Yobe

October 4, 2025
Yaki Da Miyagun Kwayoyi: Kamfanin LEADERSHIP Da NDLEA Sun Kulla Kawance
Kotu Da Ɗansanda

NDLEA Ta Farmaki Masu Safarar Muggan Kwayoyi A Sassan Nijeriya

September 27, 2025
Next Post
‘Yansanda Sun Cafke Dan Damfara Da Katin Cirar Kudi 10 A Adamawa 

An Cafke Wani Mutum Bisa Zargin Lalata Da ‘Yar Shekara 15

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025
ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

ABU Na Kashe Sama Da Naira Biliyan 4 Duk Shekara A Wutar Lantarki

October 8, 2025
Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

Gwamnati Ta Roƙi ASUU Ta Soke Shiga Tsunduma Yajin Aiki, Ta Yi Alƙawarin Biyan Buƙatunsu

October 8, 2025
Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

Boko Haram Ta Taɓa Ayyana Buhari A Matsayin Wanda Zai Yi Mata Sulhu Da Gwamnati – Dalung

October 8, 2025
A Kama Wani Likitan Bogi A Neja

‘Yansanda Sun Kama Masu Laifi 153, Sun Ƙwato Miyagun Ƙwayoyi A Jihar Jigawa

October 8, 2025
An Fara Biyan Ma’aikata Sabon Mafi Ƙarancin Albashin N70,000 A Borno

‘Yansanda Da Mutanen Gari Sun Daƙile Harin Boko Haram A Borno

October 8, 2025
…ACF Ta Nesanta Kanta Da Goyon Bayan Akpabio

‘Yan Nijeriya Sama Da Miliyan 33 Ne Ke Fama Da Matsananciyar Yunwa – Akpabio

October 8, 2025
Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Kasashen Duniya Su Hada Hannu Wajen Raya Harkokin Mata

October 7, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version