ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutumin Da Ya Yi Yunkurin Sayar Da Dansa Kan Naira Miliyan 20 Ya Shiga Hannu

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
Naira

LABARAI MASU NASABA

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

Jami’an tsaron ta Cibil Defence da ke Babban Birnin Tarayya Abuja, sun cafke wani mutum da ke shirin sayar da dansa mai shekaru takwas a kan kudi Naira miliyan 20.

Da yake gabatar da wadanda ake zargi a rundunar, Kwamandan Babban Birnin Tarayya, Olusola Odumosu, ya ce an kama mahaifin dan, Chinana Tali, tare da Pius Aondoakaa a ranar 10 ga Janairu, 2024 saboda hada-hadar sayar da Ushafa Tali.

  • ‘Yan Bindiga Sanye Da Hijabi Sun Farmaki Ofishin ‘Yansanda A Katsina
  • Gazawar Gwamnati Ta Tsananta Fatara Da Rashin Tsaro A Nijeriya –Atiku

Da yake bayyana yadda aka kama wadanda ake zargin, Odumosu ya ce, “Jami’an hukumar a FCT da hazikan jami’an leken asiri a cikin shirin da suka yi a watan Janairun 2024, sun kama wani uba da suka hada baki da wani yaro kan sayar da dan shekara takwas wanda ya ce dansa ne. akan kudi Naira miliyan 20 a FCT, inda suke ambaton yaro a matsayin “dan akuya”.

“Bayan bayanan da aka samu, nan take aka sanya wa wadanda ake zargin ido. Daya daga cikin wadanda ake zargin, Pius Aondoakaa, a kokarin neman karin kudi, bayan ya ki amincewa da Naira miliyan 12, inda ya nemi sama da Naira miliyan 20 .

“Ya kuma bayar da “Akuya” (wato yarinya) akan Naira miliyan15. Pius ya yi ikirarin cewa yana da da na sayarwa kuma mahaifin yaron yana so ya yi amfani da kudin da aka sayar don kula da sauran ’ya’yansa.”

Da yake bayar da karin bayani, kwamandan ya kara da cewa, “A bisa ga haka ne jami’an leken asiri na Babban Birnin Tarayya Abuja suka kama asalin mahaifin yaron Mista China Telpesa Solomon Tali zuwa Abuja a Janairun 2024. akan sharudan saye da biyan kudi Naira miliyan 20.

“Ma’aikatan sirri ne suka tarbe shi a wani lambu tare da dan nasa. An kamalla cinikin ne akan kudi Naira miliyan 20 daga nan ne jami’an tsaro suka shiga suka kama mahaifin mai suna Mista Chinana Tali mai shekaru 42 a karamar hukumar Logo ta jihar Benue inda suka kwato karamin yaron mai suna Ushafa dan shekara takwas. Tali.

“Wanda ake zargin, Pius Aondoakaa, namiji, dan shekara 29, daga Karamar Hukumar Logo ta Jihar Binuwe, wanda suka hada baki da mahaifin yaron, an kuma kama shi a ranar 12 ga watan Junairu, 2024. Dukan wadanda ake zargin ‘yan kabilar Tib ne kuma daga wani kauye mai suna R.C.M. Abeda Mbadyul a Karamar Hukumar Logo.”

Odumosu ya mika wadanda ake zargin ga hukumar yaki da fataucin mutane ta kasa domin ci gaba da bincike, tare da gurfanar da shi gaban kuliya yayin da za a sada yaron da mahaifiyarsa.

Da yake magana da manema labarai, mahaifin yaron ya yi ikirarin cewa matsalar rayuwa ce ta sa ya yanke shawarar sayar da dansa na hudu a kan Naira miliyan 20 don ba shi ikon daukar nauyin sauran ‘ya’yan nasa.

Ya ce, “Matsalar wahala ce ta sa na amince in sayar da dana a kan wannan kudi domin samun sukunin kula da sauran biyar din.”

Wakiliyar Hukumar ta NAPTIP, Oseafiana Chineyere, yayin da yake karbar wadanda ake zargin, ta ce, “NAPTIP za ta binciki wannan lamarin kuma sakamakon zai kasance mai kyau.”

A wani labarin kuma, Hukumar NSCDC Babban Birnin Tarayya ta kama wani matashi dan shekara 23 mai suna Yakubu Mati a watan Junairu, 2024 bisa laifin lalata igiya mai sulke a kan layin dogo na Idu.

An kama shi da faratanya, zarto, da kuma cocilan.

Naira
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Gwamnatin Tarayya Ta Bayyana Dalilanta Na Sake Fasalin Hukumar NYSC
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Sarkin Zazzau Ya Umarci A Soke Wasu Al’adu Da Ke Kawo Wa Aure Cikas
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Kotu Da Ɗansanda

Gwanjon Kadarori: Kotun Daukaka Kara Ta Kori Karar Da Sani Sha’aban Ya Shigar

June 18, 2026
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa
Kotu Da Ɗansanda

’Yansanda Sun Ceto Yaro Mai Shekara Shida Da Aka Sace, Sun Cafke Wanda Ake Zargi A Borno

June 13, 2026
Next Post
‘Yansanda Sun Cafke Dan Damfara Da Katin Cirar Kudi 10 A Adamawa 

An Cafke Wani Mutum Bisa Zargin Lalata Da ‘Yar Shekara 15

LABARAI MASU NASABA

’Yan Bindiga Sun Kashe Farfesa Har Lahira A  Jihar Benuwai

’Yan Bindiga Sun Kashe Farfesa Har Lahira A Jihar Benuwai

July 9, 2026
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga, Sun Ceto Mutane A Kaduna Da Filato

Sojoji Sun Hallaka Shugaban ’Yan Bindiga, Sun Daƙile Hare-hare A Zamfara

July 9, 2026
Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

Sin Ta Yi Kira Ga Amurka Da Iran Da Su Aiwatar Da Cikakkiyar Takardar Bayanin Fahimtar Juna Da Aka Cimma

July 8, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

Sin Ta Yi Kira Da A Cike Gibin Cin Gajiyar Fasahar AI

July 8, 2026
Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Malamin ABU Kan Zargin Gwamnatin Katsina Da Ɗaukar Nauyin Aikin Hajjin ‘Yan Bindiga

July 8, 2026
Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

Ministan Lafiya Na DRC Ya Gode Wa Sin Bisa Tura Kwararrun Likitoci Kasar Don Tallafa Wa Dakile Ebola

July 8, 2026
Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

Sin Ta Yi Watsi Da Ikirarin Philippine Kan Tekun Kudancinta

July 8, 2026
Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

Sin Da Tanzania Da Zambia Sun Karrama Jaruman Sinawa A Bikin Cika Shekaru 50 Da Kafa Layin Dogo Na TAZARA

July 8, 2026
Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

Zaɓen 2027: NNPP Ta Fara Shigar Da Sunayen ’Yan Takara, Ta Nemi INEC Ta Ƙara Mata Lokaci

July 8, 2026
Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

Damar Fita Daga Kangin Dalar Amurka Ta Sake Samuwa Ga Kasashen Afirka

July 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.