ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Mutumin Da Ya Yi Yunkurin Sayar Da Dansa Kan Naira Miliyan 20 Ya Shiga Hannu

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
Naira

LABARAI MASU NASABA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

Jami’an tsaron ta Cibil Defence da ke Babban Birnin Tarayya Abuja, sun cafke wani mutum da ke shirin sayar da dansa mai shekaru takwas a kan kudi Naira miliyan 20.

Da yake gabatar da wadanda ake zargi a rundunar, Kwamandan Babban Birnin Tarayya, Olusola Odumosu, ya ce an kama mahaifin dan, Chinana Tali, tare da Pius Aondoakaa a ranar 10 ga Janairu, 2024 saboda hada-hadar sayar da Ushafa Tali.

  • ‘Yan Bindiga Sanye Da Hijabi Sun Farmaki Ofishin ‘Yansanda A Katsina
  • Gazawar Gwamnati Ta Tsananta Fatara Da Rashin Tsaro A Nijeriya –Atiku

Da yake bayyana yadda aka kama wadanda ake zargin, Odumosu ya ce, “Jami’an hukumar a FCT da hazikan jami’an leken asiri a cikin shirin da suka yi a watan Janairun 2024, sun kama wani uba da suka hada baki da wani yaro kan sayar da dan shekara takwas wanda ya ce dansa ne. akan kudi Naira miliyan 20 a FCT, inda suke ambaton yaro a matsayin “dan akuya”.

“Bayan bayanan da aka samu, nan take aka sanya wa wadanda ake zargin ido. Daya daga cikin wadanda ake zargin, Pius Aondoakaa, a kokarin neman karin kudi, bayan ya ki amincewa da Naira miliyan 12, inda ya nemi sama da Naira miliyan 20 .

“Ya kuma bayar da “Akuya” (wato yarinya) akan Naira miliyan15. Pius ya yi ikirarin cewa yana da da na sayarwa kuma mahaifin yaron yana so ya yi amfani da kudin da aka sayar don kula da sauran ’ya’yansa.”

Da yake bayar da karin bayani, kwamandan ya kara da cewa, “A bisa ga haka ne jami’an leken asiri na Babban Birnin Tarayya Abuja suka kama asalin mahaifin yaron Mista China Telpesa Solomon Tali zuwa Abuja a Janairun 2024. akan sharudan saye da biyan kudi Naira miliyan 20.

“Ma’aikatan sirri ne suka tarbe shi a wani lambu tare da dan nasa. An kamalla cinikin ne akan kudi Naira miliyan 20 daga nan ne jami’an tsaro suka shiga suka kama mahaifin mai suna Mista Chinana Tali mai shekaru 42 a karamar hukumar Logo ta jihar Benue inda suka kwato karamin yaron mai suna Ushafa dan shekara takwas. Tali.

“Wanda ake zargin, Pius Aondoakaa, namiji, dan shekara 29, daga Karamar Hukumar Logo ta Jihar Binuwe, wanda suka hada baki da mahaifin yaron, an kuma kama shi a ranar 12 ga watan Junairu, 2024. Dukan wadanda ake zargin ‘yan kabilar Tib ne kuma daga wani kauye mai suna R.C.M. Abeda Mbadyul a Karamar Hukumar Logo.”

Odumosu ya mika wadanda ake zargin ga hukumar yaki da fataucin mutane ta kasa domin ci gaba da bincike, tare da gurfanar da shi gaban kuliya yayin da za a sada yaron da mahaifiyarsa.

Da yake magana da manema labarai, mahaifin yaron ya yi ikirarin cewa matsalar rayuwa ce ta sa ya yanke shawarar sayar da dansa na hudu a kan Naira miliyan 20 don ba shi ikon daukar nauyin sauran ‘ya’yan nasa.

Ya ce, “Matsalar wahala ce ta sa na amince in sayar da dana a kan wannan kudi domin samun sukunin kula da sauran biyar din.”

Wakiliyar Hukumar ta NAPTIP, Oseafiana Chineyere, yayin da yake karbar wadanda ake zargin, ta ce, “NAPTIP za ta binciki wannan lamarin kuma sakamakon zai kasance mai kyau.”

A wani labarin kuma, Hukumar NSCDC Babban Birnin Tarayya ta kama wani matashi dan shekara 23 mai suna Yakubu Mati a watan Junairu, 2024 bisa laifin lalata igiya mai sulke a kan layin dogo na Idu.

An kama shi da faratanya, zarto, da kuma cocilan.

Naira
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ƙungiya Ta Gudanar Da Zaɓen Sabbin Shugabanninta A Abuja
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Jihar Katsina Da UNICEF Sun Ceto Rayuwar Yara Ta Hanyar Samar Da Abinci Mai Gina Jiki
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Yadda Tinubu Ya Kashe Naira Biliyan 37.64 A Tafiye-tafiye
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Ta’addaci: Mutum 14,500 Sun Bace A Arewa Maso Gabas
ADVERTISEMENT

MASU ALAKA

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota
Kotu Da Ɗansanda

Direbobi 123 A Kano Suna Fuskantar Tuhuma Kan Laifin Keta Dokokin Amfani Da Lambar Mota

July 18, 2026
An Kama Matashi A Kano Kan Zargin Kashe Abokinsa
Kotu Da Ɗansanda

‘Yansanda Sun Kama Mutum Biyu Kan Zargin Damfarar Wayar Salula A Jihar Adamawa

July 18, 2026
Disu
Kotu Da Ɗansanda

IGP Disu Ya Hana Jami’an Ƴansanda Yin Amfani Da TikTok Da Instagram Da Sauransu

June 26, 2026
Next Post
‘Yansanda Sun Cafke Dan Damfara Da Katin Cirar Kudi 10 A Adamawa 

An Cafke Wani Mutum Bisa Zargin Lalata Da ‘Yar Shekara 15

LABARAI MASU NASABA

Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.