ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NIS Ta Bi Ƙa’ida Sau Da Ƙafa Wajen Bai Wa David Nwamina Fasfo – CGI Isah Jere

by yahuzajere
4 years ago
David Nwamina

Hukumar Kula da Shige da Fice ta Nijeriya (NIS), ta tabbatar da cewa ta bi ƙa’ida sau da ƙafa wajen bayar da Fasfon Nijeriya ga ɗan samarin nan, Mista David Ukpo Nwamina da ake ƙiƙi-ƙaƙa a kansa game da batun cire wata gava a jikinsa domin dasa wa wata yarinya mara lafiya, ‘yar gidan tsohon mataimakin shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Ike Ekweremadu.

Wata sanarwar manema labarai da Shugaban NIS, CGI Isah Idris Jere ya fitar tare da rattaba hannu da kansa, ta yi bayanin cewa yamaɗiɗin da wasu ke yaɗawa, “cewa hukumar ba ta tantance takardun wanda aka bai wa fasfon yadda ya kamata ba, ba gaskiya ba ne illa ƙazafi da wasu suka kitsa don kawai su shafa wa hukumar kashin kaji a vata mata suna.

  • Yajin Aikin ASUU: Dalibai Sun Yi Barazanar Rufe Tituna, Tashoshin Jirgin Sama Da Na Kasa
  • Da Aka Gama Rarraba Wa Deliget Kudi, Sai Kuma Me? (Ra’ayinmu)

“Don haka gaskiyar abin da ya faru game da lamarin shi ne, shi wanda ake magana a kansa, Mista David Ukpo Nwamina ya gabatar da buƙatarsa ta sabon fasfo da aka inganta kuma ya biya kuɗin fasfon ta manhajar intanet wanda bayan haka ne ya tafi Ofishin Fasfo na Abuja da ke Gwagwalada a ranar 2 ga Nuwambar 2021 domin amsa tambayoyi. Domin ƙarfafa samun fasfon nasa, Mista David Nwamina ya gabatar da dukkan takardun ƙa’ida da suka wajaba, da suka haɗa da takardar haihuwarsa wadda Hukumar ƙidaya ta ƙasa (NPC) ta ba shi, da ta nuna an haife shi a ranar 12 ga Oktobar 2000, sannan bayanan shaidar haihuwarsa ta lambar ɗan ƙasa wadda Hukumar NIMC ta ba shi, sun yi daidai da na takardar haihuwarsa sai kuma takardar shaidar asalinsa wadda Ofishin Gwamnatin Jihar Ebonyi na Abuja ya ba shi da kuma takardar shaidar mutumin da ya tsaya masa da aka rattaba wa hannu kamar yadda ya kamata.”

ADVERTISEMENT

Saboda haka bisa waɗannan hujjoji, NIS tace tana sanar da jama’a cewa ba ta wallafa ranar haihuwa ko wasu bayanai a duk wani fasfon Nijeriya har sai an tantance su yadda ya kamata tare da tantance shi kansa mai neman fasfo. “Don haka batun Mista Nwamina ba zai zama daban ko na ɗanmowa ba.”

Har ila yau, Hukumar ta NIS ta tabbatar wa da al’umma irin duƙufar da ta yi wajen kare mutuncin fasfon Nijeriya, kana ta yi amfani da wannan damar wajen yin kira ga jama’a su guji furta irin waɗannan ƙarairayi domin za su iya zubar da kimar hukumar a idon duniya.

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

  • https://portal.immigration.gov.ng/

Mista David Ukpo Nwamina dai na can Ingila ana ci gaba da bincike a kansa da wanda abin ya shafa Sanata Ike Ekweremadu.

David Nwamina
yahuzajere
+ postsBio
  • yahuzajere
    Da Kujerar Mulki Gara Zaman Lafiyar Kano
  • yahuzajere
    Ya Kamata Amurka Ta San Ana Barin Halal Don Kunya
  • yahuzajere
    Buɗaɗɗiyar Wasiƙa Ga Gwamnatin Tarayya A Kan Tozarta Marasa Lafiya Daga Jami’an FIRS A Kano
  • yahuzajere
    Sin Ta Kaddamar Da Gagarumin Bikin Ba Da Lambobin Yabo Na Kasar Sin

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Next Post
Na Dakatar Da Ayyukan Banga Har Gwamnati Ta Binciki Dalilin Kamani – Manta

Na Dakatar Da Ayyukan Banga Har Gwamnati Ta Binciki Dalilin Kamani - Manta

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.