• English
  • Business News
Saturday, September 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Gaba Ya Yi Gaba…

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Na Gaba Ya Yi Gaba…
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Da alamu dai hadin gwiwar dake tsakanin kasar Sin da kasashen Afirka, tana ci gaba da tsolewa wasu kasashe ido, wadanda a baya suke ta yunkurin kirkiro bayanai na karya da nufin bata wannan alaka mai dimbin tasiri da fa’ida ga bangarorin biyu. Amma bakin alkalami ya riga ya bushe.

Kasa ta baya-bayan nan da ta bijiro da maitarta a fili wajen ganin ta kulla alaka da kasashen Afirka, ita ce kasar Japan, inda ta shirya taron raya kasashen Afirka karo na 8 a kasar Tunusiya daga ranar 27 zuwa ta 28 ga watan Agustan shekarar 2022 da muke ciki.

  • Ya Wajaba Amurka Ta Kaucewa Sake Maimaita Irin Kuskuren Da Ta Aikata Game Da Taiwan

A yayin taron, firaministan Japan Fumio Kishida ya sanar ta kafar bidiyo cewa, a cikin shekaru 3 masu zuwa, kasarsa za ta zuba jarin dalar biliyan 30 a kasashen Afirka, sannan za ta horas da kwararrun nahiyar dubu 300 da dai sauransu. A cewarsa wai, “Wannan aiki ya sha bamban da na kasar Sin”. Amma, idan mutum ya ce zai ba ka riga, aka ce ka kalli ta wuyansa.

Idan har Japan da sauran kasashen yamma suna son su rudi kasashen Afirka da sunan tallafi ko horas da kwararru, don kulla wata alaka ta moriyar kansu, ya kamata su san cewa, kasashen Afirka sun dade suna kuma ci gaba da amfana da hadin gwiwarsu da kasar Sin. Wannan dai wani salo ne na wayon a ci, wai an kori kare daga gindin Dinya. Amma kan Mage ya waye.

Ai ko bayan Japan da wasu kasashe, ita ma kasar Amurka ta shelanta irin wannan alkawari mai kama da romon baka, yayin taron G7 da ya gudana a kasar Jamus a wani lokaci cikin wannan shekara, inda ta yi ikirarin kafa wata gidauniya da sunan tallafawa kasashe masu tasowa, duk da neman bata sunan shawarar “ziri daya da hanya daya” da kasar Sin ta gabatar.

Labarai Masu Nasaba

Ko Me Ya Sa Jihar Xinjiang Ta Kasar Sin Ke Kara Janyo Hankalin Al’ummun Duniya?

Wang Yi Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Morocco

Koma dai mene ne, abin tambaya shi ne, me ya sa sai yanzu kasar Japan da sauran kasashen yamma ke neman kulla alaka da kasashen Afirka, bayan da Sin da Afirka suke kara cin gajiyar alakarsu mai cike da aminci da mutuntawa da kare moriyar juna a dukkan sassa? Kifi dai yana ganin ka mai jar koma. A yi dai mu gani, idan har tusa tana hura wuta.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Yadda Bikin Cinikayyar Hidimomi Ke Jan Hankalin ‘Yan Kasuwa

Next Post

Dambu Ya Yi Ajalin Mutane 7 ‘Yan Gida Daya A Sakkwato 

Related

Ko Me Ya Sa Jihar Xinjiang Ta Kasar Sin Ke Kara Janyo Hankalin Al’ummun Duniya?
Daga Birnin Sin

Ko Me Ya Sa Jihar Xinjiang Ta Kasar Sin Ke Kara Janyo Hankalin Al’ummun Duniya?

58 minutes ago
Wang Yi Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Morocco
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Morocco

2 hours ago
Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Mika Lambobin Yabo A Fannin Raya Ilimin Yara Mata Da Mata Na Hukumar UNESCO 
Daga Birnin Sin

Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Mika Lambobin Yabo A Fannin Raya Ilimin Yara Mata Da Mata Na Hukumar UNESCO 

3 hours ago
Sin Da Amurka Na Iya Cimma Manyan Nasara Tare In Ji Shugaba Xi
Daga Birnin Sin

Sin Da Amurka Na Iya Cimma Manyan Nasara Tare In Ji Shugaba Xi

4 hours ago
Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu
Daga Birnin Sin

Kamfanin Kasar Sin Ya Bayar Da Gudunmuwar Kayayyaki Ga Wadanda Ambaliyar Ruwa Ta Shafa A Sudan Ta Kudu

22 hours ago
An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan
Daga Birnin Sin

An Kammala Taron Dandalin Tattauna Batun Tsaro Na Xiangshan

23 hours ago
Next Post
Dambu Ya Yi Ajalin Mutane 7 ‘Yan Gida Daya A Sakkwato 

Dambu Ya Yi Ajalin Mutane 7 'Yan Gida Daya A Sakkwato 

LABARAI MASU NASABA

Ko Me Ya Sa Jihar Xinjiang Ta Kasar Sin Ke Kara Janyo Hankalin Al’ummun Duniya?

Ko Me Ya Sa Jihar Xinjiang Ta Kasar Sin Ke Kara Janyo Hankalin Al’ummun Duniya?

September 20, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Morocco

Wang Yi Ya Gana Da Takwaransa Na Kasar Morocco

September 20, 2025
Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Mika Lambobin Yabo A Fannin Raya Ilimin Yara Mata Da Mata Na Hukumar UNESCO 

Peng Liyuan Ta Halarci Bikin Mika Lambobin Yabo A Fannin Raya Ilimin Yara Mata Da Mata Na Hukumar UNESCO 

September 20, 2025
Mun Kawo Ƙarshen Dogon Layin Mai Na Shekara 50 A Nijeriya – Matatar Dangote

Mun Kawo Ƙarshen Dogon Layin Mai Na Shekara 50 A Nijeriya – Matatar Dangote

September 20, 2025
Sin Da Amurka Na Iya Cimma Manyan Nasara Tare In Ji Shugaba Xi

Sin Da Amurka Na Iya Cimma Manyan Nasara Tare In Ji Shugaba Xi

September 20, 2025
Ta Yaya Zan Yi Tattalin Mijina?

Ta Yaya Zan Yi Tattalin Mijina?

September 20, 2025
Ajali: Wasu Ƴan Ƙauye Sun Gujewa Ƴan Bindiga Sun Nutse A Ruwa

Ajali: Wasu Ƴan Ƙauye Sun Gujewa Ƴan Bindiga Sun Nutse A Ruwa

September 20, 2025
Tinubu Ya Halarci Ɗaurin Auren Ɗan Yari, Ya Kai Ziyara Gidan Tsohon Shugaban Ƙasa Buhari

Tinubu Ya Halarci Ɗaurin Auren Ɗan Yari, Ya Kai Ziyara Gidan Tsohon Shugaban Ƙasa Buhari

September 20, 2025
Sabon Kakin Ƴansanda Ya Ziyarci Cibiyar Ƙungiyar Ƴan Jarida A FCT

Sabon Kakin Ƴansanda Ya Ziyarci Cibiyar Ƙungiyar Ƴan Jarida A FCT

September 20, 2025
Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 10.5 Sakamakon Rashin Cin Gajiyar Kashin Dabbobi

Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 10.5 Sakamakon Rashin Cin Gajiyar Kashin Dabbobi

September 20, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.