ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dambu Ya Yi Ajalin Mutane 7 ‘Yan Gida Daya A Sakkwato 

by Sadiq
4 years ago
Dambu

Wani Iftila’i ya afku a kauyen Kaura da ke Karamar Hukumar Yabo a Jihar Sakkwato, inda wasu ‘yan gida daya su bakwai suka mutu bayan sun ci abinci safe.

Magidancin da lamarin ya shafi iyalansa, Malam Danbala ya shaida wa manema labarai cewa ya rasa matansa biyu da ‘ya’yansa biyar a sanadiyyar wannan lamari.

  • Yadda Bikin Cinikayyar Hidimomi Ke Jan Hankalin ‘Yan Kasuwa
  • 2023: Atiku Da Tambuwal Sun Bukaci ‘Yan Nijeriya Ka Da Su Sake Zabar APC

Ya ce, “Ina Jihar Neja inda nake aiki a matsayin lebura, sai wani dan uwana ya kira ni a ranar Litinin cewa an samu matsala wadda ta bukaci kulawar gaggawa a gida.

ADVERTISEMENT

“Ya ce in dawo gida da wuri idan zan iya. Na tambaye shi me ya faru amma sai ya katse wayar ba tare da ya yi min wani karin bayani ba.

“Saboda haka na hau motar safe zuwa Sakkwato, da na isa gida, sai na tarar da duk iyalaina, ban da wata ’yata guda duk sun mutu. An yi jana’izarsu tun kafin isowata a ranar Talata kamar yadda addininmu ya bukata.”

LABARAI MASU NASABA

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

Danbala, ya ce matsalar ta samo asali ne lokacin da daya daga cikin matansa ta dafa Dambu ​​domin yin karin kumallo da shi.

“Dukkansu sun ci sun koshi kuma bayan wani lokaci sai suka fara korafin ciwon ciki kuma nan take aka garzaya da su asibiti.

“Yaran biyar ne suka fara rasuwa, sai matana da suka mutu da tsakar dare amma yarinyata tana karbar magani saboda ba ta cin abinci da yawa ba,” in ji shi.

A cewar wani shaidar gani da ido, matar ta dafa abincin ne a matsayin abincin dare a ranar Lahadi.

An ce ragowar abincin an ajiye shi ne domin yin karin kumallo da shi, kuma a safiyar ranar Litinin ta hada ragowar Dambun wadda ya kwana bubude. An ce ta dafa abincin sanan ta raba wa ‘yan gidan.

“Haka ne Allah ya kaddara makomarsu. Allah ya ba su Jannatul Firdaus,” in ji magidancin da iyalansa suka rasu.

MASU ALAKA

Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi
Manyan Labarai

2027: Atiku Na Amfani Da Tallafin Mai A Matsayin Dabarun Siyasa – Fayemi

September 8, 2026
Next Post
Tomas Bach Ya Taya CMG Murna

Tomas Bach Ya Taya CMG Murna

LABARAI MASU NASABA

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026
Gwamnan Kebbi Ya Bayyana Shirin Sake Duba Albashin Malaman Firamare

Gwamna Idris Ya Rushe Majalisar Shugabannin Hukumar Zaɓe Ta Kebbi

September 8, 2026
Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

Han Zheng Ya Halarci Baje Kolin CIFIT Karo Na 26 Tare Da Gabatar Da Jawabi

September 8, 2026
Wani Soja Ya Kashe Kansa Bayan Kashe Matarsa A Jihar Neja

Kano Za Ta Kafa Sansanonin Sojoji A Ƙananan Hukumomin Da Ke Fuskantar Barazanar Tsaro

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.