ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Dambu Ya Yi Ajalin Mutane 7 ‘Yan Gida Daya A Sakkwato 

by Sadiq
4 years ago
Dambu

Wani Iftila’i ya afku a kauyen Kaura da ke Karamar Hukumar Yabo a Jihar Sakkwato, inda wasu ‘yan gida daya su bakwai suka mutu bayan sun ci abinci safe.

Magidancin da lamarin ya shafi iyalansa, Malam Danbala ya shaida wa manema labarai cewa ya rasa matansa biyu da ‘ya’yansa biyar a sanadiyyar wannan lamari.

  • Yadda Bikin Cinikayyar Hidimomi Ke Jan Hankalin ‘Yan Kasuwa
  • 2023: Atiku Da Tambuwal Sun Bukaci ‘Yan Nijeriya Ka Da Su Sake Zabar APC

Ya ce, “Ina Jihar Neja inda nake aiki a matsayin lebura, sai wani dan uwana ya kira ni a ranar Litinin cewa an samu matsala wadda ta bukaci kulawar gaggawa a gida.

ADVERTISEMENT

“Ya ce in dawo gida da wuri idan zan iya. Na tambaye shi me ya faru amma sai ya katse wayar ba tare da ya yi min wani karin bayani ba.

“Saboda haka na hau motar safe zuwa Sakkwato, da na isa gida, sai na tarar da duk iyalaina, ban da wata ’yata guda duk sun mutu. An yi jana’izarsu tun kafin isowata a ranar Talata kamar yadda addininmu ya bukata.”

LABARAI MASU NASABA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Danbala, ya ce matsalar ta samo asali ne lokacin da daya daga cikin matansa ta dafa Dambu ​​domin yin karin kumallo da shi.

“Dukkansu sun ci sun koshi kuma bayan wani lokaci sai suka fara korafin ciwon ciki kuma nan take aka garzaya da su asibiti.

“Yaran biyar ne suka fara rasuwa, sai matana da suka mutu da tsakar dare amma yarinyata tana karbar magani saboda ba ta cin abinci da yawa ba,” in ji shi.

A cewar wani shaidar gani da ido, matar ta dafa abincin ne a matsayin abincin dare a ranar Lahadi.

An ce ragowar abincin an ajiye shi ne domin yin karin kumallo da shi, kuma a safiyar ranar Litinin ta hada ragowar Dambun wadda ya kwana bubude. An ce ta dafa abincin sanan ta raba wa ‘yan gidan.

“Haka ne Allah ya kaddara makomarsu. Allah ya ba su Jannatul Firdaus,” in ji magidancin da iyalansa suka rasu.

MASU ALAKA

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili
Manyan Labarai

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro
Manyan Labarai

Tambuwal Ya Jajanta Wa Waɗanda Harin ’Yan Bindiga Ya Shafa A Sokoto, Ya Nemi A Ƙara Tsaro

June 3, 2026
Next Post
Tomas Bach Ya Taya CMG Murna

Tomas Bach Ya Taya CMG Murna

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026
Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

Sarki Sanusi II Ya Tuɓe Rawanin Mai Unguwar Rikadawa Kan Badaƙalar Fili

June 4, 2026
Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

Tawagar Masanan Dakile Yaduwar Cututtuka Ta Sin Ta Isa DR Congo

June 3, 2026
Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

Uba Sani Ya Sanya Hannu Kan Sabbin Dokoki A Bangaren Sauya Fannin Wuta, Noma, Da Muhalli

June 3, 2026
Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

Han Zheng Zai Halarci Taron SPIEF Karo Na 29 A Rasha Tare Da Gudanar Da Ziyarar Aiki A Belarus

June 3, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.