• English
  • Business News
Tuesday, November 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Yi Mamakin Ganin Takardar Tuɓe Rawanina Na Sarautar Mujaddadin Bauchi – Sanata Buba

by Muhammad
1 year ago
Buba

Sanata Shehu Buba, wanda shi ne Shugaban Kwamitun Majalisar Dattijai kan tsaro da tattara bayanan sirri, ya ce ya ci karo da wani labari mai ban mamaki kan wata wasika mai ɗauke da kwanan watan 14 ga watan Augustan 2024.

Sanatan ya ce takardar mai ɗauke da sakon cewa Majalisar Masarautar Bauchi ta warware rawaninsa daga Sarautar Mujaddadin Bauchi a sakamakon zargin cin mutunci ko zagin Gwamnan jihar Bauchi a yayin wani gangamin yakin neman zabe a jihar.

  • Masarautar Bauchi Ta Tuɓe Rawanin Sanata Kan Sukar Gwamna Bala
  • Rikicin Warware Rawanin Tsohon Wazirin Bauchi Na Ci Gaba Da Daukar Sabon Salo

Sanata Buba ya bayyana martaninsa cikin wata takarda da ya fitar ranar Alhamis 15, ga Augustan 2024 da aka rabawa manema labarai ta kuma yaɗu a shafukan sada zumunta na yanar gizo, Inda ya bayyana cewa; “Ina amfani da wannan dama don bayyana wa jama’a cewa tun lokacin da na shiga harkokin siyasa ba na bin wani tsari na cin zarafin kowa idan ban da suka mai ma’ana ba tare da cin mutunci ko zagin kowa ba, wannan matakin shi ne tsarin da nake bi da nufin samar da ingantacciyar al’umma”.

“A lokacin da na saurari kalaman Gwamna lau Bauchi, Bala Muhammad da ya yi akan Shugaba Tinubu sai na ga hakan ya zama wajibi a kai na da na kare shugaban kasar daga yunkurin da ake yi na ɓata masa suna da zubar kimarsa da ƙoƙarin cusa kiyayyarsa a zukatan al’umma.” Cewar Buba.

Sanata Shehu Buba ya ce wannan shi ne iya abun da ya yi a lokacin yakin neman zaben da APC ta yi da ya halarta a kwanannan.

LABARAI MASU NASABA

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

Sanatan ya ce sai kwatsam ya ji maganganun Gwamna Bala Muhammad akan shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu, wanda kafafen yaɗa labaran ƙasar nan da dama suka rawaito, wan da ya ƙunshi fito da fito da zargi mara tushe da kuma kage, da amfani da kalamai da ka iya kawo barazana ta fuskar tsaro a ƙasa.

Sanatan ya kuma ƙara jaddada cewa zarge-zargen da Gwamna Bala Muhammad ya yi wa Shugaba Tinubu, kalamai ne na siyasa, ba su da tushe kuma ba su da wata cikakkiyar hujja da dalilai da za a dogara da su.

Sannan ya ce cikin kalamansa da ya yi ya musanta zargin da Gwamna Bala ya yi wa Gwamnatin Tinubu na rashin kula da aiki da Kare muradun al’ummar ƙasa. Tabbas ya ce ya zargi Gwamna Bala da aikata hakan.

Sanatan ya ce a jawabinsa da ya yi ya ce Gwamna Bala Muhammad ya karɓi Naira Biliyan144 daga asusun Gwamnatin Tarayya a Shekarar 2023 da kuma fiye da Naira Biliyan 47 daga watan Janairu zuwa yau, wanda ake sa ran a jumla ce za su kai Naira Biliyan 195 zuwa karshen wannan shekarar, na kima nemi bahasi akan cewa me Gwamnatin Bala Muhammad ta yi da wadannan makudan kudade.

Buba ya ce Shugaba Tinubu na yin iya bakin kokarinsa na ganin an samar da tsaro a faɗin Tarayyar Nijeriya da daidaita tattalin arziki da ganin an samu zaman lafiya tsakanin ‘yan ƙasa ba tare da samun rabuwar kai ba.

Buba ya ce shi kalamansa bai yi su da wata niyya ba face da kyayyakwar manufa da kare shugaban Tinubu.

A ƙarshe ya shawarci Majalisar Masarautar Bauchi da ta guji amfani da tunanin wasu, wanda hakan ka iya yi kawo cikasa wajen cimma manufofin masarautar.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja
Manyan Labarai

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

November 4, 2025
Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo
Manyan Labarai

Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

November 4, 2025
Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 
Manyan Labarai

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

November 4, 2025
Next Post
Inec

Laifukan Zabe Barazana Ne Ga Samun Sahihan Zabuka A Nijeriya – INEC

LABARAI MASU NASABA

Jami’an Tsaro Sun Dawo Da Fasfo Ɗin Sanata Natasha Bayan Ƙwace Shi A Abuja

Natasha Ta Zargi Akpabio Da Sanya Jami’an Tsaro Su Ƙwace Mata Fasfo A Filin Jirgin Saman Abuja 

November 4, 2025
Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

Masu Kashe Mutane A Kudu Maso Gabas Kiristoci Ne – Soludo

November 4, 2025
Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

Ribadu Ya Gana Da Hafsoshin Tsaro Biyo Bayan Kalaman Trump 

November 4, 2025
Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

Sarkin Kasar Spaniya Zai Kawo Ziyara Kasar Sin

November 3, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

Sin Ta Yi Watsi Da Zargin Trump Dangane Da Gwajin Nukiliya A Asirce

November 3, 2025
An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

An Bude Taron Kasuwanci Na Duniya Na 18 A Macau

November 3, 2025
“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

“Ƴan Adawa Sun Wuce Gona da Iri — Wike Ya Soki Masu Goyon Bayan  Trump

November 3, 2025
Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

Shugabannin Wasu Kasashe Za Su Halarci Baje Kolin CIIE Karo Na Takwas A Birnin Shanghai

November 3, 2025
Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

Li Qiang Zai Halarci Bikin Bude Taron CIIE Na 8 Da Sauran Ayyuka

November 3, 2025
Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

Likitocin Gwamnati Sun Zargi Gwamnatin Tarayya Da Yaɗa Bayanai Na Karya

November 3, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.