• English
  • Business News
Monday, July 28, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na Yi Mamakin Ganin Takardar Tuɓe Rawanina Na Sarautar Mujaddadin Bauchi – Sanata Buba

by Muhammad
12 months ago
in Labarai
0
Na Yi Mamakin Ganin Takardar Tuɓe Rawanina Na Sarautar Mujaddadin Bauchi – Sanata Buba
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sanata Shehu Buba, wanda shi ne Shugaban Kwamitun Majalisar Dattijai kan tsaro da tattara bayanan sirri, ya ce ya ci karo da wani labari mai ban mamaki kan wata wasika mai ɗauke da kwanan watan 14 ga watan Augustan 2024.

Sanatan ya ce takardar mai ɗauke da sakon cewa Majalisar Masarautar Bauchi ta warware rawaninsa daga Sarautar Mujaddadin Bauchi a sakamakon zargin cin mutunci ko zagin Gwamnan jihar Bauchi a yayin wani gangamin yakin neman zabe a jihar.

  • Masarautar Bauchi Ta Tuɓe Rawanin Sanata Kan Sukar Gwamna Bala
  • Rikicin Warware Rawanin Tsohon Wazirin Bauchi Na Ci Gaba Da Daukar Sabon Salo

Sanata Buba ya bayyana martaninsa cikin wata takarda da ya fitar ranar Alhamis 15, ga Augustan 2024 da aka rabawa manema labarai ta kuma yaɗu a shafukan sada zumunta na yanar gizo, Inda ya bayyana cewa; “Ina amfani da wannan dama don bayyana wa jama’a cewa tun lokacin da na shiga harkokin siyasa ba na bin wani tsari na cin zarafin kowa idan ban da suka mai ma’ana ba tare da cin mutunci ko zagin kowa ba, wannan matakin shi ne tsarin da nake bi da nufin samar da ingantacciyar al’umma”.

“A lokacin da na saurari kalaman Gwamna lau Bauchi, Bala Muhammad da ya yi akan Shugaba Tinubu sai na ga hakan ya zama wajibi a kai na da na kare shugaban kasar daga yunkurin da ake yi na ɓata masa suna da zubar kimarsa da ƙoƙarin cusa kiyayyarsa a zukatan al’umma.” Cewar Buba.

Sanata Shehu Buba ya ce wannan shi ne iya abun da ya yi a lokacin yakin neman zaben da APC ta yi da ya halarta a kwanannan.

Labarai Masu Nasaba

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

Sanatan ya ce sai kwatsam ya ji maganganun Gwamna Bala Muhammad akan shugaban ƙasa, Bola Ahmad Tinubu, wanda kafafen yaɗa labaran ƙasar nan da dama suka rawaito, wan da ya ƙunshi fito da fito da zargi mara tushe da kuma kage, da amfani da kalamai da ka iya kawo barazana ta fuskar tsaro a ƙasa.

Sanatan ya kuma ƙara jaddada cewa zarge-zargen da Gwamna Bala Muhammad ya yi wa Shugaba Tinubu, kalamai ne na siyasa, ba su da tushe kuma ba su da wata cikakkiyar hujja da dalilai da za a dogara da su.

Sannan ya ce cikin kalamansa da ya yi ya musanta zargin da Gwamna Bala ya yi wa Gwamnatin Tinubu na rashin kula da aiki da Kare muradun al’ummar ƙasa. Tabbas ya ce ya zargi Gwamna Bala da aikata hakan.

Sanatan ya ce a jawabinsa da ya yi ya ce Gwamna Bala Muhammad ya karɓi Naira Biliyan144 daga asusun Gwamnatin Tarayya a Shekarar 2023 da kuma fiye da Naira Biliyan 47 daga watan Janairu zuwa yau, wanda ake sa ran a jumla ce za su kai Naira Biliyan 195 zuwa karshen wannan shekarar, na kima nemi bahasi akan cewa me Gwamnatin Bala Muhammad ta yi da wadannan makudan kudade.

Buba ya ce Shugaba Tinubu na yin iya bakin kokarinsa na ganin an samar da tsaro a faɗin Tarayyar Nijeriya da daidaita tattalin arziki da ganin an samu zaman lafiya tsakanin ‘yan ƙasa ba tare da samun rabuwar kai ba.

Buba ya ce shi kalamansa bai yi su da wata niyya ba face da kyayyakwar manufa da kare shugaban Tinubu.

A ƙarshe ya shawarci Majalisar Masarautar Bauchi da ta guji amfani da tunanin wasu, wanda hakan ka iya yi kawo cikasa wajen cimma manufofin masarautar.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Gwamna Bala MuhammadMasarautar BauchiSanata Buba Shehu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jihohi Sun Kashe Naira Biliyan 139.92 Wajen Biyan Bashin Kasashen Ketare A Wata 6

Next Post

Laifukan Zabe Barazana Ne Ga Samun Sahihan Zabuka A Nijeriya – INEC

Related

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar
Labarai

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

10 hours ago
Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo
Labarai

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

11 hours ago
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas
Labarai

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

14 hours ago
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa
Manyan Labarai

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

15 hours ago
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano
Labarai

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

17 hours ago
ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark
Labarai

ADC Ce Za Ta Haɗa Kan Arewa Wajen Kawo Ci Gaba — Mark

18 hours ago
Next Post
Inec

Laifukan Zabe Barazana Ne Ga Samun Sahihan Zabuka A Nijeriya – INEC

LABARAI MASU NASABA

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

Mazauna Sokoto Sun Yi Murna Bayan Nasarar Kashe Fitattun ‘Yan Bindiga 3 A Jihar

July 27, 2025
Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

Zhao Leji Ya Kai Ziyarar Sada Zumunta A Kyrgyzstan

July 27, 2025
Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

Gwamnan Bauchi Ya Sulhunta Rikicin Manoma Da Makiyaya A Darazo

July 27, 2025
Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

Sin Ta Samu Ci Gaban Aikin Jigilar Kaya A Rabin Farko Na Bana

July 27, 2025
Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

Kudin Shigar Da Kasuwar Fina-Finai Ta Sin Ta Samu A Lokacin Zafi Na Bana Ya Zarce Yuan Biliyan 5

July 27, 2025
Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

Shanghai Ya Gabatar Da Shirin Gina Yankin Motoci Masu Tuka Kansu

July 27, 2025
Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

Sin: Fasahar Rage Asarar Hatsi Ta Yi Amfani

July 27, 2025
‘Yansanda Sun Cafke Wasu Sojojin Bogi 2 A Legas

‘Yansanda Sun Kashe ‘Yanbindiga Uku Da Kama AK-47 Guda Goma

July 27, 2025
Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

Shetima Zai Wakilci Nijeriya A Taron Tsarin Abinci A Addis Ababa

July 27, 2025
Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

Gwamnati Ta Ba Da Wa’adin Mako 6 Don Kammala Ginin Rukunin Gidaje A Kano

July 27, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.