ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Rikicin Warware Rawanin Tsohon Wazirin Bauchi Na Ci Gaba Da Daukar Sabon Salo

by Khalid Idris Doya
4 years ago
Wazirin Bauchi

A makon jiya LEADERSHIP Hausa ta ruwaito cewa masarautar Bauchi ta tsige Alhaji Muhammadu Bello Kirfi daga sarautar Wazirin Bauchi bisa zarginsa da rashin da’a da biyayya ga gwamnan Jihar Bala Muhammad.

Sai dai wakilinmu ya binciko cewa rashin fahimta ce ta siyasa ta gitta a tsakaninsu. Ko da yake shi Bello Kirfi da gwamnan jihar dukkaninsu ‘ya’yan jam’iyyar PDP ne.
Rahotonni sun bayyana cewa, shi dai Bello Kirfi wanda dattijo ne kuma tsohon ministan ayyukan musamman a Nijeriya, kana dan gani kashenin Atiku Abubakar ne, ya kira wani taro inda ya bukaci jama’an Jihar Bauchi da su zabi dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar amma a matakin gwamnan jihar kuma kowa ya zabi wanda yake so.

  • An Tsige Wazirin Masarautar Bauchi Kan Rashin Yi Wa Gwamna Biyayya

Ana ganin wannan dalilin ne ya fusata gwamna Bala Muhammad da har aka kai ga daukan matakin cire shi daga mukaminsa.
LEADERSHIP Hausa ta zanta da wani makusancin tsohon Wazirin Bauchi, Lawan Mukhtari Ladan, inda ya bayyana cewar babu komai a cikin lamarin illa batun da ya shafi harkokin siyasa da rashin fahimta irin ta siyasa.

ADVERTISEMENT

“Wannan ba shi ne na farko da aka fara ba kuma dukkanin wadannan abubuwan da ka ga su na faruwa suna faruwa ne a kan gaskiya. Shi Alhaji Bello Kirfi mutum ne da yake da gaskiya yake da kaifi guda daya a dukkanin al’amuransa.

“Matsalar da ya samu a can baya aka dakatar da shi duka a kan irin wadannan abubuwan ne, zai zo ya fadi gaskiya ga gwamnati domin a samu gyare-gyare amma sai a zo ana samun matsaloli. Shi gwamna da ke jin giyar mulki sai ya yi abun da yake so.

LABARAI MASU NASABA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

“Yanzu dakatar da Baba Waziri da ya yi bai isa ya ce zai cire sunansa a zukatan jama’an Jihar Bauchi ba. Sannan kuma abun da ya faru shi ne, a matsayinsa na uban kasa ya ba da shawara cewa Bala Muhammad ya hakura da maganar takarar shugaban kasa tun da farko amma bai yi hakan ba tun daga lokacin ne fa aka fara samun matsala.

“Alhaji Muhammad Bello ya kira taro ya ce ga Allah ya kawo Atiku zai yi takarar shugaban kasa, yankinmu na Arewa Maso Gabas ba mu taba yin shugaban kasa ba amma yanzu ga dama ta samu don haka yana neman alfarman jama’a da su zabi Atiku.”

A nasa bangaren, kwamishinan kananan hukumomi da masarautun gargajiya na Jihar Bauchi, Honorabul Abdulrazak Nuhu Zaki, ya ce sarakuna ne suka dauki matakin ladabtarwa.

“Sun kawo min takarda na ainihin sallamar Alhaji Muhammadu Bello Kirfi daga matsayin Wazirin Bauchi a wannan lokacin wanda tuni aka maye gurbi sa da Garkuwan Bauchi, Alhaji Mohammadu Uba Ahmed Kari da aka daukaka matsayinsa zuwa Wazirin Bauchi.
“Da an taba koranshi, Mai girma gwamnan Jihar Bauchi ya yi kokari ya maida shi ba tare da masarautar Bauchi tana so ba, ya je ya samu Mai Martaba Sarkin Bauchi ya ce ya yi hakuri da duk abun da ya musu a matsayin babansa, amma bai fasa abubuwan da yake yi ba.

“Wannan ne ya shi Mai girma gwamnan ya ce shi ma ya cire hannunsa kamar yadda suka niyyar cire shi, kuma daga yanzu ba ruwansa domin abun da yake musu ba daidai ba ne.”
“In ma ya zama yaya ne dai an cire shi, muna wa wanda ya samu kujerar fatan Allah ya taimakeshi ya rike sarautar da mutunci.

Domin kujera ce wacce take da bukatar mutum ya kame ya zama yana kiyayewa daga shiga harkar da ba irin ta su ba,” in ji Zaki.

Kakakin Jam’iyyar PDP, Alhaji Yayanuwa Zainari ya karyata duk wata zance da ke cewa akwai baraka tsakanin Atiku da Bala, inda yake cewa dukkaninsu suna karkashin lema daya kuma kowa na taimakon kowa a cikinsu.

Ya ce, “Ai ba abun da zai hada mai girma gwamnan jihar Bauchi da Atiku, Allah ya yi su a jam’iyya daya kuma kowa zai taimaki kowa, sannan duk inda muka je da gwamna neman alfarmar kuri’a sai mun fara nema wa Atiku a matsayinsa na dan takarar shugaban kasa, to ka ga ba wata matsala.

“Ita maganar sarauta in ka duba ma shi Waziri ba mai zaban sarki ba ne, babu hannun gwamna a kan takardar Waziri domin sarki ne yake nada Waziri. Don haka ka da a hada maganar sarauta da maganar siyasa.”
Sai dai kuma a gefe guda, Bello Kirfi ya maka gwamnatin Jihar Bauchi a kotu bisa abun da ya kira cire shi ba bisa ka’ida ba.

A wata sanarwar da mai magana da yawunsa, Barista Yakubu Bello Kirfi ya fitar ya bayyana cewa an yada wani labari na karya da aka ce Muhammad Bello Kirfi ya sha alwashin sai ya yi duk mai yiyuwa domin dakile zarcewar Bala Muhammad.
“Hankulanmu sun karkata kan wasu rahotonnin da aka wallafa a ranar 8 da 9 ga watan Janairun 2023 da aka nakalto cewa Alhaji Dakta Muhammad Bello Kirfi CON, na cewa zai yi duk mai yiyuwa domin cire gwamna Bala Muhammad daga kujerar gwamna ta hanyar hana masa nasarar zarcewa a zaben 2023 da ke tafe.

“Labarin sam babu gaskiya a ciki. A matsayinsa na musulmi, yayi imani da kaddara, kuma Allah ne mai iko, yana kuma ba da mulki ne ga wanda ya so ya karba daga hannun wanda ya so a lokacin da ya so.
“Cire shi da aka yi a matsayin Wazirin Bauchi kuma mambar majalisar sarkin Bauchi da aka yi a ranar 3 ga watan Janairu, gwamnatin Bauchi ce ke da hannu a ciki inda ta yi amfani da masarauta kuma hakan ya janyo ce-ce-ku-ce sosai a fadin jihar.”

Tunin dai Sarkin Bauchi, Dakta Rilwanu Sulaiman Adamu ya nada sabon Wazirin Bauchi, Alhaji Mohammadu Uba Ahmad Kari.
Nadin na Kari na zuwa ne bayan tunbuke rawanin tsohon Wazirin Alhaji Muhammadu Bello Kirfi bisa abun da aka ce rashin biyayya da mutunta gwamnan Jihar Bauchi, Bala Muhammad.

Wazirin Bauchi
Khalid Idris Doya
+ postsBio
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    ATBU Ta Janye Filin Ginin Masallaci Da Ta Bai wa TIMSAN, Ta Amince Kowa Ya Yi Addininsa Yadda Ya Fahimta
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Ɗan Majalisar Dokokin Bauchi, Hon. Wanzam, Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Tsohon Mataimakin Gwamnan Bauchi, Audu Sule Katagum Ya Rasu
  • Khalid Idris Doya
    https://hausa.leadership.ng/author/khalid-idris-doya/
    Kotu Ta Umarci DSS Ta Mutunta Umarninta Kan Shari’ar Filin Firo Na Bauchi

MASU ALAKA

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya
Rahotonni

Na Yi Tsayin-daka Domin Cika Alƙawarin Ƙasata Nijeriya

July 14, 2026
Labarin Farfesoshi Tagwaye Da Suka Yi Karatun Digiri Tare Suna Aiki Tare A Wuri Ɗaya
Rahotonni

Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa

July 11, 2026
Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji
Rahotonni

Matsalar Tsaro: Masana Sun Firgita Da Fitowar Sabon Bidiyon Bello Turji

June 26, 2026
Next Post
Kotu Ta Fara Sauraren Shari’ar Raba Auren ‘Yar Ganduje A Kano

Kotu Ta Fara Sauraren Shari'ar Raba Auren 'Yar Ganduje A Kano

LABARAI MASU NASABA

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

Tsohon Ɗan Takarar Gwamnan SDP A Gombe Ya Koma PDP, Ya Mara Wa Pantami Baya

July 15, 2026
Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

Zazzaɓin Lassa: Mutum 31 Sun Kamu Da Cutar A Jihohi 4, Waɗanda Suka Rasu Sun Kai 221

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

‘Yansanda Sun Kama Shugaban PFIPC, Adeyemi

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

‘Yansanda Sun Kama Wani Kan Zargin Yi Wa ‘Yan Bindiga Safarar Makamai A Kano

July 15, 2026
Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.