• English
  • Business News
Tuesday, August 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nadin Sabbin Ministoci: Kallo Ya Koma Kan Majalisar Dattawa

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Sabbin Ministoci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yanzu haka dai kallo ya koma kan Majalisar Dattawa dangane da batun nadin sabbin ministocin Gwamnatin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu.

‘Yan Nijeriya na ta dakon ganin wadanda za a nada tun daga farkon watan nan na Yuli bisa yadda ake ganin gwamnatin kamar ta zo a shirye, za ta yi komai cikin hanzari a kokarinta na fara gudanar da aikace-aikace da ‘yan kasa za su gani-a-kasa.

  • Za A Fitar Da Karin Sunayen Ministoci –Gbajabiamila

Kamar yadda sashe na 42, karamin sashe na daya na tsarin mulkin Nijeriya ya fada, an bai wa Shugaba Tinubu wa’adin gabatar da sunayen ministocin daga ranar da aka rantsar da shi 29 ga Mayun 2023 zuwa ranar 28 ga Yuli. “Za a gabatar da sunan duk wanda ake son nadawa a mukamin minista ga Majalisar Dattawa domin tabbatarwa bayan kwana 60 da rantsar da shugaban kasa”.

Domin kawar da jiran tsammanin da aka dade ana yi, a ranar Talatar makon nan, Shugaban Masu Rinjaye na Majalisar Dattawa, Sanata Micheal Opeyemi Bamidele ya tabbatar da cewa kafin karshen makon komai zai daidaita dangane da gabatar da sunayen sabbin ministocin.

A ‘yan makwannin da suka gabata dai, an yi ta yawo da wani jerin sunayen mutane a matsayin wadanda Tinubu yake son nadawa minstoci, sai dai mai magana da yawun shugaban kasan, Dele Alake ya bayyana sunayen a matsayin na bogi.

Labarai Masu Nasaba

Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi

Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna

Hukumomin tsaro da sauran masu ruwa da tsaki sun kammala duk binciken da suka kamata a kan sabbin ministocin.

Kamar yadda aka saba gani a gwamnatocin baya, Majalisar Dattawa za ta kwashe tsawon wasu kwanaki tana aikin tantance wadanda ake son nadawa ministocin. Inda wani lokaci ake watsawa kai-tsaye ta gidajen talabijin domin ‘yan kasa su shaida yadda lamarin ke gudana.

A yayin tantancewar dai, ‘yan majalisar ta dattawa kan gabatar da tambayoyi ga mutanen da aka mika sunayensu kan abubuwan da suka shafi asalin mutum, basira da kwarewar aiki, wani lokaci har da gudunmawar da mutum ya bayar ga jam’iyya mai mulki.

Haka nan ‘yan majalisar kan sauwake wa galibin wadanda suka taba zama ‘yan majalisa daga cikin sabbin ministocin, inda ba a musu tambayoyi sai dai a ce su yi gaisuwar girmamawa ga ‘yan majalisar su tafi. Lamarin da wasu masu fashin baki ke kallon son zuciya ne saboda ba duk wanda ya taba zama dan majalisa ba ne yake da basirar aiki musamman yadda wasu kan zama masu dumama kujera ba tare da gabatar da kudiri ko daya ba tun daga farko har karshen wa’adinsu na shekara hudu.

Bayan kammala tantance wadanda ake son nadawa ministocin dai, Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu zai raba musu ma’aikatun da za su yi aiki inda ake sa ran a tura kowa ma’aikatar da ake ganin yana da basira da kwazon da zai iya tafiyar da ita domin kawo ci gaba.

Ministoci su ne kashin bayan gudanar da ayyukan gwamnati, saboda duk aikin da gwamnatin tarayya za ta gudanar a karkashinsu ne, su suke tsarawa su gabatar, shugaban kasa ya rattaba hannu a kai bayan an cimma matsaya a taron majalisar zartaswa ta kasa.

Tinubu ya yi alkawarin tafiyar da gwamnatin hadin kasa tare da jam’iyyun adawa da kuma bangarorin kwararru wadanda ba ‘yan siyasa ba, sai dai nade-naden mukaman da zai yi ne za su tabbatar da abin da ya fada ko akasin haka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Manyan Ayyukan Tasoshin Teku Da Aka Watsar A Nijeriya…

Next Post

Juyin Mulki: ECOWAS Ta Lashi Takobin Tabbatar Da Dimokuradiyya A Nijar

Related

Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi
Manyan Labarai

Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi

5 hours ago
Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna
Manyan Labarai

Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna

6 hours ago
Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya
Labarai

Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya

9 hours ago
Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe
Labarai

Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe

9 hours ago
Ku Yaƙi Cin Hanci Ba Ƴan Adawa Ba – ADC GA EFCC
Labarai

Ku Yaƙi Cin Hanci Ba Ƴan Adawa Ba – ADC GA EFCC

11 hours ago
Jiragen Saman NAF Sun Kai Hari Kan Taron ‘Yan Bindiga 400 A Zamfara
Manyan Labarai

Jiragen Saman NAF Sun Kai Hari Kan Taron ‘Yan Bindiga 400 A Zamfara

13 hours ago
Next Post
ECOWAS

Juyin Mulki: ECOWAS Ta Lashi Takobin Tabbatar Da Dimokuradiyya A Nijar

LABARAI MASU NASABA

Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi

Babban Dalilin EFCC Na Yi Wa Tsohon Gwamnan Sokoto, Tambuwal, Tambayoyi

August 11, 2025
Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna

Tireloli Sun Yi Taho Mu Gama, Mutane 4 Sun Jikkata A Titin Zariya–Kaduna

August 11, 2025
An Samu Karuwar Adadin Kamfanoni Masu Yin Rajista A Yankin HK

An Samu Karuwar Adadin Kamfanoni Masu Yin Rajista A Yankin HK

August 11, 2025
Sashen Masana’antun Kirar Motoci Na kasar Sin Ya Samu Gi Gaba A Watan Yuli

Sashen Masana’antun Kirar Motoci Na kasar Sin Ya Samu Gi Gaba A Watan Yuli

August 11, 2025
Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya

Shettima Ya Jagoranci Tawagar Gwamnatin Tarayya Don Yi Wa Iyalan Ogbeh Ta’aziyya

August 11, 2025
Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe

Manoma 2 Sun Rasu, 2 Sun Jikkata A Wani Rikicin Filin Gona A Yobe

August 11, 2025
Tattalin Arzikin Kasar Sin Na Da Makoma Mai Haske In Ji Wani Kwararre 

Tattalin Arzikin Kasar Sin Na Da Makoma Mai Haske In Ji Wani Kwararre 

August 11, 2025
Sin Ta Kammala Yi Wa Yankuna 5 Na Kare Muhalli Da Halittu Na Kasar Rajista

Sin Ta Kammala Yi Wa Yankuna 5 Na Kare Muhalli Da Halittu Na Kasar Rajista

August 11, 2025
Ku Yaƙi Cin Hanci Ba Ƴan Adawa Ba – ADC GA EFCC

Ku Yaƙi Cin Hanci Ba Ƴan Adawa Ba – ADC GA EFCC

August 11, 2025
Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro

Masana Kimiyya Na Sin Sun Samar Da Fasahar Sa Ido Kan Cututtukan Da Ake Samu Daga Sauro

August 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.