• English
  • Business News
Friday, September 19, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nadin Sabbin Ministoci: Kallo Ya Koma Kan Majalisar Dattawa

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Sabbin Ministoci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yanzu haka dai kallo ya koma kan Majalisar Dattawa dangane da batun nadin sabbin ministocin Gwamnatin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu.

‘Yan Nijeriya na ta dakon ganin wadanda za a nada tun daga farkon watan nan na Yuli bisa yadda ake ganin gwamnatin kamar ta zo a shirye, za ta yi komai cikin hanzari a kokarinta na fara gudanar da aikace-aikace da ‘yan kasa za su gani-a-kasa.

  • Za A Fitar Da Karin Sunayen Ministoci –Gbajabiamila

Kamar yadda sashe na 42, karamin sashe na daya na tsarin mulkin Nijeriya ya fada, an bai wa Shugaba Tinubu wa’adin gabatar da sunayen ministocin daga ranar da aka rantsar da shi 29 ga Mayun 2023 zuwa ranar 28 ga Yuli. “Za a gabatar da sunan duk wanda ake son nadawa a mukamin minista ga Majalisar Dattawa domin tabbatarwa bayan kwana 60 da rantsar da shugaban kasa”.

Domin kawar da jiran tsammanin da aka dade ana yi, a ranar Talatar makon nan, Shugaban Masu Rinjaye na Majalisar Dattawa, Sanata Micheal Opeyemi Bamidele ya tabbatar da cewa kafin karshen makon komai zai daidaita dangane da gabatar da sunayen sabbin ministocin.

A ‘yan makwannin da suka gabata dai, an yi ta yawo da wani jerin sunayen mutane a matsayin wadanda Tinubu yake son nadawa minstoci, sai dai mai magana da yawun shugaban kasan, Dele Alake ya bayyana sunayen a matsayin na bogi.

Labarai Masu Nasaba

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

Hukumomin tsaro da sauran masu ruwa da tsaki sun kammala duk binciken da suka kamata a kan sabbin ministocin.

Kamar yadda aka saba gani a gwamnatocin baya, Majalisar Dattawa za ta kwashe tsawon wasu kwanaki tana aikin tantance wadanda ake son nadawa ministocin. Inda wani lokaci ake watsawa kai-tsaye ta gidajen talabijin domin ‘yan kasa su shaida yadda lamarin ke gudana.

A yayin tantancewar dai, ‘yan majalisar ta dattawa kan gabatar da tambayoyi ga mutanen da aka mika sunayensu kan abubuwan da suka shafi asalin mutum, basira da kwarewar aiki, wani lokaci har da gudunmawar da mutum ya bayar ga jam’iyya mai mulki.

Haka nan ‘yan majalisar kan sauwake wa galibin wadanda suka taba zama ‘yan majalisa daga cikin sabbin ministocin, inda ba a musu tambayoyi sai dai a ce su yi gaisuwar girmamawa ga ‘yan majalisar su tafi. Lamarin da wasu masu fashin baki ke kallon son zuciya ne saboda ba duk wanda ya taba zama dan majalisa ba ne yake da basirar aiki musamman yadda wasu kan zama masu dumama kujera ba tare da gabatar da kudiri ko daya ba tun daga farko har karshen wa’adinsu na shekara hudu.

Bayan kammala tantance wadanda ake son nadawa ministocin dai, Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu zai raba musu ma’aikatun da za su yi aiki inda ake sa ran a tura kowa ma’aikatar da ake ganin yana da basira da kwazon da zai iya tafiyar da ita domin kawo ci gaba.

Ministoci su ne kashin bayan gudanar da ayyukan gwamnati, saboda duk aikin da gwamnatin tarayya za ta gudanar a karkashinsu ne, su suke tsarawa su gabatar, shugaban kasa ya rattaba hannu a kai bayan an cimma matsaya a taron majalisar zartaswa ta kasa.

Tinubu ya yi alkawarin tafiyar da gwamnatin hadin kasa tare da jam’iyyun adawa da kuma bangarorin kwararru wadanda ba ‘yan siyasa ba, sai dai nade-naden mukaman da zai yi ne za su tabbatar da abin da ya fada ko akasin haka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Manyan Ayyukan Tasoshin Teku Da Aka Watsar A Nijeriya…

Next Post

Juyin Mulki: ECOWAS Ta Lashi Takobin Tabbatar Da Dimokuradiyya A Nijar

Related

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi
Labarai

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

23 minutes ago
Sabbin Ministoci
Labarai

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

3 hours ago
Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 
Rahotonni

Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

4 hours ago
Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa Ɗaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma
Labarai

Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa Ɗaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma

4 hours ago
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Harajin Kashi 4 Na Shigo Da Kaya Wanda Ya Janyo Cece-kuce

4 hours ago
GORON JUMA’A 01-07-2025
Labarai

GORON JUMA’A 19-09-2025

5 hours ago
Next Post
ECOWAS

Juyin Mulki: ECOWAS Ta Lashi Takobin Tabbatar Da Dimokuradiyya A Nijar

LABARAI MASU NASABA

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

Wata Mata Ta Ƙona Al’aurar Ƙaramar Yarinya A Bauchi

September 19, 2025
Sabbin Ministoci

Murnar Maulidin Cikar Manzon Allah (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa (2)

September 19, 2025
Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

Maulud 1,500: Yadda Zawiyar Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Ta Yi Maulidin Takutaha A Kaduna 

September 19, 2025
Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa Ɗaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma

Matatar Dangote Ta Dakatar Da Zuwa Ɗaukar Man Fetur, Sai Dai Ka Saya Ta Kai Ma

September 19, 2025

Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Harajin Kashi 4 Na Shigo Da Kaya Wanda Ya Janyo Cece-kuce

September 19, 2025
GORON JUMA’A 01-07-2025

GORON JUMA’A 19-09-2025

September 19, 2025
Sabbin Ministoci

2027: Su Wane Ne Ke Tsoron Guguwar Makinde A Jam’iyyar  PDP

September 19, 2025
Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

Nan Ba Da Jimawa Ba Hauhawar Farashin Kayayyaki Za Ta Zama Tarihi —Fadar Shugaban

September 19, 2025
Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

Ce-ce-kuce Kan Shirin Ƙara Wa Ƴan Siyasa Masu Riƙe Da Madafun Iko Albashi

September 19, 2025
An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

An Yi Bikin Tunawa Da Ranar Kaddamar Da Yakin Kin Mamayar Dakarun Japan A Birnin Shenyang

September 18, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.