• English
  • Business News
Monday, June 30, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Juyin Mulki: ECOWAS Ta Lashi Takobin Tabbatar Da Dimokuradiyya A Nijar

by Sulaiman and Sadiq
2 years ago
in Labarai
0
ECOWAS
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Shugaban Kungiyar Raya Tattalin Arzikin Kasashen Yammacin Afirka (ECOWAS) kuma Shugaban Nijeriya, Bola Ahmed Tinubu, ya mayar da martani kan rikicin siyasa a Jamhuriyar Nijar, inda ya bayyana goyon kungiyar ga zababbiyar gwamnatin dimokuradiyya a kasar.

Tinubu ya jaddada cewa ECOWAS ta lashi takobin tabbatar da mulkin dimokuradiyya da tsarin mulki a kasar ya shimfida tare da gargadin sojojin da ke kwadayin mulki ko ta halin kaka su shiga taitayinsu.

  • Juyin Mulki: Amurka Ta Bukaci Gaggauta Sakin Bazoum

Tinubu ya jaddada cewa yankin zai tsaya tsayin daka wajen goyon bayan zababbiyar gwamnati a Nijar. Ya jaddada muhimmancin kiyaye dimokuradiyya ga al’ummar Nijar da zaman lafiya da ci gaban yankin yammacin Afirka baki daya.

Ya ce, “Bayanan da ke fitowa daga Jamhuriyar Nijar na nuni da cewa wasu abubuwa marasa dadi na faruwa a kan manyan shugabannin siyasar kasar.

“Ya kamata duk wadanda suke da hannu a lamarin sun san cewa shugabannin yankin ECOWAS da duk masu kaunar dimokuradiyya a duniya ba su goyi bayan wannan lamari ba.
“Shugabannin ECOWAS ba za su amince da duk wani mataki da zai kawo cikas ga halattacciyar gwamnatin Nijar ko wani yanki na yammacin Afirka ba.

Labarai Masu Nasaba

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

“Ina so sanar da cewa muna sa ido sosai kan al’amura da abubuwan da ke faruwa a Nijar kuma za mu yi duk abin da ya dace don tabbatar da cewa dimokuradiyya ta kafu, ta bunkasa, da tushe mai kyau a yankinmu.
“Ina tuntubar sauran shugabannin yankinmu, kuma za mu kare dimokuradiyyar da muke buri bisa ka’idar tsarin mulki wanda kowa ya yarda da shi.

“A matsayina na shugaban kungiyar ECOWAS, ina jadadda aniyar goyon bayan Nijeriya ga zababbiyar gwamnati a Nijar, sannan ina tabbatar da cewar shugabannin ECOWAS ba za su bar Nijar cikin jimami ba, sai mun tsaya tsayin daka don kiyaye tsarin mulkin kasar.”

Kungiyar kasashen yankin ta kara da cewa ba za ta lamunci sake juyin mulki a yammacin Afirka ba.
Nijar kasa ce da ba ta da ruwa a yammacin Afirka, wadda ta fuskanci juyin mulki hudu tun bayan samun ‘yancin kai daga Faransa a 1960, da kuma yunkurin juyin mulki da dama.

Shugaba Bazoum, wanda aka zaba ta hanyar dimokuradiyya a shekarar 2021, ya kasance babban abokin kasar Faransa da ta yi wa kasar mulkin mallaka.

Juyin mulki na karshe a kasar ya faru ne a watan Fabrairun 2010, wanda ya hambarar da shugaba Mamadou Tandja na lokacin.

Nijar dai na fama da boren mayakan Jihadi guda biyu – daya a kudu maso yammacin kasar, wanda tagayyara makwabciyar kasar Mali a shekarar 2015, dayan kuma a kudu maso gabas, wanda ya hada da mayakan jihadi dake arewa maso gabashin Nijeriya.

Kungiyoyin masu fafutuka da ke da alaka da al-Kaeda da kuma kungiyar IS sun addabi kasar a shekarun baya-bayan nan wanda ya kai ga mutuwar mutane.

Kasashen Yammacin Afirka na kara fuskantar matsalar juyin mulki a ‘yan kwanakin nan. Mali Guinea da Burkina Faso sun fuskanci juyin mulki kwanan nan a cikin mawuyacin hali na tattalin arziki da talauci.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Nadin Sabbin Ministoci: Kallo Ya Koma Kan Majalisar Dattawa

Next Post

“Da Mijina Ya Yi Min Kishiya, Gwamma Ya Rika Kwanciya Da ‘Ya`yanmu”

Related

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano
Labarai

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

2 hours ago
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa
Manyan Labarai

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

3 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

4 hours ago
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara
Manyan Labarai

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

6 hours ago
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata
Labarai

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Isa Saudiyya Don Halartar Jana’izar Ɗantata

11 hours ago
Yaushe Za A Dakatar Da Yi Wa `Yan Arewa Kisan Gilla?
Labarai

‘Yan Bindiga Sun Sake Kai Hari Kan Al’ummar Benuwe, Sun Kashe ‘Yansanda 4

12 hours ago
Next Post
“Da Mijina Ya Yi Min Kishiya, Gwamma Ya Rika Kwanciya Da ‘Ya`yanmu”

“Da Mijina Ya Yi Min Kishiya, Gwamma Ya Rika Kwanciya Da ‘Ya`yanmu”

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

Sin Na Fatan More Fasahohi Da Kirkire-kirkire Da Kasashen Duniya Don Sa Kaimi Ga Ci Gaba Da Zamanintar Da Kasashen Duniya

June 30, 2025
Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

Jarumin Matashi Ya Ragargaji  Wani Ɗan Fashi A Kano

June 30, 2025
Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

Xi Ya Jaddada Bukatar Yin Aiki Tukuru Wajen Aiwatar Da Jagorancin Jam’iyya Bisa Kyawawan Akidu

June 30, 2025
Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

Sin Ta Yi Watsi Da Bangaren Rahoton SAGO Mai Nasaba Da Binciken Tushen Cutar COVID-19

June 30, 2025
Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

Bello Turji, Yana Neman Ayi Sulhu Bayan An Kashe Yaronsa

June 30, 2025
Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

Tawagar Gwamnatin Tarayya Ta Miƙa Saƙon Ta’aziyyar Shugaba Tinubu A Gidan Ɗantata Na Madina

June 30, 2025
Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

Alkaluman PMI Na Sin Na Bunkasa Cikin Watanni 2 A Jere

June 30, 2025
CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

CAF Za Ta Ƙaddamar Da Sabon Kofin Gasar Ƙasashen Afrika Na Mata

June 30, 2025
Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

Sin Ta Kammala Aikin Agajin Gaggawa A Yankin Da Ambaliyar Ruwa Ta Afku

June 30, 2025
Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

Matasa Sun Ƙona Ofishin NDLEA, Sun Kutsa Fadar Sarki A Kwara

June 30, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.