• English
  • Business News
Friday, July 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nadin Sabbin Ministoci: Kallo Ya Koma Kan Majalisar Dattawa

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
Sabbin Ministoci
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yanzu haka dai kallo ya koma kan Majalisar Dattawa dangane da batun nadin sabbin ministocin Gwamnatin Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu.

‘Yan Nijeriya na ta dakon ganin wadanda za a nada tun daga farkon watan nan na Yuli bisa yadda ake ganin gwamnatin kamar ta zo a shirye, za ta yi komai cikin hanzari a kokarinta na fara gudanar da aikace-aikace da ‘yan kasa za su gani-a-kasa.

  • Za A Fitar Da Karin Sunayen Ministoci –Gbajabiamila

Kamar yadda sashe na 42, karamin sashe na daya na tsarin mulkin Nijeriya ya fada, an bai wa Shugaba Tinubu wa’adin gabatar da sunayen ministocin daga ranar da aka rantsar da shi 29 ga Mayun 2023 zuwa ranar 28 ga Yuli. “Za a gabatar da sunan duk wanda ake son nadawa a mukamin minista ga Majalisar Dattawa domin tabbatarwa bayan kwana 60 da rantsar da shugaban kasa”.

Domin kawar da jiran tsammanin da aka dade ana yi, a ranar Talatar makon nan, Shugaban Masu Rinjaye na Majalisar Dattawa, Sanata Micheal Opeyemi Bamidele ya tabbatar da cewa kafin karshen makon komai zai daidaita dangane da gabatar da sunayen sabbin ministocin.

A ‘yan makwannin da suka gabata dai, an yi ta yawo da wani jerin sunayen mutane a matsayin wadanda Tinubu yake son nadawa minstoci, sai dai mai magana da yawun shugaban kasan, Dele Alake ya bayyana sunayen a matsayin na bogi.

Labarai Masu Nasaba

Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

Hukumomin tsaro da sauran masu ruwa da tsaki sun kammala duk binciken da suka kamata a kan sabbin ministocin.

Kamar yadda aka saba gani a gwamnatocin baya, Majalisar Dattawa za ta kwashe tsawon wasu kwanaki tana aikin tantance wadanda ake son nadawa ministocin. Inda wani lokaci ake watsawa kai-tsaye ta gidajen talabijin domin ‘yan kasa su shaida yadda lamarin ke gudana.

A yayin tantancewar dai, ‘yan majalisar ta dattawa kan gabatar da tambayoyi ga mutanen da aka mika sunayensu kan abubuwan da suka shafi asalin mutum, basira da kwarewar aiki, wani lokaci har da gudunmawar da mutum ya bayar ga jam’iyya mai mulki.

Haka nan ‘yan majalisar kan sauwake wa galibin wadanda suka taba zama ‘yan majalisa daga cikin sabbin ministocin, inda ba a musu tambayoyi sai dai a ce su yi gaisuwar girmamawa ga ‘yan majalisar su tafi. Lamarin da wasu masu fashin baki ke kallon son zuciya ne saboda ba duk wanda ya taba zama dan majalisa ba ne yake da basirar aiki musamman yadda wasu kan zama masu dumama kujera ba tare da gabatar da kudiri ko daya ba tun daga farko har karshen wa’adinsu na shekara hudu.

Bayan kammala tantance wadanda ake son nadawa ministocin dai, Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu zai raba musu ma’aikatun da za su yi aiki inda ake sa ran a tura kowa ma’aikatar da ake ganin yana da basira da kwazon da zai iya tafiyar da ita domin kawo ci gaba.

Ministoci su ne kashin bayan gudanar da ayyukan gwamnati, saboda duk aikin da gwamnatin tarayya za ta gudanar a karkashinsu ne, su suke tsarawa su gabatar, shugaban kasa ya rattaba hannu a kai bayan an cimma matsaya a taron majalisar zartaswa ta kasa.

Tinubu ya yi alkawarin tafiyar da gwamnatin hadin kasa tare da jam’iyyun adawa da kuma bangarorin kwararru wadanda ba ‘yan siyasa ba, sai dai nade-naden mukaman da zai yi ne za su tabbatar da abin da ya fada ko akasin haka.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Manyan Ayyukan Tasoshin Teku Da Aka Watsar A Nijeriya…

Next Post

Juyin Mulki: ECOWAS Ta Lashi Takobin Tabbatar Da Dimokuradiyya A Nijar

Related

Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal
Labarai

Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

10 hours ago
Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci
Labarai

Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

11 hours ago
Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 1,191, Sun Ceto 543 Cikin Watanni Uku
Tsaro

Sojoji Sun Kama Ƴan Ta’adda 1,191, Sun Ceto 543 Cikin Watanni Uku

11 hours ago
Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa
Ra'ayi Riga

Dutsen Da Amurka Ta Jefa Ya Fado Kasa

12 hours ago
Kamfanin Simintin Dangote Ya Tallafa Wa Manoma 50 A Benue
Labarai

Kamfanin Simintin Dangote Ya Tallafa Wa Manoma 50 A Benue

13 hours ago
Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram
Manyan Labarai

Gwamnatin Yobe Ta Rufe Kasuwanni Uku Saboda Fargabar Hare-haren Boko Haram

14 hours ago
Next Post
ECOWAS

Juyin Mulki: ECOWAS Ta Lashi Takobin Tabbatar Da Dimokuradiyya A Nijar

LABARAI MASU NASABA

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

Sin Na Kara Rungumar Nau’o’in Makamashi Marasa Gurbata Muhalli

July 3, 2025
Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

Bayan Taron Haɗaka, Hankali Wike Ya Tashi — ADC

July 3, 2025
Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

Mai Tsaron Ragar Nijeriya, Peter Rufai Ya Rasu

July 3, 2025
Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

Sin Na Fatan Yin Tafiya Bai Daya Tare Da Amurka 

July 3, 2025
Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

Ƴan PDP Na Fice Wa Na Barin Jam’iyyar Ga Wike Da Ƴan Koransa –  Dele Momodu

July 3, 2025
Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

Han Zheng Ya Halarci Bikin Bude Dandalin Tattaunawa Kan Zaman Lafiya Na Duniya Karo Na 13

July 3, 2025
Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

Kuriar Jin Raayoyin Jamaa Na CGTN Ta Shaida Yadda Akasarin Jamaa Ke Ganin Baiken Kudurin Dokar Bunkasa Amurka

July 3, 2025
Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

Zamfara Babban Wuri Ne Na Aikin Noma Mai Amfani Da Hasken Rana – Gwamna Lawal

July 3, 2025
CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya

CMG Za Ta Gabatar Da Labaran Sinawa Na Yakin Kin Harin Sojojin Japan Bisa Fifikonta Na Yayata Labarai A Duniya

July 3, 2025
Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

Kotu Ta Yanke Wa Ɗan TikTok Tsulange Hukuncin Ɗauri Kan Shigar Zubar Da Mutunci

July 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.