• English
  • Business News
Tuesday, August 26, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NAFDAC Ta Fayyace Sakamakon Bincikenta Kan Taliyar Indomie

by Sulaiman
2 years ago
in Labarai
0
NAFDAC Ta Fayyace Sakamakon Bincikenta Kan Taliyar Indomie
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Labarai Masu Nasaba

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

Darakta Janar ta Hukumar Kula da Abinci da Magunguna ta Kasa (NAFDAC), Farfesa Mojisola Adeyeye, ta bayyana cewa gwajin kimiyyar da hukumar ta gudanar ya tabbatar da cewa taliyar Indomie lafiyarta kalau babu wani hadari a tare da ita.

A lokacin da take jawabi ga manema labarai, Adeyeye ta jaddada ingancin lafiyar Indomie da ake samarwa a cikin gida Nijeriya. Ta tabbatar wa masu saye da sayar da kayayyakin abincin cewa, taliyar da aka janye ta “mai dandanon kaza ta musamman (Special Chicken Flabour)” a Taiwan da Malaysia ba ta tsallako cikin Nijeriya ba, don haka ba a sayar da ita ko’ina a kasuwannin Nijeriya.

  • Abin Da Ya Kamata A Sani Game Da Barkewar Cutar Diptheria A Abuja
  • Ina Son Kara Aure, Ko Me Yake Kawo Matsaloli Tsakanin Kishiyoyi Da Yadda Za A Magance?

A cewar shugabar ta NAFDAC, “An gwada jimillar samfura guda 114 na taliyar da abubuwan da suka hada da sinadarai daban-daban na ingancin abinci. Mun samu samfurori 58 daga masana’antu daban-daban, samfurori 24 daga kasuwannin Legas, samfurori 16 daga Abuja, da kuma samfurori 16 daga Kano. An yi amfani da hanyoyi guda biyu don gwada samfurori daban-daban da aka tattara, su ne: dabarar nazari da ake amfani da ita don rarrabewa da gano abubuwan da ke tattare da sinadarai, da kuma dabarar nazarin da ake gano abubuwan sinadarai ta hanyar tantancewa.”

Da take bayani kan jinkirin da aka samu wajen fitar da sakamakon binciken, Adeyeye ta bayyana cewa, hakan ta faru ne saboda wasu kayan aiki da fasahar zamanin da aka yi amfani da su dole sai da aka shigo da su cikin kasar nan daga waje, sannan hukumar ta NAFDAC ta natsu ce ta yi aikin a kimiyance.

Domin nuna gamsuwa da kuma amincewarta da sakamakon gwajin da aka yi, shugabar ta NAFDAC ta cinye taliyar indomie da aka girka aka zuba mata a lokacin taron, inda abokan aikinta suka bukaci su ma ta raba musu ko da taba-ka-lashe.

Manajan Sadarwa da Shirya Bukukuwa na Kamfanin Dufil Prima Foods Plc, Temitope Ashiwaju ya bayyana kudurin kamfanin na kiyaye ka’idojin tabbatar da inganci na kasa da kuma duniya tare da tallafa wa bunkasa tattalin arzikin cikin gida.

Da yake karin haske daga ofishin Dufil Prima Foods da ke Legas, Ashiwaju ya ce, “Ana samar da nau’ikan taliyar Indomie ne a Nijeriya kuma an shafe akalla shekaru talatin ana sarrafa taliyar a kasar. Dupil Prima ya kara fadada ayyukan da yake yi a cikin gida wanda hakan zai bunkasa yawan kayan da yake sarrafawa da daukar ma’aikata domin cimma bukatun kasuwa da zarce ka’idojin da aka gindaya na inganci a gida da waje.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: BincikeIndomieNAFDAC
ShareTweetSendShare
Previous Post

Bidiyon Dala: Kotu Ta Dakatar Da Gwamnatin Kano Da ‘Ƴansanda Da DSS Kan Kama Ganduje

Next Post

An Maka Shi Gaban Kotu Bisa Satar Karafan Naira Miliyan 5

Related

Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15
Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

7 hours ago
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna
Labarai

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

8 hours ago
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu
Manyan Labarai

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

9 hours ago
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya
Labarai

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

10 hours ago
Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF
Manyan Labarai

Rashin Tsaro: Ana Ƙoƙarin Ganin Ƙarshen Haƙurin Arewa – ACF

11 hours ago
Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike
Manyan Labarai

Gwamnatin Sokoto Ta Ƙaryata Rahoton NBS Kan Talauci, Ta Ƙaddamar Da Sabon Bincike

14 hours ago
Next Post
An Daure Matashi Shekara 1 Kan Satar Janareta A Abuja

An Maka Shi Gaban Kotu Bisa Satar Karafan Naira Miliyan 5

LABARAI MASU NASABA

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

An Yi Bikin Mu’ammalar Al’Adu Na SCO Na 2025 A Beijing

August 25, 2025
Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

Kuri’ar Jin Ra’ayin Jama’a Ta CGTN: Sin Ta Yi Rawar Gani A Fannin Bunkasa SCO

August 25, 2025
CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

CGTN Poll: Ba Da Kariya Shi Ne Tuna Baya—-Shekaru 80 Bayan Yakin Duniya Na II

August 25, 2025
Gwamnatin Tarayya Ta Yi Hasashen Ambaliyar Ruwa A Jihohin Arewa 15

Gwamnatin Tarayya Ta Sake Gargadin Jihohin Arewa 9 Kan Afkuwar Ambaliya 

August 25, 2025
Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 3 Da Kubutar Da Mutum 16 Da Aka Sace A Kaduna

ECOWAS Za Ta Kaddamar Da Rundunar Yaki Da Ta’addanci Mai Jami’ai 260,000

August 25, 2025
Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

Za A Watsa Shirin “Sha’awar Xi Jinping Ga Al’adu” a Manyan Kafofin Watsa Labarai Na Kasashen SCO

August 25, 2025
Mauludi: Gwamnatin Kano Ta Sake Ɗage Ranar Komawa Makarantu

Zargin Babban Hadimin Gwamnan Kano Ya Karkatar Da Kuɗaɗen Jama’a Ba Gaskiya Ba Ne

August 25, 2025
Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

Wani Rahoton Kasar Sin Ya Kalubalanci Halaccin Ayyukan Amurka Bisa Dogaro Da “’Yancin Zirga-zirga”

August 25, 2025
Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

Burkina Faso Da Mali Sun Yi Watsi Da Taron Sojojin Afirka A Nijeriya

August 25, 2025
Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

Beijing Zai Bunkasa Amfani Da Fasahohin Zamani A Wuraren Adana Kayan Tarihi

August 25, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.