• English
  • Business News
Wednesday, June 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Najeriya Ta Yi Imanin Shawarar BRI Za Ta Inganta Ci Gaban Kasashen Afirka

by CGTN Hausa
2 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Najeriya Ta Yi Imanin Shawarar BRI Za Ta Inganta Ci Gaban Kasashen Afirka
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A halin yanzu, ana gudanar da taron dandalin tattaunawar hadin gwiwar kasa da kasa kan raya shawarar “ziri daya da hanya daya” karo na 3, kuma kafin shirya wannan muhimmin taro, wakiliyarmu ta zanta da wasu manyan jami’an gwamnatin Najeriya a birnin Abuja, ciki har da ministan harkokin wajen kasar Yusuf Tuggar, da kakakin majalisar wakilan kasar Abbas Tajudeen.

A zantawa da ministan wajen Najeriya Yusuf Tuggar, ya bayyana cewa, wannan taron yana da muhimmanci kwarai, kuma zai kawo sabon ci gaba ga Najeriya. A cewarsa gwamnatin Najeriya na mutunta dangantakarta da kasar Sin. A cikin ‘yan shekarun nan, kasashen biyu sun ci gaba da yin hadin gwiwa, tare da samun sakamako mai inganci. Najeriya ta yi imani cewa, shawarar “ziri daya da hanya daya” da Sin ta gabatar za ta inganta ci gaban kasashen Afirka, tana kuma fatan hada kai da Sin wajen gina al’umma mai makomar bai daya ga bil’adama.

  • Kasashen Yamma Suna Tsotse Jinin ‘Yan Afirka Yayin Da Kasar Sin Ke Kawo Bege

Tuggar ya kara da cewa, tun lokacin da kasashen Sin da Najeriya suka kulla dangantakar diplomassiya tsakaninsu, kasashen biyu suke gudanar da hadin gwiwa mai inganci a fannoni daban daban, tare da samun babban sakamako a fannonin amincewar siyasa da hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya. Ya jaddada cewa, shawarar “ziri daya da hanya daya” tana da babbar ma’ana ga kyautata zaman rayuwar Najeriya da inganta ci gaban tattalin arzikin kasar, kana dandali na da kyau a fannin hadin gwiwar gina manyan kayayyakin more rayuwa da karfafa hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka.

Shawara

Haka kuma, a nasa bangare, kakakin majalisar wakilan kasar Abbas Tajudeen, ya bayyana cewa, kasashen Najeriya da Sin dukkansu kasashe ne masu tasowa dake da kamanceceniya, kuma suna tunkarar ayyukan raya kasa da dama. Yana mai cewa, shawarar ta kawo ci gaba masu amfani da yawa ga Najeriya, kuma an sami manyan nasarori a hadin gwiwar kasashen a fannoni daban daban.

Labarai Masu Nasaba

Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba

Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

Abbas ya ce, Sin ta kau da matsaloli da yawa a kan hanyar samun bunkasuwa a fannonin siyasa da tattalin arziki da al’adu da sauransu, musamman a fannin kau da matsanancin talauci, aikin da Sin ta yi ya kafa wata sabuwar hanya ga kasashe masu tasowa na duniya. Kuma a bisa tallafin Sin, an kyautata manyan gine-ginen more rayuwa na Najeriya, wanda ya kara kuzari ga ci gban tattalin arzikin Najeriya, don haka Najeriya tana godiya matuka da wannan karamci.

Ban da wannan kuma, game da maganganu kan wai batun “tarkon bashi” da wasu kafofin watsa labarai na kasashen yamma suke yi kuwa, Abbas ya ce wanann ba gaskiya ba ne, bangaren Sin ya baiwa Najeriya bashin da ake bukata a fannin hadin gwiwar gina manyan kayayyakin more rayuwa, kuma bashin da kasar Sin ta baiwa Najeriya mai karancin kudin ruwa ne da kuma tsawon lokacin biya. Ya kara da cewa, Najeriya za ta tsaya tsayin daka kan shiga cikin aikin raya shawarar “ziri daya da hanya daya”, don samar da makoma mai kyau ga al’ummun kasar. (Amina Xu, Safiyah Ma)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AfirkaNajeriyaShawarar ziri dayaSin
ShareTweetSendShare
Previous Post

Mahara Sun Hallaka ‘Yan Sintiri 9 A Bauchi

Next Post

Kotu Ta Daure Dillalin Tabar Wiwi Shekara 10 A Kano

Related

Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba
Daga Birnin Sin

Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba

24 minutes ago
Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana
Daga Birnin Sin

Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

2 hours ago
Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 
Daga Birnin Sin

Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

4 hours ago
Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin
Daga Birnin Sin

Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

5 hours ago
Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya
Daga Birnin Sin

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

23 hours ago
Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva
Daga Birnin Sin

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

24 hours ago
Next Post
PDP A Kano: Kotu Ta Sanya Ranar Yanke Hukuncin Shari’ar Sadiq Wali Da Abacha

Kotu Ta Daure Dillalin Tabar Wiwi Shekara 10 A Kano

LABARAI MASU NASABA

Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba

Sin: Batun Taiwan Sha’ani Ne Na Cikin Gidan Kasar Sin Kuma Bai Yi Kama Da Rikicin Ukraine Ba

June 4, 2025
Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

June 4, 2025
‘Yansanda Sun Ceto Mutum 21 Da Aka Sace, Sun Kwato N4.8m Kuɗin Fansa

‘Yansanda Sun Kama ‘Yan Ƙungiyar Asiri 4, Sun Ƙwato Makamai A Filato

June 4, 2025
Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

Darajar Hajojin Da Aka Fitar Waje Daga Birnin Shanghai Ta Kai Yuan Biliyan 629 Cikin Watanni Hudu Na Farkon Shekarar Bana

June 4, 2025
Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

Babban Sauyi Da Ba a Taba Ganin Irinsa Ba a Karni Guda: Alkiblar Da Sin Take Bi Wajen Samun Bunkasuwa 

June 4, 2025
‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

‘Yansanda Sun Kama Mutane 2 Da Makamai Masu Yawa A Jihar Nasarawa

June 4, 2025
Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

Wang Yi Ya Gana Da Sabon Jakadan Amurka A Sin

June 4, 2025
Garkuwa: Sarkin Gobir Ya Bukaci Agajin Gaggawa Daga Gwamnatin Sakkwato

Mutum 7 Sun Rasu Sakamakon Kifewar Kwale-kwale A Sakkwato 

June 4, 2025
Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

Sabon Shugaban Koriya Ta Kudu Ya Yi Alkawarin Sulhu Da Takwaransa Na Arewa

June 4, 2025
DSS

DSS Da Sojoji Sun Kashe ‘Yan Bindiga 45 A Neja

June 4, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.