• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Najeriya Ta Yi Imanin Shawarar BRI Za Ta Inganta Ci Gaban Kasashen Afirka

by CGTN Hausa
2 years ago
Shawara

A halin yanzu, ana gudanar da taron dandalin tattaunawar hadin gwiwar kasa da kasa kan raya shawarar “ziri daya da hanya daya” karo na 3, kuma kafin shirya wannan muhimmin taro, wakiliyarmu ta zanta da wasu manyan jami’an gwamnatin Najeriya a birnin Abuja, ciki har da ministan harkokin wajen kasar Yusuf Tuggar, da kakakin majalisar wakilan kasar Abbas Tajudeen.

A zantawa da ministan wajen Najeriya Yusuf Tuggar, ya bayyana cewa, wannan taron yana da muhimmanci kwarai, kuma zai kawo sabon ci gaba ga Najeriya. A cewarsa gwamnatin Najeriya na mutunta dangantakarta da kasar Sin. A cikin ‘yan shekarun nan, kasashen biyu sun ci gaba da yin hadin gwiwa, tare da samun sakamako mai inganci. Najeriya ta yi imani cewa, shawarar “ziri daya da hanya daya” da Sin ta gabatar za ta inganta ci gaban kasashen Afirka, tana kuma fatan hada kai da Sin wajen gina al’umma mai makomar bai daya ga bil’adama.

  • Kasashen Yamma Suna Tsotse Jinin ‘Yan Afirka Yayin Da Kasar Sin Ke Kawo Bege

Tuggar ya kara da cewa, tun lokacin da kasashen Sin da Najeriya suka kulla dangantakar diplomassiya tsakaninsu, kasashen biyu suke gudanar da hadin gwiwa mai inganci a fannoni daban daban, tare da samun babban sakamako a fannonin amincewar siyasa da hadin gwiwar tattalin arziki da cinikayya. Ya jaddada cewa, shawarar “ziri daya da hanya daya” tana da babbar ma’ana ga kyautata zaman rayuwar Najeriya da inganta ci gaban tattalin arzikin kasar, kana dandali na da kyau a fannin hadin gwiwar gina manyan kayayyakin more rayuwa da karfafa hadin gwiwar Sin da kasashen Afirka.

Shawara

Haka kuma, a nasa bangare, kakakin majalisar wakilan kasar Abbas Tajudeen, ya bayyana cewa, kasashen Najeriya da Sin dukkansu kasashe ne masu tasowa dake da kamanceceniya, kuma suna tunkarar ayyukan raya kasa da dama. Yana mai cewa, shawarar ta kawo ci gaba masu amfani da yawa ga Najeriya, kuma an sami manyan nasarori a hadin gwiwar kasashen a fannoni daban daban.

LABARAI MASU NASABA

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Abbas ya ce, Sin ta kau da matsaloli da yawa a kan hanyar samun bunkasuwa a fannonin siyasa da tattalin arziki da al’adu da sauransu, musamman a fannin kau da matsanancin talauci, aikin da Sin ta yi ya kafa wata sabuwar hanya ga kasashe masu tasowa na duniya. Kuma a bisa tallafin Sin, an kyautata manyan gine-ginen more rayuwa na Najeriya, wanda ya kara kuzari ga ci gban tattalin arzikin Najeriya, don haka Najeriya tana godiya matuka da wannan karamci.

Ban da wannan kuma, game da maganganu kan wai batun “tarkon bashi” da wasu kafofin watsa labarai na kasashen yamma suke yi kuwa, Abbas ya ce wanann ba gaskiya ba ne, bangaren Sin ya baiwa Najeriya bashin da ake bukata a fannin hadin gwiwar gina manyan kayayyakin more rayuwa, kuma bashin da kasar Sin ta baiwa Najeriya mai karancin kudin ruwa ne da kuma tsawon lokacin biya. Ya kara da cewa, Najeriya za ta tsaya tsayin daka kan shiga cikin aikin raya shawarar “ziri daya da hanya daya”, don samar da makoma mai kyau ga al’ummun kasar. (Amina Xu, Safiyah Ma)

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka
Daga Birnin Sin

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa
Daga Birnin Sin

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace
Daga Birnin Sin

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Next Post
PDP A Kano: Kotu Ta Sanya Ranar Yanke Hukuncin Shari’ar Sadiq Wali Da Abacha

Kotu Ta Daure Dillalin Tabar Wiwi Shekara 10 A Kano

LABARAI MASU NASABA

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Ta Lashe Zaɓe, Duk Da Rikicin Da Ya Mamaye Ƙasar

November 1, 2025
An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

An Cafke Ma’aikatan Gidan Marayu Da Suka Sayar Da Yara 4 A Kan Naira Miliyan 3

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Yadda Gwamnatin Tarayya Ta Dakile Yaɗuwar Ɓarkewar Cutar Dabbobi A Jihar Jigawa

November 1, 2025
Jerin Gwarazan Taurarinmu

Jerin Gwarazan Taurarinmu

November 1, 2025
CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

CMG Ta Kammala Gabatar Da Rahoto Kan Ganawar Shugabannin Sin Da Amurka

October 31, 2025
Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

Ministan Wajen Malawi: Tsarin Ci Gaban Kasar Sin Ya Samar Da Darussa Ga Kasashe Masu Tasowa

October 31, 2025
Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

Xi: A Shirye Sin Take Ta Hada Hannu Da Canada Wajen Mayar Da Dangantakarsu Bisa Turbar Da Ta Dace

October 31, 2025
Donald Trump Zai Gurfana A Gaban Kotu Kan Tuhumar Da Ake Masa

Trump Ya Ayyana Nijeriya A Matsayin Ƙasar Da Rayuwar Kiristoci Ke Cikin Hatsari

October 31, 2025
Yadda Waliyin Amarya Ya Sace Sadaki A Kano

An Tsare Wani Mutum A Gidan Yari Kan Zargin Kashe Matarsa Saboda Ƙuli-Ƙuli A Kano

October 31, 2025
Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

Xi Ya Gabatar Da Rubutaccen Jawabi Ga Taron Kolin Shugabannin Masana’antu Da Kasuwanci Na APEC

October 31, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.