• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nan Ba Da Jimawa Ba Za Mu Fara Zawarcin Kwankwaso – PDP

by Sadiq
9 months ago
in Manyan Labarai
0
NNPP Za Ta Kwace Mulki A Jihar Imo – Kwankwaso
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar PDP ta bayyana cewa tana shirin tuntubar tsohon gwamnan Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, domin ya dawo cikin jam’iyyar don haɗa kai wajen yaƙar jam’iyyar APC a babban zaɓen 2027. 

Muƙaddashin shugaban PDP, Ambasada Umar Damagun ne, ya bayyana hakan a wata hira da BBC, inda ya ce PDP a shirye ta ke ta karɓi duk wani ɗan jam’iyyar da ya bar ta.

  • Shugaba Xi Ya Mika Sakon Ta’aziyyar Rasuwar Tsohon Shugaban Amurka Jimmy Carter
  • Conceicao Ya Zama Sabon Kocin AC Milan Bayan Raba Gari Da Fonseca

Damagun, ya mayar da martani kan kalaman Kwankwaso na cewa PDP ta mutu, inda ya ce wannan ra’ayi ne kawai kuma ba gaskiya ba ne.

Ya ce PDP ta riga ta tsallake manyan ƙalubale tun daga 2015, lokacin da wasu jiga-jigan jam’iyyar suka bar ta, amma hakan bai rusa ta ba.

Ya ƙara da cewa PDP ce kaɗai ke da ƙarfin cin zaɓe a Nijeriya idan aka cire jam’iyyar APC mai mulki.

Labarai Masu Nasaba

Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi

Damagun ya ce, “Duk da kalaman da Kwankwaso ya yi, muna da yaƙinin cewa PDP ce ta haife sa kuma ta gina siyasarsa, har ya kai inda yake yau.

“Muna fatan zai dawo domin mu haɗa kai mu fuskanci wannan azzalumar gwamnati.”

Hakazalika, Damagun ya bayyana cewa jam’iyyar PDP tana da tarihin karɓar duk wani ɗan jam’iyyar da ya bar ta kuma ya dawo daga baya.

“A PDP, ba ma rufe ƙofa ga wanda ya tafi. Lokacin da ya dawo, muna karɓarsa kuma muna ba shi dama kamar sauran mambobi,” in ji shi.

Muƙaddashin shugaban ya kuma yi kira ga Kwankwaso da ya sake tunani game da batun haɗin kai da PDP, yana mai cewa jam’iyyar ce ta fi kowace damawa ga ‘yan Nijeriya.

Ya ce idan PDP ta mutu kamar yadda Kwankwaso ya faɗa, babu yadda za a yi ta ci gaba da samun gwamnoni da sanatoci a Nijeriya.

Damagun ya kammala da cewa nan ba da jimawa ba za su tuntuɓi Kwankwaso don tattaunawa da shi kan yadda za su yi aiki tare domin ceto Nijeriya daga matsalolin da ke damunta a yanzu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCDamagumKwankwasoPDPZabeZawarci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ɓarayin Wutar Sola Sun Baƙunci Lahira Yayin Da Suke Tsaka Da Kwancewa

Next Post

Matatar Mai Ta Warri Ta Dawo Aiki Bayan Shafe Shekaru A Rufe

Related

Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL
Manyan Labarai

Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

2 hours ago
Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi
Manyan Labarai

Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi

3 hours ago
Gwamnatin Tarayya Ta Ɓullo Da Kwasakwasai 26 Na Kasuwanci Don Rage Yawan Masu Neman Aikin Gwamnati
Manyan Labarai

Gwamnatin Tarayya Ta Ɓullo Da Kwasakwasai 26 Na Kasuwanci Don Rage Yawan Masu Neman Aikin Gwamnati

19 hours ago
DSS Ta Gurfanar Da Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Kan Zargin Ta’addanci
Manyan Labarai

DSS Ta Gurfanar Da Shugabannin Ƙungiyar Ansaru Kan Zargin Ta’addanci

24 hours ago
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Manyan Labarai

Tinubu Ya Bayar Da Umarni Karya Farashin Kayan Abinci A Nijeriya

1 day ago
Mun Gano Famfo 5,570 Da Ake Amfani Da Su Wajen Satar Danyen Mai — NNPCL
Manyan Labarai

Mele Kyari Ya Bayyana A Ofishin EFCC Kan Zargin Badaƙalar Dala Biliyan 7.2

1 day ago
Next Post
Matatar Mai Ta Warri Ta Dawo Aiki Bayan Shafe Shekaru A Rufe

Matatar Mai Ta Warri Ta Dawo Aiki Bayan Shafe Shekaru A Rufe

LABARAI MASU NASABA

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

Ba Lallai Ne FIFA Ta Cirewa Afrika Ta Kudu Maki 3 Ba – Rayond Hack

September 12, 2025
Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro?

Gwamnonin Arewa Sun Amince Da Kafa Ƴansandan Jihohi: Ko Hakan Zai Yi Tasiri Ga Sha’anin Tsaro?

September 12, 2025
Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

Nijeriya Na Shirin Samun Jarin Dala Biliyan 60 A Fannin Gas – Shugaban NNPCL

September 12, 2025
Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi

Yadda Tinubu Ya Shawo Kan Gwamnonin Arewa Wajen Amincewa Da Kafa Ƴansandan Jihohi

September 12, 2025
Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

Rashin Wutar Lantarki: Masana Sun Nuna Damuwa Kan Asarar Dala Biliyan 29 Da Ƙananan Masana’antu Ke Yi

September 12, 2025
Buƙatar Daƙile Yawan Ɓacewar Mutane A Nijeriya

Buƙatar Daƙile Yawan Ɓacewar Mutane A Nijeriya

September 12, 2025
Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

Tattalin Arzikin Sin Babban Ginshiki Ne Na Karuwar Tattalin Arzikin Duniya

September 12, 2025
Duniya Za Ta Ci Karin Gajiya Daga Karfafuwar Hadin Gwiwar BRICS 

Duniya Za Ta Ci Karin Gajiya Daga Karfafuwar Hadin Gwiwar BRICS 

September 12, 2025
Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

Hasashen Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kaduna Ta Ƙaddamar Da Shirin Ko-ta-kwana

September 11, 2025
Sin Ta Kasance Kan Gaba A Yawan Hakkin Mallakar Fasaha A Bangaren Tattalin Arziki Na Dijital

Sin Ta Kasance Kan Gaba A Yawan Hakkin Mallakar Fasaha A Bangaren Tattalin Arziki Na Dijital

September 11, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.