• English
  • Business News
Saturday, November 1, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nan Ba Da Jimawa Ba Za Mu Fara Zawarcin Kwankwaso – PDP

by Sadiq
10 months ago
Kwankwaso

Jam’iyyar PDP ta bayyana cewa tana shirin tuntubar tsohon gwamnan Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, domin ya dawo cikin jam’iyyar don haɗa kai wajen yaƙar jam’iyyar APC a babban zaɓen 2027. 

Muƙaddashin shugaban PDP, Ambasada Umar Damagun ne, ya bayyana hakan a wata hira da BBC, inda ya ce PDP a shirye ta ke ta karɓi duk wani ɗan jam’iyyar da ya bar ta.

  • Shugaba Xi Ya Mika Sakon Ta’aziyyar Rasuwar Tsohon Shugaban Amurka Jimmy Carter
  • Conceicao Ya Zama Sabon Kocin AC Milan Bayan Raba Gari Da Fonseca

Damagun, ya mayar da martani kan kalaman Kwankwaso na cewa PDP ta mutu, inda ya ce wannan ra’ayi ne kawai kuma ba gaskiya ba ne.

Ya ce PDP ta riga ta tsallake manyan ƙalubale tun daga 2015, lokacin da wasu jiga-jigan jam’iyyar suka bar ta, amma hakan bai rusa ta ba.

Ya ƙara da cewa PDP ce kaɗai ke da ƙarfin cin zaɓe a Nijeriya idan aka cire jam’iyyar APC mai mulki.

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

Damagun ya ce, “Duk da kalaman da Kwankwaso ya yi, muna da yaƙinin cewa PDP ce ta haife sa kuma ta gina siyasarsa, har ya kai inda yake yau.

“Muna fatan zai dawo domin mu haɗa kai mu fuskanci wannan azzalumar gwamnati.”

Hakazalika, Damagun ya bayyana cewa jam’iyyar PDP tana da tarihin karɓar duk wani ɗan jam’iyyar da ya bar ta kuma ya dawo daga baya.

“A PDP, ba ma rufe ƙofa ga wanda ya tafi. Lokacin da ya dawo, muna karɓarsa kuma muna ba shi dama kamar sauran mambobi,” in ji shi.

Muƙaddashin shugaban ya kuma yi kira ga Kwankwaso da ya sake tunani game da batun haɗin kai da PDP, yana mai cewa jam’iyyar ce ta fi kowace damawa ga ‘yan Nijeriya.

Ya ce idan PDP ta mutu kamar yadda Kwankwaso ya faɗa, babu yadda za a yi ta ci gaba da samun gwamnoni da sanatoci a Nijeriya.

Damagun ya kammala da cewa nan ba da jimawa ba za su tuntuɓi Kwankwaso don tattaunawa da shi kan yadda za su yi aiki tare domin ceto Nijeriya daga matsalolin da ke damunta a yanzu.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima
Manyan Labarai

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori
Manyan Labarai

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

November 1, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna
Manyan Labarai

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Next Post
Matatar Mai Ta Warri Ta Dawo Aiki Bayan Shafe Shekaru A Rufe

Matatar Mai Ta Warri Ta Dawo Aiki Bayan Shafe Shekaru A Rufe

LABARAI MASU NASABA

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

Yadda Ƴan Mata Ke Kashe Kuɗaɗe Wajen Yi Wa Samarinsu Hidima

November 1, 2025
Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

Tinubu Ya Kaddamar Da Ayyuka Bakwai A Jami’ar Ilori

November 1, 2025
Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

Rikicin PDP Ya Ƙara Ta’azzara Yayin Da Ɓangarori Ke Dakatar Da Juna

November 1, 2025
Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

Sin: Katsalandan Cikin Harkokin Kamfani Da Netherlands Ta Yi Ya Kawo Tsaiko Ga Tsarin Masana’antu Da Samar Da Kayayyaki Na Duniya

November 1, 2025
An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

An Gudanar Da Taron Tattaunawa Na Duniya Kan Kirkire-Kirkire Da Bude Kofa Da Ci Gaba Na Bai Daya A Nijeriya

November 1, 2025
Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

Sabbin ‘Yan Saman Jannatin Kasar Sin Sun Shiga Tashar Sararin Samaniya Ta Kasar

November 1, 2025
Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

Xi Jinping Ya Tattauna Da Shugaban Koriya Ta Kudu Lee Jae-myung 

November 1, 2025
Musabbabin Hana Sule Lamido Fom Ɗin Takarar Shugabancin PDP

Babban Burina Zama Fitacciyar Jaruma A Duniya —Aisha Umar

November 1, 2025
Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

Xi: A Hada Kai Wajen Gina Al’ummar Bai Daya Ta Asiya-Pasifik

November 1, 2025
Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

Dalibin Jami’ar Jos Ya Kashe Abokinsa Ya Binne Gawar A Rami

November 1, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.