• English
  • Business News
Saturday, August 23, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nan Ba Da Jimawa Ba Za Mu Fara Zawarcin Kwankwaso – PDP

by Sadiq
8 months ago
in Manyan Labarai
0
NNPP Za Ta Kwace Mulki A Jihar Imo – Kwankwaso
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Jam’iyyar PDP ta bayyana cewa tana shirin tuntubar tsohon gwamnan Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, domin ya dawo cikin jam’iyyar don haɗa kai wajen yaƙar jam’iyyar APC a babban zaɓen 2027. 

Muƙaddashin shugaban PDP, Ambasada Umar Damagun ne, ya bayyana hakan a wata hira da BBC, inda ya ce PDP a shirye ta ke ta karɓi duk wani ɗan jam’iyyar da ya bar ta.

  • Shugaba Xi Ya Mika Sakon Ta’aziyyar Rasuwar Tsohon Shugaban Amurka Jimmy Carter
  • Conceicao Ya Zama Sabon Kocin AC Milan Bayan Raba Gari Da Fonseca

Damagun, ya mayar da martani kan kalaman Kwankwaso na cewa PDP ta mutu, inda ya ce wannan ra’ayi ne kawai kuma ba gaskiya ba ne.

Ya ce PDP ta riga ta tsallake manyan ƙalubale tun daga 2015, lokacin da wasu jiga-jigan jam’iyyar suka bar ta, amma hakan bai rusa ta ba.

Ya ƙara da cewa PDP ce kaɗai ke da ƙarfin cin zaɓe a Nijeriya idan aka cire jam’iyyar APC mai mulki.

Labarai Masu Nasaba

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

Damagun ya ce, “Duk da kalaman da Kwankwaso ya yi, muna da yaƙinin cewa PDP ce ta haife sa kuma ta gina siyasarsa, har ya kai inda yake yau.

“Muna fatan zai dawo domin mu haɗa kai mu fuskanci wannan azzalumar gwamnati.”

Hakazalika, Damagun ya bayyana cewa jam’iyyar PDP tana da tarihin karɓar duk wani ɗan jam’iyyar da ya bar ta kuma ya dawo daga baya.

“A PDP, ba ma rufe ƙofa ga wanda ya tafi. Lokacin da ya dawo, muna karɓarsa kuma muna ba shi dama kamar sauran mambobi,” in ji shi.

Muƙaddashin shugaban ya kuma yi kira ga Kwankwaso da ya sake tunani game da batun haɗin kai da PDP, yana mai cewa jam’iyyar ce ta fi kowace damawa ga ‘yan Nijeriya.

Ya ce idan PDP ta mutu kamar yadda Kwankwaso ya faɗa, babu yadda za a yi ta ci gaba da samun gwamnoni da sanatoci a Nijeriya.

Damagun ya kammala da cewa nan ba da jimawa ba za su tuntuɓi Kwankwaso don tattaunawa da shi kan yadda za su yi aiki tare domin ceto Nijeriya daga matsalolin da ke damunta a yanzu.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: APCDamagumKwankwasoPDPZabeZawarci
ShareTweetSendShare
Previous Post

Ɓarayin Wutar Sola Sun Baƙunci Lahira Yayin Da Suke Tsaka Da Kwancewa

Next Post

Matatar Mai Ta Warri Ta Dawo Aiki Bayan Shafe Shekaru A Rufe

Related

Mahara Sun Kai Hari Banki A Kogi
Manyan Labarai

’Yansanda Sun Kama Jagororin ‘Yan Bindiga A Abuja, Sun Ƙwato Makamai Da ₦7.4m

7 hours ago
An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja
Manyan Labarai

An San Masu Ɗaukar Nauyin Boko Haram, Kariya Ake Ba Su – Tsohon Babban Soja

14 hours ago
Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?
Manyan Labarai

Yawaitar Haduran Kwale-kwale A Arewa: Ina Mafita?

17 hours ago
Gwamnatin Tinubu “Kasuwa Ce Mara Amfani Ga Talaka” – PDP
Manyan Labarai

Bukatar Farfado Da Cibiyoyin Bincike Don Bunkasa Kasa

18 hours ago
EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo
Manyan Labarai

EFCC Na Neman Surukin Atiku Abubakar Ruwa A Jallo

1 day ago
Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu
Manyan Labarai

Sanata Wadada Ya Fice Daga Jam’iyyar SDP Bayan Ganawa Da Tinubu

1 day ago
Next Post
Matatar Mai Ta Warri Ta Dawo Aiki Bayan Shafe Shekaru A Rufe

Matatar Mai Ta Warri Ta Dawo Aiki Bayan Shafe Shekaru A Rufe

LABARAI MASU NASABA

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

Wajibi Ne Sassan Kasa Da Kasa Su Raya Ruhin Jin Kan Bil’adama

August 22, 2025
UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

UNICEF Na Neman Naira Biliyan 240 Don Ayyukan Agaji A Nijeriya

August 22, 2025
Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

Sin Ta Samu Karin Kamfanoni Kusan Miliyan 20 A Cikin Shirin Shekaru Biyar Karo Na 14

August 22, 2025
Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

Ɓarayin Waya Sun Hallaka Ɗalibin ATAP A Bauchi

August 22, 2025
JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

JAMB Ta Kaddamar Da Kwamitin Bincike Kan Satar Jarabawa

August 22, 2025
Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

Wadanda Suka Mutu A Wani Hadarin Ginin Gada A Sin Sun Karu Zuwa 12

August 22, 2025
Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

Raguwar Hauhawar Farashi: ‘Yan Nijeriya Da ‘Yan Kasuwa Ba Su Ga Saukin A Zahirance Ba

August 22, 2025
Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

Kamfanin Novo Nordisk Na Denmark Zai Ci Gaba Da Zuba Jari A Kasar Sin A Bana

August 22, 2025
Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

Xi Jinping Zai Halarci Taron Kolin SCO Na 2025

August 22, 2025
Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

Ruben Dias Ya Rattaba Hannu Kan Sabon Kwantiragi A Manchester City

August 22, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.