ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, September 9, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nan Ba Da Jimawa Ba Za Mu Fara Zawarcin Kwankwaso – PDP

by Sadiq
2 years ago
Kwankwaso

Jam’iyyar PDP ta bayyana cewa tana shirin tuntubar tsohon gwamnan Kano, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso, domin ya dawo cikin jam’iyyar don haɗa kai wajen yaƙar jam’iyyar APC a babban zaɓen 2027. 

Muƙaddashin shugaban PDP, Ambasada Umar Damagun ne, ya bayyana hakan a wata hira da BBC, inda ya ce PDP a shirye ta ke ta karɓi duk wani ɗan jam’iyyar da ya bar ta.

  • Shugaba Xi Ya Mika Sakon Ta’aziyyar Rasuwar Tsohon Shugaban Amurka Jimmy Carter
  • Conceicao Ya Zama Sabon Kocin AC Milan Bayan Raba Gari Da Fonseca

Damagun, ya mayar da martani kan kalaman Kwankwaso na cewa PDP ta mutu, inda ya ce wannan ra’ayi ne kawai kuma ba gaskiya ba ne.

ADVERTISEMENT

Ya ce PDP ta riga ta tsallake manyan ƙalubale tun daga 2015, lokacin da wasu jiga-jigan jam’iyyar suka bar ta, amma hakan bai rusa ta ba.

Ya ƙara da cewa PDP ce kaɗai ke da ƙarfin cin zaɓe a Nijeriya idan aka cire jam’iyyar APC mai mulki.

LABARAI MASU NASABA

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

Damagun ya ce, “Duk da kalaman da Kwankwaso ya yi, muna da yaƙinin cewa PDP ce ta haife sa kuma ta gina siyasarsa, har ya kai inda yake yau.

“Muna fatan zai dawo domin mu haɗa kai mu fuskanci wannan azzalumar gwamnati.”

Hakazalika, Damagun ya bayyana cewa jam’iyyar PDP tana da tarihin karɓar duk wani ɗan jam’iyyar da ya bar ta kuma ya dawo daga baya.

“A PDP, ba ma rufe ƙofa ga wanda ya tafi. Lokacin da ya dawo, muna karɓarsa kuma muna ba shi dama kamar sauran mambobi,” in ji shi.

Muƙaddashin shugaban ya kuma yi kira ga Kwankwaso da ya sake tunani game da batun haɗin kai da PDP, yana mai cewa jam’iyyar ce ta fi kowace damawa ga ‘yan Nijeriya.

Ya ce idan PDP ta mutu kamar yadda Kwankwaso ya faɗa, babu yadda za a yi ta ci gaba da samun gwamnoni da sanatoci a Nijeriya.

Damagun ya kammala da cewa nan ba da jimawa ba za su tuntuɓi Kwankwaso don tattaunawa da shi kan yadda za su yi aiki tare domin ceto Nijeriya daga matsalolin da ke damunta a yanzu.

MASU ALAKA

Sojoji
Manyan Labarai

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Ballon D'or
Manyan Labarai

Ballon d’Or: Messi, Yamal, Da Mane Na Cikin ‘Yan Wasa 30 Da Aka Zaɓo

September 8, 2026
Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue
Manyan Labarai

Ɓata-gari Sun Kai Wa Ayarin Peter Obi Hari A Benue

September 8, 2026
Next Post
Matatar Mai Ta Warri Ta Dawo Aiki Bayan Shafe Shekaru A Rufe

Matatar Mai Ta Warri Ta Dawo Aiki Bayan Shafe Shekaru A Rufe

LABARAI MASU NASABA

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

ASUU Ta Yi Barazanar Yajin Aiki A Jami’ar Jihar Sokoto

September 9, 2026
Taron PDP Na Ƙasa: Ɓangaren Wike Ya Kafa Sabon NWC A Abuja

PDP Ta Musanta Mara Wa APM Baya A Bauchi

September 9, 2026
Sojoji

Sojoji Sun Dakile Hare-Hare, Sun Ceto Mutane 12 A Zamfara

September 9, 2026
Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

Batun AI Zai Fi Daukar Hankali A Bikin Baje Kolin Fasahar Zamani Ta Duniya Karo Na 5

September 8, 2026
Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

Gwamna Radda Ya Samu Goyon Bayan APC A Katsina Gabanin Zaɓen 2027

September 8, 2026
Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

Cinikin Wajen Sin Ya Ci Gaba Da Samun Bunkasa Cikin Sauri A Watanni Takwas Na Farkon Bana

September 8, 2026
'Yan Bindiga

‘Yan Bindiga Sun Kashe 2, Sun Yi Garkuwa Da 26 A Kaduna

September 8, 2026
Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

Binciken CGTN Ya Nuna Gamsuwa Da Yadda Baje Kolin CIFTIS Ke Shaida Karfin Gwiwar Sin A Fannin Kara Fadada Bude Kofa Bisa Babban Matsayi

September 8, 2026
Yadda Taron Tattalin Arziki Da Zuba Jari Na Kwana Biyu Ya Gudana A Katsina

Gwamna Radda Ya Gabatar Da Kasafin N828.6bn Na 2027

September 8, 2026
Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

Sin Za Ta Yi Aiki Tare Da Sassa Daban Daban Domin Mayar Da Fasahar AI Wata Dama Ta Cin Gajiya Mai Dorewa

September 8, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.