ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Sunday, December 21, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nasara A Yaƙi Da ‘Yan Ta’adda: Tattalin Arziƙin Jihar Zamfara Na Ƙara Haɓaka – Gwamna Lawal 

by Sulaiman
9 months ago
Zamfara

Gwamnan Jihar Zamfara, Dauda Lawal ya tabbatar da cewa za a samu ƙaruwar kuɗaɗen shiga sakamakon ci gaban da aka samu a fannin tsaro a faɗin jihar.

 

A ranar Larabar nan ne gwamnan ya zagaya wurare da masana’antar haƙar ma’adinai a ƙananan hukumomin Anka da Maru.

ADVERTISEMENT
  • ‘Yan Aware Na Taiwan Za Su Fuskanci Karin Hukunci Matukar Ba Su Daina Ba
  • Mun Rage Tasirin ‘Yan Bindiga A Kebbi Da Zamfara – Sojoji

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan jihar, Sulaiman Bala Idris, ya fitar ta bayyana cewa ziyarar na da nufin gano ɗimbin albarkatun jihar Zamfara da kuma samar da ƙarin hanyoyin samun kuɗaɗen shiga.

 

LABARAI MASU NASABA

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

“A yau ne Gwamna Dauda Lawal ya fara rangaɗin wuraren haƙar ma’adanai da masana’antu, inda ya fara ziyarar aiki a wani kamfani mai zaman kansa na Comet Star Industry da ke Ƙaramar Hukumar Anka.

 

“Ma’aikatar, mallakin Prince James Uduji OON, tana sarrafa kusan tan 1,000 a kullum. Tana da cikakkun kayan aiki da sabbin fasahohin haƙar ma’adinai don tabbatar da gudanar da ayyuka masu inganci.

Zamfara

“Lokacin da ya je masana’antar, Gwamna Lawal ya zagaya wurare da dama, inda ya fara tun daga magudanar ruwa da zuwa duka sassan injina da kayan aiki.

 

“Gwamna Lawal ya kuma ziyarci wurare daban-daban a cikin masana’antar, ciki har da gidan wutar lantarki da ke samar da wutar lantarki ga ɗaukacin kamfanin, da ɗakin gwaje-gwajen da ake sarrafa kayayyakin.”

 

A jawabinsa jim kaɗan bayan kammala rangaɗin, Gwamna Lawal ya bayyana gamsuwarsa da ƙa’idojin masana’antar, inda ya bayyana cewa irin jarin da gwamnatin jihar ke nema kenan.

 

“Na ji daɗi a yau domin wannan ya nuna ƙarara cewa an samu nasara a fannin tsaro a jihar Zamfara, ina godiya ga sojoji da duk masu ruwa da tsaki da suke aiki tuƙuru domin samar da zaman lafiya.

 

“Bugu da ƙari, ana ci gaba da tattaunawa tsakanin Gwamnatin Tarayya, Gwamnatin Jiha, kamfanoni masu zaman kansu, da sauran al’umma don fahimtar kadarorinmu da kuma gano alfanun su, wannan jiha tana da albarkar ma’adanai masu inganci, idan har za mu iya gano amfani su, ina tabbatar muku cewa za mu inganta kuɗaɗen shiga da kuma bunƙasa jihar Zamfara cikin sauri.”

 

A Ƙaramar Hukumar Maru, Gwamna Dauda Lawal ya yi wa masu haƙar ma’adan alƙawarin cikakken goyon bayan gwamnati, matuƙar suna aiki yadda doka da ƙayyade

 

Gwamnan ya yi alƙawarin samar wa da ma’aikatan muhimman kayan aiki don kauce wa gurɓatar muhalli.

Zamfara

Ya ce, “Muna haɗin gwiwa da gwamnatin yarayya, kuma suna ɗaukar muhimman matakai don aiwatar da abubuwan da suka wajaba. Zan turo Kwamishinan muhalli ya zauna da kuma, ta yadda kowa zai iya yin rajista. Ta hanyar rajista ne kawai za mu iya taskace sahihan bayanai.

 

“Gwamnatin jiha za ta samar maku da tallafin da ya wajaba, wanda zai haɗa da samo maku mataƙaicin izinin aikin haƙar ma’adanan daga gwamnatin tarayya, amma dole sai kun kafa ƙungiyoyin taimakon kai da kai.”

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta
Manyan Labarai

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani
Manyan Labarai

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025
Next Post
Karin Haraji: Amurka Ta Debo Ruwan Dafa Kanta

Karin Haraji: Amurka Ta Debo Ruwan Dafa Kanta

LABARAI MASU NASABA

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

Akpabio, Ganduje, Ogundoyin Sun Halarci Naɗa Seyi Tinubu Sarauta

December 21, 2025
Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

Tashar Teku Ta Ciniki Mai ‘Yanci Ta Hainan Ta Bude Sabon Babin Hadin Gwiwar Sin Da Kasashen Afirka

December 21, 2025
Tinubu

Dambarwar Naɗa Muƙamai Da Soke Su A Gwamnatin Tinubu

December 21, 2025
Zaben Fidda Gwani A APC: Sanatocin Jigawa Sun Rasa Tikitin Komawa Majalisa

APC Za Ta Gudanar Da Babban Taronta Na Kasa A Watan Maris

December 21, 2025
Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

Mun Shirya Tsaf Domin Lashe Gasar AFCON Ta Bana – Bassey

December 21, 2025
Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

Sarakuna Na Da Rawar Takawa Wajen Kare Muhalli A Nijeriya – Ministan Muhalli

December 21, 2025
Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

Me Ya Sa Ake Fifita Ilimin Boko A Kan Na Addini?

December 21, 2025
Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

Yadda Itacen Dorawa Ke Warkar Da Cututtuka Daban-daban

December 21, 2025
‘Yansanda Sun Kama Ɗan Bindiga Da Kuɗin Fansa Naira Miliyan 5 A Delta

An Cafke Wani Mutum Da Ya Lakada Wa Dansa Duka Har Lahira A Edo

December 21, 2025
Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

Bambance-bambancenmu Shine Ƙarfinmu — Uba Sani

December 21, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.