• English
  • Business News
Wednesday, August 27, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nasarar Yaki Da Hanci A Kasar Sin

by CMG Hausa
3 years ago
in Daga Birnin Sin
0
Nasarar Yaki Da Hanci A Kasar Sin
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Yaki da cin hanci shi ne babban kudurin da shugabannin kasar Sin suka sa a gaba,musamman bayan babban taro karo na 18 na wakilan jam’iyyar kwaminis mai mulki a kasar da aka gudanar a shekarar 2012, inda suka zage dantse wajen yaki da cin hanci a bisa doron halaccin tsarin siyasa.

Gwamanti mai ci a yanzu karkashin jagorancin shugaba Xi Jinping duk da irin kalubalen da take fuskanta ta sami gagarumar nasara wajen fito da sabuwar dokar daukar hukunci mai tsanani ga duk wata harkar cin hanci da karbar rashawa a kasar.

  • Shugaban Zimbabwe Ya Jinjinawa Kasar Sin Bisa Kammala Sabon Ginin Majalisar Dokokin Kasar

A yunkurin kawo karshen cin hanci a kasar Sin, gwamnatin kasar ta yi nazari na tsanaki domin gano dalilai da kuma illar da cin hanci da rashawa suka yiwa kasar.

Irin matakin da kasar Sin ta dauka na kawo karshen cin hanci sun hada da kafa hukumomin yaki da cin hanci da rashawa tare da yin hukunci mai tsanani ga duk wanda aka samu da aikata laifin cin hanci.

Hakika a wannan mataki kwalliya ta biya kudin sabulu domin gwamnati da jam’iyyar Kwaminisanci mai mulki sun hada karfi wuri guda wajen yakar cin hanci da kuma wanzar da hukunci kan doron shari’a ta yadda aka sami tsabtatacciyar gwamnati wadda babu bara gurbi a cikinta.

Labarai Masu Nasaba

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Irin matakan da gwamnatin ta Xi Jinping ta dauka da zummar cika burinta na kakkabe rashawa su ne kafa babban kwamitin binciko laifin cin rashawa na kasar.

Wannan kwamiti na binciko laifin cin rashawa ya zamanto kan gaba wajen gano ayyukan rashawa a kasar, inda ya binciko laifukan cin hanci da rashawa da kuma hukunta wadanda ke da hannu a ciki sama da mutane miliyan hudu a kowane matakin mukami na gwamnati.

Abin sha’awa a nan shi ne wannan kwamiti na binciko aikita laifin rashawa yana gabatar da wani shiri na kashin kansa mai suna “ba gudu babu ja baya wajen kauda rashawa” wato “zero tolerance” a Turance. Manufar wannan shiri ita ce nunawa ’yan kasa irin nasarar da kwamitin yake samu na yaki da karbar shawara tare da fallasa duk wani hamshakin gwamnati da aka samu da aikata laifin cin rashawa komai girman mukaminsa.

A rahoton kwamitin na shekarar 2018 zuwa ta 2020, kwamitin ya bayyana cewa ya yi nasarar kamo ’yan kasar da suka tsere zuwa kasashen ketare kimanin 3848, haka kuma an sami nasarar dawo da kusan biliyan goma na kudin kasar da aka yi awon gaba da su.

A hannu guda hukumar ta dauki matakan kau da cin hanci a kasar ta hanyoyi da dama, kadan daga ciki su ne, na daya, gwamantin kasar Sin ta bijiro da shirin ilmantar da ma’aikatan gwamnati kan rikon amana da kishin kasa ta yadda cin hanci da rashawa ba zai sami gurbi a cikin aikin gwamnati ba.

A dai wannan gabar gwamnatin ta tsara jadawalin ilimi a manhajar manyan makarantu na jami’o’i, makarantun sakandare da kuma makarantun firamare.

Duk wadannan matakai an dauke su ne da zimmar fahimtar da ‘yan kasa illar cin hanci da rashawa da kuma yadda suke rugurguza manufofin gwamnati na kyautata rayuwar ‘yan kasa.

Babu shakka irin wannan matakai da kasar Sin ta dauka sun taimaka kwarai da gaske wajen manufofin gwamnati na samar da rayuwa mai inganci ga ‘yan kasa.

Abin alfahari ga kasar ta Sin a yau shi ne yadda kasar ta yi bikin fidda miliyoyin ‘ya’yanta daga kangin talauci da fatara gami da kuma inganta rayuwar mazauna yankunan karkara, inda aka samar musu mazauni na zamani mai dauke da kayan alatu na more rayuwa kamar a manyan birane na kasar ta Sin.

A karshe wannan mataki na kauda cin hanci da rashawa da gwamnatin kasar Sin ta dauka karkashin jagorancin shugaba Xi Jinping ya jawowa kasar ta Sin kima a idon sauran kasashen duniya, haka kuma irin ci gaban da kasar ta Sin ta samu a bangaren kimiyya da fasahar zamani ta zamanto gagara gasa a fagen kere-kere a duk fadin duniya. (Garba Shu’aibu Dakata)


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

INEC Ta Maye Sunan Mohammed Abacha Da Sadiq Wali A Matsayin Dan Takarar PDP A Kano

Next Post

Tinubu Da Gwamnonin Kudu Ba Su Halarci Taron Da Buhari Ya Yi Game Da APC Ba

Related

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?
Daga Birnin Sin

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

17 hours ago
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi
Daga Birnin Sin

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

18 hours ago
Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha
Daga Birnin Sin

Shugaban Kasar Sin Xi Jinping Ya Gana Da Shugaban Majalisar Dokokin Rasha

20 hours ago
Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi
Daga Birnin Sin

Sin Ta Bukaci Japan Ta Waiwayi Tarihin Kutsen Da Ta Yi

20 hours ago
Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya
Daga Birnin Sin

Xi Da Uwargidansa ​​Sun Gana Da Sarkin Cambodia Da Mahaifiyarsa Sarauniya

22 hours ago
Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC
Daga Birnin Sin

Sassou Nguesso: Muna Fatan Gaggauta Tabbatar Da Sakamakon Taron Beijing Na FOCAC

23 hours ago
Next Post
Tinubu Da Gwamnonin Kudu Ba Su Halarci Taron Da Buhari Ya Yi Game Da APC Ba

Tinubu Da Gwamnonin Kudu Ba Su Halarci Taron Da Buhari Ya Yi Game Da APC Ba

LABARAI MASU NASABA

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

Gwamnatin Imo Ta Amince Da N104,000 A Matsayin Sabon Mafi Ƙarancin Albashin Ma’aikata 

August 27, 2025
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

‘Yan Bindiga Sun Kashe Mutane 8 A Kaduna, Sun Jikkata Wasu

August 27, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

‘Yansanda Sun Ceto Mutum 5 Da Aka Sace A Jihar Kebbi

August 27, 2025
Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Ya Yi Hatsari, Ba A San Halin Da Fasinjoji Ke Ciki Ba

NRC Ta Dakatar Da Sufurin Jirgin Ƙasan Abuja-Kaduna Bayan Hatsarin Da Ya Yi 

August 27, 2025
PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

PDP Na Tattaunawa Da Obi Da Jonathan Kan Yi Mata Takarar Shugaban Ƙasa A 2027 – Moro

August 27, 2025
Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

Kwalara Ta Kashe Mutum 7 A Zamfara, Sama Da Mutum 200 Sun Kamu Da Cutar

August 27, 2025
Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

Gwamnati Ta Fara Aikin Gyara Na’urar Watsa Shirye-shirye Mai Gajeren Zango Ta Gidan Rediyon Muryar Nijeriya

August 26, 2025
Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

Shin Mummunan Halin Da Aka Shiga Yayin Yakin Duniya Na II Bai Isa Darasi Ba?

August 26, 2025
Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

Gwamna Buni Ya Kaddamar Da Dashen Bishiyoyi Na 2025

August 26, 2025
Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

Firaministan Kasar Sin Li Qiang Ya Taya Nestor Ntahontuye Murnar Zama Sabon Firaministan Kasar Burundi

August 26, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.