Kungiyar Womanifesto, wacce ke wakiltar sama da ƙungiyoyin kare haƙƙin mata 350, ta buƙaci gudanar da bincike kan zargin cin zarafin jima’i da Sanata Natasha Akpoti-Uduaghan ta yi wa Shugaban Majalisar Dattawa, Godswill Akpabio.
Ƙungiyar ta buƙaci Akpabio ya sauka daga muƙaminsa nan take, a gudanar da bincike kan zargin, a gudanar da zaman jin bahasi na jama’a a kwamitin ladabtarwa na majalisa, da kuma barin duk wasu batutuwan da ke kotu su ci gaba da bin ƙa’ida.
- Matar Akpabio Ta Maka Sanata Natasha Kotu, Ta Nemi Diyyar Naira Biliyan 350
- Zargin Neman Yin Lalata: Ina Da Kwararan Hujjoji Akan Akpabio – Natasha
Womanifesto ta bayyana cewa yawan mata a muƙaman yanke hukunci a Nijeriya yana da matuƙar ƙaranci, kuma cin zarafin mata na ƙara ƙamari. Ta ce wannan batu ba zai iya shuɗewa ba tare da ɗaukar mataki ba.
Dr. Abiola Akiyode-Afolabi, ɗaya daga cikin shugabannin ƙungiyar, ta ce majalisa na fuskantar gwajin yadda take mutunta kundin tsarin mulki. Ta ce dukkanin ‘yan majalisa suna wakiltar al’ummarsu kuma dole a basu mutunci da martaba, ciki har da mata.
Ƙungiyar ta jaddada cewa majalisa na kan gwaji a idon duniya kuma dole ne ta ɗauki matakin tabbatar da adalci. Ta buƙaci a tabbatar da kare haƙƙoƙin mata da ‘yan mata, tare da tabbatar da cewa majalisa ta zama abin misali wajen kare ‘yancin mata daga cin zarafi.
Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe
Shiga zaurenmu na WhatsApp