• English
  • Business News
Friday, September 12, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Na’urorin Kula Da Iyakokin Kasa Za Su Fara Aiki Ba Da Jimawa Ba – Ministan Cikin Gida

by Khalid Idris Doya
1 year ago
in Labarai
0
iyakokin kasa
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Gwamnatin tarayya ta ce dukkanin iyakokin kasar nan an jibge musu na’urorin sanya ido masu sarrafa kansu domin inganta tsaron kasar da za su fara aiki nan ba da jimawa ba.

Ministan kula da harkokin cikin gida, Dakta Olubunmi Tunji-Ojo, shi ne ya shaida hakan a cikin makon nan a lokacin duba aikin da ake yi na ginawa da zuba kayan aiki a cibiyar kula da ba da umarni na mashiga ta fasahar zamani a filayen jiragen sama da kuma cibiyoyin tattara bayanai na kan iyakoki wadanda suke cikin shalkwatar hukumar kula da shige da fice ta kasa (NIS).

  • Ministan Kudin Zimbabwe Ya Jinjinawa Gudummawar Masu Zuba Jari Daga Sin
  • Ma’aikatar Harkokin Wajen Sin Ta Kira Taron Manema Labarai Game Da Halartar Shugaba Xi Jinping Bikin Bude Taron Ministoci Na Dandalin Tattauna Hadin-Kan Sin Da Kasashen Larabawa

Ya nuna gamsuwarsa da yadda ake gudanar da aiki mai inganci kuma cikin hanzari, ya lura kan cewa aikin farko na sanya na’uorin sa ido a iyakoki za su kammalu a watan Oktoban 2024.

Ya sanar da cewa ginawa da sanya kayan aiki a cibiyar ba da umarnin da kula da ke NIS ya kammalu kaso dari bisa dari, wanda ana jiran kaddamar daga Shugaban kasa, Bola Ahmed Tinubu zai jagoranta. Ya kuma ce aikin sa ido kan iyakoki na zamani ya kai kaso 60 cikin dari na kammaluwa.

“Muna zaman jiran shugaban kasa ne domin kaddamarwa. TunI muka sanar da shugaban kasa kuma ina farin cikin sanar da ‘yan jarida cewa aikin an kammala shi 100 bisa 100.”

Labarai Masu Nasaba

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Tunji-Ojo ya kara da cewa tsarin sa ido kan iyakoki mai amfani da kansa na zamani zai taimaka wajen dakile aikata laifuka a iyakoki da kuma samun damar bibiyar iyakoki tun daga shalkwatar NIS kai tsaye.

Ministan ya jaddada cewa kula da tsaron iyakoki na da muhimmanci kuma na daga cikin muhimman abubuwan da Shugaban Tinubu ba zai yi sako-sako da su ba domin tabbatar da tsaro da kare ‘yan kasa.

Kwanturola janar na hukumar shige da fice, Kemi Nanna Nandap, ta bayyana cewa an horas da jami’ansu yadda za su tafiyar da sabbin na’urorin da ke aiki da kansa, inda ta ce a yanzu haka ma wasu jami’an na samun horo kan hakan.

Nandap ta kara da cewa al’ummomin da suke iyakokin kasar su ma an wayar musu da kai kan irin gudunmawar da ake fatan za su bayar domin cimma nasarorin da aka sanya a gaba ciki har da bayar da muhimman bayanan da suka dace ga NIS a duk lokacin da bukatar hakan.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Iyakokin NijeriyaNCSNIS
ShareTweetSendShare
Previous Post

Jihohin Arewa Za Su Ware Kaso 5 Na Kasafi Don Taimaka Wa ‘Yan Gudun Hijira

Next Post

NAHCON Ta Karyata Rahoton Bayar Da Abinci Mara Inganci Ga Alhazai A Makkah

Related

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya
Labarai

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

57 minutes ago
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido
Manyan Labarai

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

1 hour ago
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja
Manyan Labarai

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

3 hours ago
Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano
Manyan Labarai

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

6 hours ago
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata
Labarai

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

6 hours ago
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group
Rahotonni

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

7 hours ago
Next Post
nahcon

NAHCON Ta Karyata Rahoton Bayar Da Abinci Mara Inganci Ga Alhazai A Makkah

LABARAI MASU NASABA

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

Shugaban Ghana: Manufar Soke Biyan Harajin Kwastam Ta Kasar Sin Ta Ba Da Damammaki Ga Afirka

September 12, 2025
Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

Gwamna Lawal Ya Tallafa Wa Ƙananan ’Yan Kasuwa Da Sama Da Naira Biliyan Ɗaya

September 12, 2025
Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

Akpabio Da Abbas Sun Yi Gargaɗi Kan Ciwo Bashi Ba Tare Da Sa Ido

September 12, 2025
Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

Yawan Yarjejeniyar Zuba Jari Da Aka Kulla a CIFIT Ya Kai 1154

September 12, 2025
Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

Korafin Philippines Ya Tabbatar Da Halascin Matakan Da Sin Ke Dauka Na Kare Muhalli a Tsibirin Huangyan

September 12, 2025
‘Yan Bindiga Sun Sace Mutum 7 A Jihar Neja

‘Yan Bindiga Sun Harbi Fasinjoji 2 A Jihar Neja

September 12, 2025
Kasar Sin Daya Ce Daga Cikin Kasashen Duniya Da Aka Amince Da Su a Matsayin Mafi Zaman Lafya

Kasar Sin Daya Ce Daga Cikin Kasashen Duniya Da Aka Amince Da Su a Matsayin Mafi Zaman Lafya

September 12, 2025
Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

Gwamnan Abba Ya Gabatar Da Ƙudurin Haramta Auran Jinsi A Kano

September 12, 2025
Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Shirin RenewHER, Don Magance Mutuwar Mata

September 12, 2025
Ahlul Faidhati Mai Diwani Group

Yadda Ahlul Faidhati Mai Diwani Group Suka Yi Maulidin Cikar Annabi (SAW) Shekara 1,500 Da Haihuwa 

September 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.