ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Friday, November 14, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nazarin CGTN: Kasar Sin Na Bayar Da Gudunmuwa Wajen Warware Batun Nukiliyar Iran

by CGTN Hausa and Sulaiman
8 months ago
Cgtn

Kasar Sin ta karbi bakuncin wani taro da ya gudana tsakaninta da kasashen Rasha da Iran, jiya Alhamis a birnin Beijing, don gane da lalubo hanyoyin warware batun nukiliyar Iran.

Bisa wani nazari da kafar yada labarai ta CGTN ta gudanar tsakanin masu amfani da intanet a fadin duniya, wadanda suka bayar da amsa na ganin taron na Beijing a matsayin yunkuri mai ma’ana dake da nufin inganta samar da mafita a siyasance kan batun nukiliyar Iran, inda suka yabawa kasar Sin din game da kyakkyawar rawa da take takawa game da lamarin.

  • Kalaman Lai Chin-te Na Shan Suka A Fadin Taiwan
  • Yawan Cire Haraji Ya Sa Albashinmu Babu Albarka – SSANU

Kimanin shekaru 10 da suka wuce, Iran da Amurka da Rasha da Sin da Birtaniya da Faransa da Jamus, suka cimma yarjejeniyar nukiliyar Iran. Sai dai daga baya, Amurka ta yi gaban kanta wajen janyewa daga yarjejeniyar a shekarar 2018, tare da sake kakaba takunkumai da matsawa Iran, lamarin da ya sake haifar da shakku don gane da batun nukiliyar.

ADVERTISEMENT

Cikin nazarin, kaso 87.6 bisa dari na masu bayar da amsa sun ce yarjejeniyar muhimmiyar nasara ce ta tafiyar da batutuwa masu muhimmanci ta hanyar tattaunawa, kuma ya kamata dukkan kasashe su yi biyayya da ita maimakon soke ta da sake wata sabuwa. Kaso 89.8 bisa dari na ganin aiwatar da ra’ayi na kashin kai wajen kakaba takunkumai da barazanar amfani da karfi da matsin lamba ba za su taimaka wajen warware batun ba. Kaso 89.5 bisa dari kuma sun yi amanna cewa tattaunawar siyasa da diplomasiyya bisa mutunta juna, ita ce kadai hanya kuma zabi mai ma’ana ta warware batun nukiliyar Iran. Wasu kaso 90.6 bisa dari kuma sun yi kira ga dukkan bangarorin da batun ya shafa su kauracewa daukar matakan da ka iya ta’azzara yanayin da ake ciki, kuma su samar da kyakkyawan yanayi da sharadin samar da mafita ta hanyar diplomasiyya.

Nazarin wanda dandamalin CGTN na harsunan Igilishi da Spaniyanci da Faransanci da Larabci da Rashanci suka wallafa, ya samu jimilar mutane 7,766 da suka kada kuri’a tare da bayyana ra’ayinsu cikin sa’o’i 24. (Fa’iza Mustapha)

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 
Daga Birnin Sin

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

November 13, 2025
Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia
Daga Birnin Sin

Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

November 13, 2025
Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana
Daga Birnin Sin

Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

November 13, 2025
Next Post
Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai

Fa’ida Daga Tafsirin Alƙur’ani Na Ibnu Juzai [8]

LABARAI MASU NASABA

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

Sin: Ya Zama Wajibi Japan Ta Janye Kalamanta Dangane Da Taiwan 

November 13, 2025
Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

Li Qiang Zai Halarci Tarukan SCO Da G20 Tare Da Ziyarar Aiki A Zambia

November 13, 2025
Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

Shugabar IOC: Gasar Wasanni Ta Kasar Sin Tana Da Babbar Ma’ana

November 13, 2025
Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

Ayyukan Kirkire-kirkire Na Kamfanonin Sin Na Kara Zama Babbar Kadara Ga Duniya

November 13, 2025
Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

Neman Gurbin Kofin Duniya: Nijeriya Ta Lallasa Gabon Da Ci 4

November 13, 2025
An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

An Gudanar Da Taro Mai Taken “Shugabancin Duniya: Ayyukan Matasa” A Johannesburg Dake Afirka Ta Kudu

November 13, 2025
Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

Xi Ya Bukaci Matasa Masanan Harkokin Sin Su Kasance Gada Tsakanin Sin Da Duniya

November 13, 2025
Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

Shugabannin Sin Da Comoros Sun Taya Juna Murnar Cika Shekaru 50 Da Kafa Alakar Diplomasiyya Tsakanin Kasashensu 

November 13, 2025
Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

Sanarwar Taron Ministocin Harkokin Waje Na Kungiyar G7 Ba Ta Da Tushe

November 13, 2025
NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

NDLEA Ta Ƙona Miyagun Ƙwayoyi Sama Da Kilo 52,000 A Kaduna

November 13, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.