• English
  • Business News
Thursday, May 15, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NDLEA Ta Kama Abubuwa Masu Fashewa 399, Da Haramtattun Kwayoyi A Neja

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Labarai
0
NDLEA Ta Kama Abubuwa Masu Fashewa 399, Da Haramtattun Kwayoyi A Neja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kalla bama-bamai 399 ne jami’an hukumar yaki da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa suka kwato daga hannun wani mai suna Asana Leke mai shekaru 39 a hanyar Mokwa-Jebba a ranar Alhamis, 7 ga watan Satumba.

Wanda ake zargin, ya ce an mika masa bamabaman ne a wani wurin shakatawa da ke Ibadan a Jihar Oyo, domin a kai wa wani a Kaduna, tare da baje kolin, an mika shi ga hukumomin soji a Jihar Neja.

  • Na’urorin Tattara Wutar Lantarki Na TCN A Birnin Kebbi Sun Fashe

Baya ga kokarin da ake yi na dakile yaduwar miyagun kwayoyi, hukumar ta NDLEA ta kuma ci gaba da yakin da take yi a makarantu, wuraren ibada, fadoji da sauran al’ummomin yankin da dai sauransu.

Mai Magana Da Yawun Hukumar NDLEA, Femi Babafemi ne ya bayyana hakan a wani sakon email da ya aika wa wakilinmu.

Ya kuma yi nuni da cewa, jami’an NDLEA sun kama wasu kayan laifi da aka boye a cikin tumatur, da kuma methamphetamine da aka boye a cikin tufafin da aka yi yunkurin fitar da su zuwa Kasar Dubai, Hadaddiyar Daular Larabawa.

Labarai Masu Nasaba

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

“Yayin da kwayar da aka boye cikin tumatur mai nauyin kilogiram 20 aka kama ta a ranar Juma’a, 8 ga watan Satumba, a shagon fitar da kayayyaki na SAHCO na filin jirgin saman Murtala Muhammed, Ikeja, a yayin jigilar an samu meth mai nauyin kilogiram 1.60 da aka kama a wani kamfanin jigilar kaya na Legas.

“Wani kaya mai nauyin gram 556 na Canadian Loud da aka aiko daga Kanada zuwa wani mutum mai suna Tunji Adebayo a Ikorodu, Legas, jami’an NDLEA na ofishin Darakta ayyuka da bincike na kasa da kasa, wadanda ke da alaka da kamfanonin jigilar kaya sun kama su.

A halin da ake ciki kuma, jami’an NDLEA sun kai samame unguwar wani kasurgumin dillalin kwaya da ke Akala, Mushin, Legas, Abdul Rauf, wanda ake kira ‘Na God’, inda aka kwato kilogiram 1,101 na Loud Ghana, tare da kama wasu mutum uku da ake nema ruwa a jallo.

A Jihar Ogun, wani bincike da aka gudanar ya kai ga cafke Yinka Azeez a Sabo Lafenwa, Abeokuta biyo bayan kama wata nau’in tabar wiwi mai nauyin kilogiram 41 daga hannun Titilayo Adetayo a mahadar Sagumu.

Har ila yau, akalla an kama wasu mutum biyu: Muhammad Aliyu mai shekaru 38 da Abdullahi Zakariyya mai shekaru 40 a hanyar Zaria zuwa Kano da Haye Arewa, Hotoro, Kano, da sama da kilogiram 426.5 na skunk.

Yayin da aka kama Onyeka Uzor, mai shekaru 25 a Idemili, Jihar Anambra, tare da skunk mai nauyin kilo giram 64.8 da Tramadol, wani wanda ake zargi, Destiny Irabor, an kama dauke da fiye da kilogiram 180 na opioids a cikin motarsa kirar Toyota Sienna.

A Kaduna, wasu mutum biyu; Ahmed Yusuf da Rilwan Nura, an kama su ne bisa laifin safarar tabar wiwi kulli 100 kilogiram 55 a hanyar Abuja.

A Jihar Edo, jami’an hukumar NDLEA sun kai farmaki dajin Ekudo dake Karamar Hukumar Onwude inda suka lalata gonakin tabar wiwi mai fadin hekta 4.236347.

Yayin da aka kama Onyeka Uzor, mai shekaru 25 a Idemili, Jihar Anambra, tare da kilo giram 64.8 na skunk da Tramadol, wani wanda ake zargi, Destiny Irabor, an kama shi dauke da fiye da kilogiram 180 na opioids a cikin motarsa kirar Toyota Sienna.

Hakazalika, jami’an ‘yansanda sun kai samame gidan wani Amuodu Egwehide, mai shekaru 40, da ke Iloje Okpuje, Karamar Hukumar Owan ta Yamma, inda suka kwato buhu 22 na skunk mai nauyin kilogiram 261.4, yayin da wata tsohuwa mai shekaru 60 Misis Eunice Egwehide, aka kama ta a garin a wannan rana tare da kilo giram 17 na tabar wiwi.

An kama wani da ake zargi mai suna Gapchiya Modu mai shekaru 26 da tabar wiwi mai nauyin kilogiram 60 a kan hanyar Kano zuwa Nguru, Jihar Yobe, yayin da a Jihar Imo kuma an kwato buhuna 200 na irin wannan wiwi mai nauyin kilogiram 57 daga Usim Orji mai shekaru 45 a hanyar Aba-Owerri.

Bayan sama da watanni biyu ana sa ido, jami’an NDLEA sun kama wani basarake da ake nema ruwa a jallo, Idoko Ifesinachi, mai shekaru 40, da laifin shigo da Loud mai nauyin kila giram 76.9 na Canada Loud da aka kama a cikin wani akwati mai lamba MSDU6686346 a tashar Port Harcourt, Onne. Jihar Ribers. An kama shi a maboyarsa da ke Legas aka kai shi Fatakwal.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: MakamaiNDLEA
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Hukumar Kula Da Hakkin Bil Adam Ta MDD Kan Batun Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Ta Japan

Next Post

Gwamnatin Kano Ta Kori Kwamishina Kan Kalaman Barazana Ga Alkalai

Related

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi
Labarai

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

55 minutes ago
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja
Labarai

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

4 hours ago
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?
Da ɗumi-ɗuminsa

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

5 hours ago
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 
Labarai

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

5 hours ago
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi
Labarai

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

6 hours ago
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara
Manyan Labarai

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

8 hours ago
Next Post
Gwamnatin Kano

Gwamnatin Kano Ta Kori Kwamishina Kan Kalaman Barazana Ga Alkalai

LABARAI MASU NASABA

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

An Bayar Da ₦95m Ga Iyalan Maharba Da Mutanen Da ‘Yan Ta’adda Suka Kashe A Bauchi

May 15, 2025
NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

NNPP Ta Tafka Asara, Ƴan Majalisa 2 Daga Kano Sun Koma APC

May 15, 2025
Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

Ya Kamata A Kori Ministan Ilimi – Aisha Yesufu

May 15, 2025
Lassa Da Shawara Sun Kashe Mutum 183 A Jihohi 36 Da Abuja

Lassa: Mutane 138 Sun Rasu, 717 Sun Kamu A Jihohi 18 – NCDC

May 15, 2025
Wa Suka Fi Cancanta A Nada Ministocin Tinubu?

Tinubu Ya Ƙaddamar Da Dakarun Da Za Suke Tsaron Daji Don Yaƙar ‘Yan Ta’adda

May 15, 2025
ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

ECOWAS Na Fuskantar Matsala Saboda Rashin Kyakkyawan Shugabanci – Bala Mohammed 

May 15, 2025
‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

‘Yansanda Sun Musanta Zargin Kai Wa ‘Yan Bindiga Abinci Ta Jirgin Sama A Kogi

May 15, 2025
Gabar ‘Yan Bindiga A Tsakaninsu Ta Kara Tsanani A Zamfara

’Yan Bindiga Sun Sace Mutane 200 A Mazaɓa Ta A Zamfara – Ɗan Majalisar Tarayya

May 15, 2025
An Yi Wa ‘Yar Shekara 18 Fyade Har Lahira A Taraba

’Yansanda Sun Cafke Mutane 9 Kan Kisan Jigon Jam’iyyar PDP A Adamawa

May 15, 2025
UTME

ASUU Ta Yi Barazanar Maka JAMB A Kotu Biyo Bayan Samun Mummunan Sakamako A UTME

May 14, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.