• English
  • Business News
Sunday, June 8, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NDLEA Ta Kama Abubuwa Masu Fashewa 399, Da Haramtattun Kwayoyi A Neja

by Rabi'u Ali Indabawa
2 years ago
in Labarai
0
NDLEA Ta Kama Abubuwa Masu Fashewa 399, Da Haramtattun Kwayoyi A Neja
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

A kalla bama-bamai 399 ne jami’an hukumar yaki da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa suka kwato daga hannun wani mai suna Asana Leke mai shekaru 39 a hanyar Mokwa-Jebba a ranar Alhamis, 7 ga watan Satumba.

Wanda ake zargin, ya ce an mika masa bamabaman ne a wani wurin shakatawa da ke Ibadan a Jihar Oyo, domin a kai wa wani a Kaduna, tare da baje kolin, an mika shi ga hukumomin soji a Jihar Neja.

  • Na’urorin Tattara Wutar Lantarki Na TCN A Birnin Kebbi Sun Fashe

Baya ga kokarin da ake yi na dakile yaduwar miyagun kwayoyi, hukumar ta NDLEA ta kuma ci gaba da yakin da take yi a makarantu, wuraren ibada, fadoji da sauran al’ummomin yankin da dai sauransu.

Mai Magana Da Yawun Hukumar NDLEA, Femi Babafemi ne ya bayyana hakan a wani sakon email da ya aika wa wakilinmu.

Ya kuma yi nuni da cewa, jami’an NDLEA sun kama wasu kayan laifi da aka boye a cikin tumatur, da kuma methamphetamine da aka boye a cikin tufafin da aka yi yunkurin fitar da su zuwa Kasar Dubai, Hadaddiyar Daular Larabawa.

Labarai Masu Nasaba

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

“Yayin da kwayar da aka boye cikin tumatur mai nauyin kilogiram 20 aka kama ta a ranar Juma’a, 8 ga watan Satumba, a shagon fitar da kayayyaki na SAHCO na filin jirgin saman Murtala Muhammed, Ikeja, a yayin jigilar an samu meth mai nauyin kilogiram 1.60 da aka kama a wani kamfanin jigilar kaya na Legas.

“Wani kaya mai nauyin gram 556 na Canadian Loud da aka aiko daga Kanada zuwa wani mutum mai suna Tunji Adebayo a Ikorodu, Legas, jami’an NDLEA na ofishin Darakta ayyuka da bincike na kasa da kasa, wadanda ke da alaka da kamfanonin jigilar kaya sun kama su.

A halin da ake ciki kuma, jami’an NDLEA sun kai samame unguwar wani kasurgumin dillalin kwaya da ke Akala, Mushin, Legas, Abdul Rauf, wanda ake kira ‘Na God’, inda aka kwato kilogiram 1,101 na Loud Ghana, tare da kama wasu mutum uku da ake nema ruwa a jallo.

A Jihar Ogun, wani bincike da aka gudanar ya kai ga cafke Yinka Azeez a Sabo Lafenwa, Abeokuta biyo bayan kama wata nau’in tabar wiwi mai nauyin kilogiram 41 daga hannun Titilayo Adetayo a mahadar Sagumu.

Har ila yau, akalla an kama wasu mutum biyu: Muhammad Aliyu mai shekaru 38 da Abdullahi Zakariyya mai shekaru 40 a hanyar Zaria zuwa Kano da Haye Arewa, Hotoro, Kano, da sama da kilogiram 426.5 na skunk.

Yayin da aka kama Onyeka Uzor, mai shekaru 25 a Idemili, Jihar Anambra, tare da skunk mai nauyin kilo giram 64.8 da Tramadol, wani wanda ake zargi, Destiny Irabor, an kama dauke da fiye da kilogiram 180 na opioids a cikin motarsa kirar Toyota Sienna.

A Kaduna, wasu mutum biyu; Ahmed Yusuf da Rilwan Nura, an kama su ne bisa laifin safarar tabar wiwi kulli 100 kilogiram 55 a hanyar Abuja.

A Jihar Edo, jami’an hukumar NDLEA sun kai farmaki dajin Ekudo dake Karamar Hukumar Onwude inda suka lalata gonakin tabar wiwi mai fadin hekta 4.236347.

Yayin da aka kama Onyeka Uzor, mai shekaru 25 a Idemili, Jihar Anambra, tare da kilo giram 64.8 na skunk da Tramadol, wani wanda ake zargi, Destiny Irabor, an kama shi dauke da fiye da kilogiram 180 na opioids a cikin motarsa kirar Toyota Sienna.

Hakazalika, jami’an ‘yansanda sun kai samame gidan wani Amuodu Egwehide, mai shekaru 40, da ke Iloje Okpuje, Karamar Hukumar Owan ta Yamma, inda suka kwato buhu 22 na skunk mai nauyin kilogiram 261.4, yayin da wata tsohuwa mai shekaru 60 Misis Eunice Egwehide, aka kama ta a garin a wannan rana tare da kilo giram 17 na tabar wiwi.

An kama wani da ake zargi mai suna Gapchiya Modu mai shekaru 26 da tabar wiwi mai nauyin kilogiram 60 a kan hanyar Kano zuwa Nguru, Jihar Yobe, yayin da a Jihar Imo kuma an kwato buhuna 200 na irin wannan wiwi mai nauyin kilogiram 57 daga Usim Orji mai shekaru 45 a hanyar Aba-Owerri.

Bayan sama da watanni biyu ana sa ido, jami’an NDLEA sun kama wani basarake da ake nema ruwa a jallo, Idoko Ifesinachi, mai shekaru 40, da laifin shigo da Loud mai nauyin kila giram 76.9 na Canada Loud da aka kama a cikin wani akwati mai lamba MSDU6686346 a tashar Port Harcourt, Onne. Jihar Ribers. An kama shi a maboyarsa da ke Legas aka kai shi Fatakwal.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: MakamaiNDLEA
ShareTweetSendShare
Previous Post

Kasar Sin Ta Yi Kira Ga Hukumar Kula Da Hakkin Bil Adam Ta MDD Kan Batun Zubar Da Ruwan Dagwalon Nukiliya Ta Japan

Next Post

Gwamnatin Kano Ta Kori Kwamishina Kan Kalaman Barazana Ga Alkalai

Related

‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi
Labarai

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

2 hours ago
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote
Labarai

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

3 hours ago
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne
Ra'ayi Riga

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

4 hours ago
Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno
Labarai

Sojojin Sama Sun Tarwatsa Maɓoyar Ƴan Ta’adda, Ya Daƙile Hari Ranar Idi A Borno

9 hours ago
NDLEA
Rahotonni

2027: An Yi Kira Ga Masu Mulki Da Su Rungumi Tafarkin Inganta Rayuwar Al’umma

9 hours ago
Tufka Da Warwarar INEC Kan Yiwuwar Zaben 2023
Labarai

Ana Ci Gaba Da Samun Rudani Yayin Da INEC Ta Jinkirta Rajistar Sabbin Jam’iyyu

10 hours ago
Next Post
Gwamnatin Kano

Gwamnatin Kano Ta Kori Kwamishina Kan Kalaman Barazana Ga Alkalai

LABARAI MASU NASABA

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

Tattaunawar Da Shugabannin Sin Da Amurka Suka Yi Ta Wayar Tarho Ta Ba Da Jagoranci Ga Dangantakar Dake Tsakanin Kasashen Biyu

June 7, 2025
‘Yansanda Sun Kashe Masu Garkuwa Da Mutane 8, Sun Kubutar Da Mutane 3 A Jihar Bauchi

An Kama Magidanci A Bauchi Bisa Zargin Lalata Da Agolarsa

June 7, 2025
Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

Dabarar Yaudara Ta Kasar Philippines Kan Batun Tekun Kudancin Sin Ta Fito Fili

June 7, 2025
Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

Wang Yi Ya Nanata Matsayin Taiwan Yayin Tattaunawa Da Takwaransa Na Faransa

June 7, 2025
Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

Hako Man Fetur: Jihar Neja Ta Nemi Hadin Gwiwar Kamfanin Dangote

June 7, 2025
Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

Aikin Ba Da Ilmi Ba Makamin Takarar Jam’iyyu Ba Ne

June 7, 2025
Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

Hukumar NPA Ta Bayar Da Kwangilar Aikin Ruwa Na Tashar Lekki

June 7, 2025
Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

Roland Busch: Kasar Sin Tana Daya Daga Cikin Kasuwanni Mafi Kuzari A Bangaren Kirkire-kirkire A Duniya

June 7, 2025
Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

Gwamnatin Tarayya Da Hadin Gwiwar IFAD Za Su Yi Wa Manoma Rijista Domin Tantance Su

June 7, 2025
Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

Dalibai Sama Da Miliyan 13 Ne Za Su Rubuta Jarrabawar Shiga Jami’a Ta Kasar Sin

June 7, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.