ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, July 16, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

NDLEA Ta Kama Abubuwa Masu Fashewa 399, Da Haramtattun Kwayoyi A Neja

by Rabi'u Ali Indabawa
3 years ago
NDLEA

A kalla bama-bamai 399 ne jami’an hukumar yaki da fataucin miyagun kwayoyi ta kasa suka kwato daga hannun wani mai suna Asana Leke mai shekaru 39 a hanyar Mokwa-Jebba a ranar Alhamis, 7 ga watan Satumba.

Wanda ake zargin, ya ce an mika masa bamabaman ne a wani wurin shakatawa da ke Ibadan a Jihar Oyo, domin a kai wa wani a Kaduna, tare da baje kolin, an mika shi ga hukumomin soji a Jihar Neja.

  • Na’urorin Tattara Wutar Lantarki Na TCN A Birnin Kebbi Sun Fashe

Baya ga kokarin da ake yi na dakile yaduwar miyagun kwayoyi, hukumar ta NDLEA ta kuma ci gaba da yakin da take yi a makarantu, wuraren ibada, fadoji da sauran al’ummomin yankin da dai sauransu.

ADVERTISEMENT

Mai Magana Da Yawun Hukumar NDLEA, Femi Babafemi ne ya bayyana hakan a wani sakon email da ya aika wa wakilinmu.

Ya kuma yi nuni da cewa, jami’an NDLEA sun kama wasu kayan laifi da aka boye a cikin tumatur, da kuma methamphetamine da aka boye a cikin tufafin da aka yi yunkurin fitar da su zuwa Kasar Dubai, Hadaddiyar Daular Larabawa.

LABARAI MASU NASABA

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

“Yayin da kwayar da aka boye cikin tumatur mai nauyin kilogiram 20 aka kama ta a ranar Juma’a, 8 ga watan Satumba, a shagon fitar da kayayyaki na SAHCO na filin jirgin saman Murtala Muhammed, Ikeja, a yayin jigilar an samu meth mai nauyin kilogiram 1.60 da aka kama a wani kamfanin jigilar kaya na Legas.

“Wani kaya mai nauyin gram 556 na Canadian Loud da aka aiko daga Kanada zuwa wani mutum mai suna Tunji Adebayo a Ikorodu, Legas, jami’an NDLEA na ofishin Darakta ayyuka da bincike na kasa da kasa, wadanda ke da alaka da kamfanonin jigilar kaya sun kama su.

A halin da ake ciki kuma, jami’an NDLEA sun kai samame unguwar wani kasurgumin dillalin kwaya da ke Akala, Mushin, Legas, Abdul Rauf, wanda ake kira ‘Na God’, inda aka kwato kilogiram 1,101 na Loud Ghana, tare da kama wasu mutum uku da ake nema ruwa a jallo.

A Jihar Ogun, wani bincike da aka gudanar ya kai ga cafke Yinka Azeez a Sabo Lafenwa, Abeokuta biyo bayan kama wata nau’in tabar wiwi mai nauyin kilogiram 41 daga hannun Titilayo Adetayo a mahadar Sagumu.

Har ila yau, akalla an kama wasu mutum biyu: Muhammad Aliyu mai shekaru 38 da Abdullahi Zakariyya mai shekaru 40 a hanyar Zaria zuwa Kano da Haye Arewa, Hotoro, Kano, da sama da kilogiram 426.5 na skunk.

Yayin da aka kama Onyeka Uzor, mai shekaru 25 a Idemili, Jihar Anambra, tare da skunk mai nauyin kilo giram 64.8 da Tramadol, wani wanda ake zargi, Destiny Irabor, an kama dauke da fiye da kilogiram 180 na opioids a cikin motarsa kirar Toyota Sienna.

A Kaduna, wasu mutum biyu; Ahmed Yusuf da Rilwan Nura, an kama su ne bisa laifin safarar tabar wiwi kulli 100 kilogiram 55 a hanyar Abuja.

A Jihar Edo, jami’an hukumar NDLEA sun kai farmaki dajin Ekudo dake Karamar Hukumar Onwude inda suka lalata gonakin tabar wiwi mai fadin hekta 4.236347.

Yayin da aka kama Onyeka Uzor, mai shekaru 25 a Idemili, Jihar Anambra, tare da kilo giram 64.8 na skunk da Tramadol, wani wanda ake zargi, Destiny Irabor, an kama shi dauke da fiye da kilogiram 180 na opioids a cikin motarsa kirar Toyota Sienna.

Hakazalika, jami’an ‘yansanda sun kai samame gidan wani Amuodu Egwehide, mai shekaru 40, da ke Iloje Okpuje, Karamar Hukumar Owan ta Yamma, inda suka kwato buhu 22 na skunk mai nauyin kilogiram 261.4, yayin da wata tsohuwa mai shekaru 60 Misis Eunice Egwehide, aka kama ta a garin a wannan rana tare da kilo giram 17 na tabar wiwi.

An kama wani da ake zargi mai suna Gapchiya Modu mai shekaru 26 da tabar wiwi mai nauyin kilogiram 60 a kan hanyar Kano zuwa Nguru, Jihar Yobe, yayin da a Jihar Imo kuma an kwato buhuna 200 na irin wannan wiwi mai nauyin kilogiram 57 daga Usim Orji mai shekaru 45 a hanyar Aba-Owerri.

Bayan sama da watanni biyu ana sa ido, jami’an NDLEA sun kama wani basarake da ake nema ruwa a jallo, Idoko Ifesinachi, mai shekaru 40, da laifin shigo da Loud mai nauyin kila giram 76.9 na Canada Loud da aka kama a cikin wani akwati mai lamba MSDU6686346 a tashar Port Harcourt, Onne. Jihar Ribers. An kama shi a maboyarsa da ke Legas aka kai shi Fatakwal.

NDLEA
Rabi'u Ali Indabawa
+ postsBio
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Wasu Fusatattun Mutane Sun Lakaɗa Wa Mutum Biyu Duka Har Lahira A Kaduna
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Mun Ɗauki Nauyin Karatun Masu Digiri Ta Hanyar Sayar Da Ƙosai Da Ƙuli-ƙuli —Wasu Ƴan Kasuwa
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Adadin Mutanen Da Tsananin Zafi Ya Kashe A Turai Ya Haura Dubu 1,300 —WHO
  • Rabi'u Ali Indabawa
    https://hausa.leadership.ng/author/rabiu-ali-indabawa/
    Pakistan Ta Kashe Mutum 36 A Hare-haren Da Ta Kai Kan Iyakarta Da Afghanistan

MASU ALAKA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje
Manyan Labarai

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya
Labarai

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Sabbin Ministoci
Labarai

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
Next Post
Gwamnatin Kano

Gwamnatin Kano Ta Kori Kwamishina Kan Kalaman Barazana Ga Alkalai

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Yana Zuba Kyawawan Ayyuka A Nijeriya – Ganduje

Ganduje Ya Buƙaci A Yi Siyasar Aƙida Domin Inganta Dimokuraɗiyya A Nijeriya

July 16, 2026
Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

Binciken CGTN: Amfanar Da Kowa Da Kowa Shi Ne Ainihin Alherin Da Fasahohin Kwaikwayon Tunanin Bil Adama Suka Kawo

July 15, 2026
Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

Sin Ta Yi Kira Da A Kafa Tsarin Jagorantar Muhimman Ma’adinai Ga Sauyawa Zuwa Amfani Da Makamashi Mai Tsafta

July 15, 2026
Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

Gwamna Dauda Lawal Zai Gabatar Da Jawabi A Taron Ƙasa Da Ƙasa Na Jami’ar FUE Zariya

July 15, 2026
Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

Neman Raba-Gari Da Sauran Kasashe Zai Kawo Mummuann Tasiri Ga Bangarorin Da Abin Ya Shafa

July 15, 2026
Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

Kevin Kelly: AI Na Iya Taimakawa Wajen Cimma Burin “Koyar Da Dalibai Da Kwazonsu”

July 15, 2026
Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

Gwamna Yusuf Ya Bai Wa Masu Kula Da Akwatinan Zaɓe Na APC Filaye 1,540 Da Tallafin Miliyan 100

July 15, 2026
Sabbin Ministoci

Rashin Tsaro: Majalisar Dattawa Ta Bukaci A Tura Ƙarin Sojoji da ’Yansanda Zuwa Benuwe

July 15, 2026
GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

GDPn Sin A Rabin Farko Na Shekarar 2026 Ya Karu Da Kashi 4.7% Idan Aka Kwatanta Da Na Kwatankwacin Lokacin Bara

July 15, 2026
‘Yansanda Sun Tsaurara Tsaron Iyakokin Kano Bayan Hare-haren ‘Yan Bindiga 

Atiku Ya Nuna Damuwa Kan Kasafin Naira Biliyan 6.44 Don Gasar Cin Kofin Duniya ta 2026

July 15, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.