• English
  • Business News
Tuesday, June 3, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Ndume Ya Bukaci Tinubu Ya Dauko Sojojin Haya Don Yakar ‘Yan Ta’adda

by Sadiq
8 months ago
in Labarai
0
Ndume Ya Bukaci Tinubu Ya Dauko Sojojin Haya Don Yakar ‘Yan Ta’adda
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Sanata mai wakiltar Borno ta Kudu a majalisar dattawa, Mohammed Ali Ndume, ya yi kira ga shugaban kasa Bola Tinubu da ya dauko sojojin haya don kawar ‘yan ta’addan Boko Haram a Jihar Borno.

Ndume, ya yaba da irin rawar da sojojin Nijeriya ke takawa, amma ya ce ba su da kayan aikin da za su yaki ‘yan tada kayar baya a yankin Arewa maso Gabas.

  • Saudiyya Ta Taya Nijeriya Murnar Cika Shekaru 64 Da Samun ‘Yancin Kai
  • Jirgin Ruwa Dauke Da ‘Yan Maulidi 200 Ya Nutse A Neja

Ya ce manyan kasashen duniya suna daukar sojojin haya don taimaka musu a yaki da ‘yan ta’adda.

Ya ce kasashe irin su Amurka da Rasha da Birtaniya da Faransa da dai sauransu, suna amfani da sojojin haya.

Sanatan ya bayyana cewa matakin zai kasance na wucin gadi.

Labarai Masu Nasaba

Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

Ndume, ya yi wannan kiran ne a kan yadda ‘yan ta’addan Boko Haram suka kashe wasu manoma shida a garin Ngoshe da ke karamar hukumar Gwoza ta Jihar Borno, tare da sace wasu biyar da suka hada da mata.

Ya koka da yadda hare-haren Boko Haram ke tilastawa manoma barin amfanin gonakinsu daidai lokacin da kasar ke fama da matsalar karancin abinci.

“A duk fadin duniya, gwamnatoci suna daukar hayar sojoji don shiga wasu wurare. Shugaba Bola Ahmed Tinubu na iya daukar wannan mataki na wucin gadi. Wadannan sojoji za su iya aiki da Civilian JTF kafada da kafada.

“Wadannan ‘yan kwangila za su zo da kayan aikinsu da kayan aikin soja. A cikin kankanin lokaci, za su kawar da ‘yan ta’addar Boko Haram.

“Ana kuma iya amfani da su wajen kawar da ‘yan fashin daji a Arewa maso Yamma.

“Gwamnatin Tarayya za ta iya daukar matasa aikin soja akalla miliyan daya. Hakan zai taimaka wajen yaki da ta’addanci.”

LEADERSHIP ta ruwaito cewa a baya-bayan nan, ‘yan ta’addan sun kashe kwamandan Civilian JTF, Jubril Dada Zarana.

Sabon harin na zuwa ne ‘yan makonni kadan bayan da ‘yan ta’addan suka kashe mutane da dama a ta hanyar amfani da bam.

 

 

 

 

 

 

 

 

 


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Boko HaramNdumeSojojin HayaTinubu
ShareTweetSendShare
Previous Post

Saudiyya Ta Taya Nijeriya Murnar Cika Shekaru 64 Da Samun ‘Yancin Kai

Next Post

Tinubu Zai Yi Balaguro Zuwa Birtaniya Na Mako 2

Related

Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 
Labarai

Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

1 hour ago
Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

2 hours ago
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus
Manyan Labarai

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus

5 hours ago
Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki
Manyan Labarai

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

8 hours ago
Jihohin Da Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Watan Yuni – NiMet
Manyan Labarai

Jihohin Da Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Watan Yuni – NiMet

9 hours ago
Gwamnatin Yobe Ta Rufe Makarantu Na Tsawon Kwanaki 10 Don Bikin Sallah Babba
Labarai

Gwamnatin Yobe Ta Rufe Makarantu Na Tsawon Kwanaki 10 Don Bikin Sallah Babba

10 hours ago
Next Post
Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Halartar Taron Sauyin Yanayi A Dubai

Tinubu Zai Yi Balaguro Zuwa Birtaniya Na Mako 2

LABARAI MASU NASABA

Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

June 3, 2025
An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

June 3, 2025
Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

June 3, 2025
Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

June 3, 2025
Darajar Hajojin Da Aka Yi Jigilarsu a Kasuwar Sin Daga Watan Janairu Zuwa Na Afrilu Ta Karu Da 5.6% 

Darajar Hajojin Da Aka Yi Jigilarsu a Kasuwar Sin Daga Watan Janairu Zuwa Na Afrilu Ta Karu Da 5.6% 

June 3, 2025
Sin Da Masar Sun Cimma Yarjejeniyar Kafa Cibiyar Harkokin Kasuwanci Ta Sabon Birnin Masar 

Sin Da Masar Sun Cimma Yarjejeniyar Kafa Cibiyar Harkokin Kasuwanci Ta Sabon Birnin Masar 

June 3, 2025
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus

June 3, 2025
Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

June 3, 2025
Jihohin Da Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Watan Yuni – NiMet

Jihohin Da Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Watan Yuni – NiMet

June 3, 2025
Gwamnatin Yobe Ta Rufe Makarantu Na Tsawon Kwanaki 10 Don Bikin Sallah Babba

Gwamnatin Yobe Ta Rufe Makarantu Na Tsawon Kwanaki 10 Don Bikin Sallah Babba

June 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.