• English
  • Business News
Friday, June 6, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Ba Ta Cikin Kasashe 10 Da Suka Fi Cin Bashi A Afirka – IMF

by Sadiq
5 months ago
in Manyan Labarai
0
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Asusun Lamuni na Duniya (IMF) ya fitar da rahoton jerin ƙasashen 10 da suka fi cin bashi a nahiyar Afirka, a lokacin da ƙasashen ke fama da matsanancin bashin da ya dabaibaye su.

Rahoton ya bayyana cewa, duk da ɗimbin bashin da Nijeriya ke karɓowa, ba ta cikin jerin ƙasashen da suka fi dogaro da lamuni daga IMF a Afirka.

  • Sin Na Matukar Adawa Da Binciken Da Amurka Ta Yi Kan Manufofin Sana’o’in Na’urorin Lantarki Na Kasar Sin
  • Sin Ta Sha Alwashin Karfafa Kare Muhallin Halittun Rawayen Kogi

Akwai ƙasashe 10 da suka yi fice wajen karɓar bashin IMF, galibi don cike gibin kasafin kuɗi da kuma magance matsalolin tattalin arziƙi.

Koyaushe, IMF na gindaya tsauraran sharuɗa, kamar cire tallafi, rage darajar kuɗaɗen ƙasa, da tsuke bakin aljihu kafin bayar da bashin.

Ga jerin ƙasashen 10 da suka fi cin bashi daga IMF:

Labarai Masu Nasaba

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

1. Masar – Ta karbi bashin dala biliyan 9.45, tana cikin matsanancin hali na tattalin arziƙi.

2. Kenya – Ta karɓi dala biliyan 3.02 don bunƙasa tattalin arziƙi da magance matsalolin cikin gida.

3. Angola – Ta dogara kan dala biliyan 2.99 don farfaɗo da tattalin arziƙinta.

4. Ghana – Ta karɓi dala biliyan 2.25, tana fama da karyewar darajar kuɗi.

5. Ivory Coast – Dala biliyan 2.19 don aiwatar da tsare-tsaren ci gaba.

6. Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Congo – Ta amshi dala biliyan 1.6 don magance matsalolin tattalin arziƙi duk da arziƙin albarkatun ƙasa.

7. Habasha – Ta karɓi dala biliyan 1.31 don magance matsalolin tattalin arziƙi.

8. Afirka ta Kudu – Dala biliyan 1.14 don tunkarar matsalolin cikin gida.

9. Kamaru – Ta ciyo dala biliyan 1.13.

10. Senegal – Ta karɓi dala biliyan 1.11 bayan karɓar tsauraran sharuɗa na IMF.

Dogaron ƙasashen Afirka kan bashin IMF yana nuna karuwar matsalolin tattalin arziƙi, yayin da suke ƙoƙarin cike gibin kasafin kuɗi da cimma burin ci gaba mai ɗorewa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AfrikaCin BashiIMFNijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Na Matukar Adawa Da Binciken Da Amurka Ta Yi Kan Manufofin Sana’o’in Na’urorin Lantarki Na Kasar Sin

Next Post

‘Yan Bindiga Sun Ƙwace Kayan Abincin Kirsimeti A Kaduna

Related

Hukumar kashe gobara
Manyan Labarai

An Samu Asarar Dukiya ta Miliyan ₦273, Tare Da Mutuwar Mutum 5 A Kano – Hukuma

10 hours ago
Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 
Manyan Labarai

Kashinku Ya Bushe: Sojoji Sun Lashi Takobin Kawo Ƙarshen ‘Yan Ta’adda A Zamfara Da Katsina 

15 hours ago
An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja
Manyan Labarai

An Kashe Wani, Wasu Sun Jikkata A Rikicin Manoma Da Makiyaya A Neja

16 hours ago
Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa
Manyan Labarai

Hajjin Bana: Falalar Tsayuwar Arfa

18 hours ago
Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa
Manyan Labarai

Hajjin 2025: Alhajin Kano Ya Rasu A Makka Kwana Ɗaya Kafin Arfa

18 hours ago
Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano
Manyan Labarai

Kotu Ta Tura Ɗan Tiktok Gidan Yari Kan Shigar Mata Da Kalaman Batsa A Kano

1 day ago
Next Post
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

'Yan Bindiga Sun Ƙwace Kayan Abincin Kirsimeti A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

Xi Da Trump Sun Tattauna Ta Wayar Tarho

June 5, 2025
Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

Kasar Sin Ta Bukaci Amurka Ta Yi Watsi Da Amfani Da Batun Tsaron Kasa Barkatai

June 5, 2025
Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

Wani Matashi Dan Shekara 33 Ya Rasu Bayan Ya Fada Wata Tsohuwar Rijiya A Kano

June 5, 2025
Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

Ma’aikatar Harkokin Waje: Kasar Sin Ta Kasance Gwarzuwa Wajen Samar Da Ci Gaba Ba Tare Da Gurbata Muhalli Ba

June 5, 2025
‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

‘Yansanda Sun Hallaka Ɗan Fashi Da Makami Tare Da Jikkata Wasu Da Dama A Bauchi 

June 5, 2025
Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

Lambar “-1.5” Gargadi Ce Da Al’ummar Duniya Ke Yi Ga Azzaluma 

June 5, 2025
Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

Sabbin Matakan Amurka Game Da Masu Shiga Kasar Sun Ci Karo Da Ikirarinta Na Mutunta Hakkokin Bil Adama

June 5, 2025
Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

Bukola Saraki Ya Tallafawa Al’ummar Mokwa Da Gudunmawar Kuɗi

June 5, 2025
Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

Diaz Ba Na Sayarwa Bane – Liverpool Ta Fadawa Barcelona

June 5, 2025
Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

Wani Injin Jirgi Mai Saukar Ungulu Kirar Kasar Sin Ya Samu Shaidar Amincewa 

June 5, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.