• English
  • Business News
Wednesday, August 13, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Ba Ta Cikin Kasashe 10 Da Suka Fi Cin Bashi A Afirka – IMF

by Sadiq
8 months ago
in Manyan Labarai
0
Shugaban Kasa Yana Bibiyar Zanga-zangar Matsin Rayuwa – Minista
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Asusun Lamuni na Duniya (IMF) ya fitar da rahoton jerin ƙasashen 10 da suka fi cin bashi a nahiyar Afirka, a lokacin da ƙasashen ke fama da matsanancin bashin da ya dabaibaye su.

Rahoton ya bayyana cewa, duk da ɗimbin bashin da Nijeriya ke karɓowa, ba ta cikin jerin ƙasashen da suka fi dogaro da lamuni daga IMF a Afirka.

  • Sin Na Matukar Adawa Da Binciken Da Amurka Ta Yi Kan Manufofin Sana’o’in Na’urorin Lantarki Na Kasar Sin
  • Sin Ta Sha Alwashin Karfafa Kare Muhallin Halittun Rawayen Kogi

Akwai ƙasashe 10 da suka yi fice wajen karɓar bashin IMF, galibi don cike gibin kasafin kuɗi da kuma magance matsalolin tattalin arziƙi.

Koyaushe, IMF na gindaya tsauraran sharuɗa, kamar cire tallafi, rage darajar kuɗaɗen ƙasa, da tsuke bakin aljihu kafin bayar da bashin.

Ga jerin ƙasashen 10 da suka fi cin bashi daga IMF:

Labarai Masu Nasaba

Majalisar Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukuma Bisa Zargin Kara Farashin Takin Gwamnati

Gwamnatin Neja Ta Tabbatar Da Kama Hatsabibin Ɗan Bindiga, Abubakar Abba

1. Masar – Ta karbi bashin dala biliyan 9.45, tana cikin matsanancin hali na tattalin arziƙi.

2. Kenya – Ta karɓi dala biliyan 3.02 don bunƙasa tattalin arziƙi da magance matsalolin cikin gida.

3. Angola – Ta dogara kan dala biliyan 2.99 don farfaɗo da tattalin arziƙinta.

4. Ghana – Ta karɓi dala biliyan 2.25, tana fama da karyewar darajar kuɗi.

5. Ivory Coast – Dala biliyan 2.19 don aiwatar da tsare-tsaren ci gaba.

6. Jamhuriyar Dimokuraɗiyyar Congo – Ta amshi dala biliyan 1.6 don magance matsalolin tattalin arziƙi duk da arziƙin albarkatun ƙasa.

7. Habasha – Ta karɓi dala biliyan 1.31 don magance matsalolin tattalin arziƙi.

8. Afirka ta Kudu – Dala biliyan 1.14 don tunkarar matsalolin cikin gida.

9. Kamaru – Ta ciyo dala biliyan 1.13.

10. Senegal – Ta karɓi dala biliyan 1.11 bayan karɓar tsauraran sharuɗa na IMF.

Dogaron ƙasashen Afirka kan bashin IMF yana nuna karuwar matsalolin tattalin arziƙi, yayin da suke ƙoƙarin cike gibin kasafin kuɗi da cimma burin ci gaba mai ɗorewa.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: AfrikaCin BashiIMFNijeriya
ShareTweetSendShare
Previous Post

Sin Na Matukar Adawa Da Binciken Da Amurka Ta Yi Kan Manufofin Sana’o’in Na’urorin Lantarki Na Kasar Sin

Next Post

‘Yan Bindiga Sun Ƙwace Kayan Abincin Kirsimeti A Kaduna

Related

Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure
Manyan Labarai

Majalisar Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukuma Bisa Zargin Kara Farashin Takin Gwamnati

1 hour ago
Za Mu Nome Dazuka Don Magance Matsalar Tsaro A Neja – Bago
Manyan Labarai

Gwamnatin Neja Ta Tabbatar Da Kama Hatsabibin Ɗan Bindiga, Abubakar Abba

6 hours ago
PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi
Manyan Labarai

Tambuwal: ’Yan Nijeriya Sun Soki EFCC Kan Rashin Kama Okowa, Ganduje Da Yahaya Bello

10 hours ago
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12
Manyan Labarai

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N820 Kan Kowace Lita

11 hours ago
Kano
Manyan Labarai

Gwamnatin Kano Ta Bayar Da Kwangilar Hanyoyi 17 Akan Naira Biliyan 40.8

1 day ago
PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi
Manyan Labarai

PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

1 day ago
Next Post
Mazauna Kuyello A Jihar Kaduna Na Cikin Zullumin Bayyanar ‘Yan Ta’addar Ansaru

'Yan Bindiga Sun Ƙwace Kayan Abincin Kirsimeti A Kaduna

LABARAI MASU NASABA

Aikin Hakar Kwal Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani Ya Fara Wuce 50% a Kasar Sin

Aikin Hakar Kwal Ta Hanyar Amfani Da Fasahar Zamani Ya Fara Wuce 50% a Kasar Sin

August 13, 2025
Majalisar Kano Na Shirin Zartar Da Dokar Gwajin Kwayoyin Jini, Kanjamau Da Cutar Hanta Kafin Aure

Majalisar Kano Ta Dakatar Da Shugaban Karamar Hukuma Bisa Zargin Kara Farashin Takin Gwamnati

August 13, 2025
PLA Ta Kori Jirgin Ruwan Yakin Amurka Daga Yankin Ruwan Kasar Sin A Kusa Da Huangyan Dao

PLA Ta Kori Jirgin Ruwan Yakin Amurka Daga Yankin Ruwan Kasar Sin A Kusa Da Huangyan Dao

August 13, 2025
NDLEA Ta Kama Dilolin Ƙwaya 49 A Kano

NDLEA Ta Kama Dilolin Ƙwaya 49 A Kano

August 13, 2025
Za Mu Nome Dazuka Don Magance Matsalar Tsaro A Neja – Bago

Gwamnatin Neja Ta Tabbatar Da Kama Hatsabibin Ɗan Bindiga, Abubakar Abba

August 13, 2025
ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi

ADC Ta Dakatar Da Shugabanta Da Wasu Jiga-jigai 3 A Kebbi

August 13, 2025
An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe

An Kama Hakimi Kan Zargin Yi Wa ‘Yar Shekara 12 Fyaɗe A Gombe

August 13, 2025
PDP Ta Soki Gwamnatin Tinubu Kan Tsare Tambuwal Da EFCC Ta Yi

Tambuwal: ’Yan Nijeriya Sun Soki EFCC Kan Rashin Kama Okowa, Ganduje Da Yahaya Bello

August 13, 2025
Dangote Ya Sake Zama Wanda Ya Fi Kowa Kudi A Afrika Karo Na 12

Matatar Dangote Ta Sake Rage Farashin Man Fetur Zuwa N820 Kan Kowace Lita

August 13, 2025
Yadda Jami’an ‘Yansanda Suka Yi Garkuwa Da Wani Mazaunin Abuja, Sun Kwashe Fiye Da Naira Miliyan 20 A Asusunsa

‘Yansanda Sun Fara Bincike Kan Rasuwar Wani Dan NYSC A Bauchi

August 12, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.