• English
  • Business News
Wednesday, June 4, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Da Brazil Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Kasuwanci Ta Dala Biliyan 1

by Khalid Idris Doya and Sulaiman
2 months ago
in Labarai
0
Nijeriya Da Brazil Sun Sanya Hannu Kan Yarjejeniyar Kasuwanci Ta Dala Biliyan 1
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Nijeriya da kasar Brazil sun sanya hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna a bangaren kasuwanci ta ‘Green Imperative Project’ (GIP) na dala biliyan 1.1 domin bunkasa harkokin noma da zuba hannun jari ga kamfanoni masu zaman kansu a Nijeriya.
Wannnan na cikin matakan kariya kan wadata kasa da abinci.

Shirin GIP, shiri ne kan aikin noma mafi girma a Afirka wanda ke ba da fifiko ga ci gaban noma mai dorewa, yana da nufin habaka yanayin tsari don samar da abinci a Nijeriya cikin inganci.

  • Hauhawar Farashi A Nijeriya Ta Ragu Zuwa 23.18 Cikin 100 A Fabrairu — NBS
  • Azumi Ya Dara Wa Sauran Ibadu

A shekarar 2018 ne aka fara rattaba hannu kan yarjejeniyar dala biliyan 1.1 na GIP 1, yayin da kashi na 2 na shirin dala biliyan 4.3 da kuma JBS na dala biliyan 2.5 aka sanya hannu a Brazil a ziyarar da Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya kai kasar a bara.

Mataimakin shugaban kasa, Kashim Shettima ya misalta sanya hannu kan shirin farko na kasuwancin GIP 1 a wani mataki na gwamnatin Tinubu na wadata kasa da abinci.
Da yake jawabi yayin rattaba hannu a rukunin shirin kasuwanci GIP 1 a fadar shugaban kasa da ke Abuja, Shettima ya ce shirin GIP zai bude wasu damarmakin masu tarin yawa da za su kai ga bude kofofin ci gaban tattalin arzikin kasa da inganta kwarin gwiwa ga masu zuba hannun jari a Nijeriya.

Ya ce, “Yayin da wannan gwamnatin ke kan kokarin magance kalubalen samar da abinci da muke fuskanta tare da maida hankali kan ajandar guda 8 na Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ya zama wajibi mu hada hannu tare da yin amfani da shirye-shiryen da ake da su kamar su GIP domin ci gaba da manufofinsu, yin amfani da dabaru da hikimomin bunkasa tattalin arzikinmu da kuma kara kwarin gwiwar masu zuba jari.”
Shettima ya lura cewa, yayin da GIP ya yi daidai da manufofi da shirye-shiryen gwamnatin Tinubu, ya ce, shirin zai kyautata harkokin kananan manoma da sauran harkokin da suka shafi noma a fadin kasar nan.

Labarai Masu Nasaba

‘Yansanda A Kano Sun Gargaɗi Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

Ya ce tabbas shirin zai taimaka wajen magance matsaloli da dama da manoma ke fama a Nijeriya, musamman kananan manoma da suke fuskatar matsalar fitar da amfani gona.

Bisa wannan nasarar sanya hannun da aka samu, mataimakin shugaban ya jinjina wa ministan noma, ministan kudi, ministan shari’a da ministan harkokin waje da sauran wadanda suka dafa har aka kai ga wannan matakin.

Shi kuma a bangarensa, Jakadar Brazil a Nijeriya, Carlos Garcete, ya ce babban abin alfahari ne ga Brazil ta hada kai da ‘Green Imperatibe Project (GIP), yana mai cewa a cikin shekaru bakwai da suka gabata, an yi shawarwari da gwamnatin Nijeriya da nufin samun kudaden da ake bukata daga bankuna masu zaman kansu da na raya kasa na yanki don gudanar da wannan gagarumin aiki, wanda ya kai kusan dala biliyan 1.1.

A madadin gwamnatin kasar Burazil, Mista Garcete ya jinjina wa Shugaban Tinubu bisa nasarar tabbatar da dogon muhawarar yiyuwar shirin.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

An Yi Tarukan Tattaunawar Kasa Da Kasa Kan More Damammakin Sin A Havana Da Doha

Next Post

Gobara Ta Kashe Yaro A Sansanin ‘Yan Gudun Hijira A Maiduguri

Related

Sanusi
Manyan Labarai

‘Yansanda A Kano Sun Gargaɗi Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

9 hours ago
Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 
Labarai

Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

12 hours ago
Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya
Manyan Labarai

Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

13 hours ago
Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus
Manyan Labarai

Mataimakin Kakakin Majalisar Dokokin Ondo Da Shugaban Masu Rinjaye Sun Yi Murabus

16 hours ago
Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki
Manyan Labarai

Shehu Sani Ya Buƙaci Shugabannin Arewa Su Mara Wa Tinubu Baya Ya Yi Shekaru 8 A Kan Mulki

19 hours ago
Jihohin Da Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Watan Yuni – NiMet
Manyan Labarai

Jihohin Da Za Su Iya Fuskantar Ambaliyar Ruwa A Watan Yuni – NiMet

20 hours ago
Next Post
Gobara Ta Kashe Yaro A Sansanin ‘Yan Gudun Hijira A Maiduguri

Gobara Ta Kashe Yaro A Sansanin 'Yan Gudun Hijira A Maiduguri

LABARAI MASU NASABA

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

Manufar Bude Kofa Ta Shaida Niyyar Sin Ta Ingiza Dunkulewar Duniya

June 3, 2025
Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

Kocin Inter Milan Simone Inzaghi Ya Bar Kungiyar Kwanaki Biyu Bayan Rashin Nasara A Hannun PSG

June 3, 2025
Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

Sin Ta Yi Fatali Da Ikirarin Amurka Cewa Ta Karya Yarjejeniyar Tattaunawar Geneva

June 3, 2025
Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

Karuwar Darajar Sana’ar Samar Da Kayan Laturoni Da Dangoginsu a Sin Cikin Watanni 4 Na Farkon Bana Ya Karu Da 11.3% 

June 3, 2025
Sanusi

‘Yansanda A Kano Sun Gargaɗi Sarki Sanusi II Kan Fitowa Hawan Sallah

June 3, 2025
Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

Masani Kwadifwa: Kasar Sin Ce Mai Kare Tabbatuwar Adalci A Duniya

June 3, 2025
An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

An Samu Karuwar Kaso 2.7 Na Yawan Tafiye-Tafiye Zuwa Ketare Yayin Hutun Bikin Dragon Boat Na Kasar Sin

June 3, 2025
Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

Sallah: Gwamnatin Kebbi Ta Raba Naira Miliyan 337 Ga Mata 11,229 

June 3, 2025
Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

Yanzu-yanzu: JUSUN Ta Dakatar Da Yajin Aikin Da Fara A Faɗin Ƙasa Baki Ɗaya

June 3, 2025
Darajar Hajojin Da Aka Yi Jigilarsu a Kasuwar Sin Daga Watan Janairu Zuwa Na Afrilu Ta Karu Da 5.6% 

Darajar Hajojin Da Aka Yi Jigilarsu a Kasuwar Sin Daga Watan Janairu Zuwa Na Afrilu Ta Karu Da 5.6% 

June 3, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.