• English
  • Business News
Saturday, June 7, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 1.1 Duk Shekara Sakamakon Zazzabin Cizon Sauro – Ministan Lafiya

by Yusuf Shuaibu
6 months ago
in Labarai
0
Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 1.1 Duk Shekara Sakamakon Zazzabin Cizon Sauro – Ministan Lafiya
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan lafiya da walwalar jama’a, Farfesa Muhammad Pate, ya ce asarar da ake samu a duk shekara a Nijeriya sakamakon cutar zazzabin cizon sauro ya zarce dala biliyan 1.1.

Pate ya bayyana haka ne a wajen taron kaddamar da shawarwarin kawar da zazzabin cizon sauro a Nijeriya wanda ya gudana a Abuja.

  • Leicester City Ta Kori Kocinta Bayan Rashin Nasara A Hannun Chelsea 
  • Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Biyu

Wata sanarwa da mataimakin daraktan yada labarai da hulda da jama’a na ma’aikatar lafiya, Alaba Balogun, ya fitar a ranar Talata, ta bayyana cewa Pate ya bayyana cutar zazzabin cizon sauro ba wai matsalar kiwon lafiya kadai ba, amma matsalar tattalin arziki ne da ya kamata a kawar da ita.

Pate ya ce wannan yunkuri mataki ne mai kwarin gwiwa na yanke hukunci tinkarar cutar da magance ta.

Ya ce, “Maleriya na ci gaba da yin illar da ba za a amince da ita ba a Nijeriya, inda kashi 27 cikin 100 na masu fama da cutar zazzabin cizon sauro a duniya da kuma kashi 31 cikin 100 na mace-macen zazzabin cizon sauro a duniya, kasarmu ce tafi kowace kasa daukar nauyin wannan cuta. A cikin 2022, yara sama da 180,000 na Nijeriya ‘yan kasa da shekaru biyar sun rasa rayukansu sakamakon zazzabin cizon sauro. Muke da kayan aikin da za mu iya magance cutar.

Labarai Masu Nasaba

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

“Wannan ba matsalar lafiya ba ce kawai, matakin gaggawa ce ga ci gaban tattalin arziki. Zazzabin cizon sauro yana rage yawan aiki, yana kara kashe kudin kiwon lafiya daga aljihu da kuma habaka kalubalen talauci. Nijeriya na asarar kudaden shiga duk shekara daga zazzabin cizon sauro wanda ya zarce dala biliyan 1.1, babban abin tunatarwa kan muhimmancin tattalin arziki na kawar da cutar.”

A cewarsa, kawar da zazzabin cizon sauro wani muhimmin bangare ne na tsarin sake zuba jari na sashen lafiya na Nijeriya don kawo sauyi a fannin kiwon lafiya, daidai da sabon ajandar da gwamnatin yanzu ke da shi.

Ya kuma bayyana muhimmancin shugabannin gargajiya da na addini don samar da goyon baya daga tushe da kuma tasiri wajen sauya halayya.

Karamin ministan lafiya da walwalar jama’a, Dakta Iziak Salako, ya tabbatar da kungiyar masu ba da shawara a matsayin gungun kwararru da za su ba da shawarwari masu inganci don taimakawa kasar nan wajen rage matsalar zazzabin cizon sauro da ba za a amince da ita ba tare da samar da sahihin hanyoyin da za a bi a Nijeriya.

“Domin mu samu nasara, kamfanoni masu zaman kansu da abokan huldar kasa da kasa da ma’aikatan kiwon lafiya da kuma al’ummomin da muke yi wa hidima dole ne mu hada kai,” in ji Salako.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

ShareTweetSendShare
Previous Post

Gwamnan Sakkwato Ya Gabatar Da Kasafin Kudin 2025 Na Biliyan 526

Next Post

“Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 492 Duk Shekara Kan Noƙe Haraji”

Related

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya
Manyan Labarai

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

3 hours ago
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC
Labarai

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

6 hours ago
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi
Labarai

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

6 hours ago
Daurarru
Labarai

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

16 hours ago
Wutar lantarki
Labarai

Fadar Shugaban Kasa Na Yunkurin Biyan Basukan Wutar Lantarki Na Naira Tiriliyan 2

18 hours ago
Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka
Labarai

Jihohi Bakwai Na Kashe Kaso 190 Na Kudin Shigarsu Wajen Biyan Basuka

19 hours ago
Next Post
“Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 492 Duk Shekara Kan Noƙe Haraji”

“Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 492 Duk Shekara Kan Noƙe Haraji”

LABARAI MASU NASABA

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

Manchester City Ta Kammala Daukar Tijjani Reijnders Daga AC Milan

June 7, 2025
Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

Ban Sa Ran Lashe Kyautar Ballon D’or Ta Bana Ba – Lamine Yamal

June 7, 2025
Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

Dangote Ya Sanya Wa Hanya Sunan Tinubu, Zai Kashe Naira Biliyan 900 Don Gina Hanyoyi A Nijeriya

June 7, 2025
Neja

Dalilin Rashin Fara Aikin Kamfanin Takin Zamani Na Gwamnatin Jihar Neja

June 7, 2025
Adawa

Yadda Rarrabuwar Kawunan Jam’iyyu Zai Iya Sauya Alkiblar Zaben 2027

June 7, 2025
2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

2027: Wasu Gwamnonin PDP Na Shan Matsin Lamba Don Sauya Sheka Zuwa APC

June 7, 2025
Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

Tsarin Jam’iyya Daya Ba Barazana Ba Ce Ga Tsarin Dimokuradiyyar Nijeriya – Gwamna Namadi

June 7, 2025
Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

Jami’i: Kasuwar Kasar Sin Ta Kasance Mai Jan Hankalin Zuba Jarin Waje A Ko Yaushe

June 6, 2025
Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

Kasar Sin Ta Samu Ci Gaba Wajen Inganta Amfani Da Ruwa A Shekarar 2024

June 6, 2025
Daurarru

Kashi 70 Na Fursunonin Nijeriya Ba A Yanke Musu Hukunci Ba

June 6, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.