ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Wednesday, July 15, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 1.1 Duk Shekara Sakamakon Zazzabin Cizon Sauro – Ministan Lafiya

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Nijeriya

Ministan lafiya da walwalar jama’a, Farfesa Muhammad Pate, ya ce asarar da ake samu a duk shekara a Nijeriya sakamakon cutar zazzabin cizon sauro ya zarce dala biliyan 1.1.

Pate ya bayyana haka ne a wajen taron kaddamar da shawarwarin kawar da zazzabin cizon sauro a Nijeriya wanda ya gudana a Abuja.

  • Leicester City Ta Kori Kocinta Bayan Rashin Nasara A Hannun Chelsea 
  • Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Biyu

Wata sanarwa da mataimakin daraktan yada labarai da hulda da jama’a na ma’aikatar lafiya, Alaba Balogun, ya fitar a ranar Talata, ta bayyana cewa Pate ya bayyana cutar zazzabin cizon sauro ba wai matsalar kiwon lafiya kadai ba, amma matsalar tattalin arziki ne da ya kamata a kawar da ita.

ADVERTISEMENT

Pate ya ce wannan yunkuri mataki ne mai kwarin gwiwa na yanke hukunci tinkarar cutar da magance ta.

Ya ce, “Maleriya na ci gaba da yin illar da ba za a amince da ita ba a Nijeriya, inda kashi 27 cikin 100 na masu fama da cutar zazzabin cizon sauro a duniya da kuma kashi 31 cikin 100 na mace-macen zazzabin cizon sauro a duniya, kasarmu ce tafi kowace kasa daukar nauyin wannan cuta. A cikin 2022, yara sama da 180,000 na Nijeriya ‘yan kasa da shekaru biyar sun rasa rayukansu sakamakon zazzabin cizon sauro. Muke da kayan aikin da za mu iya magance cutar.

LABARAI MASU NASABA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

“Wannan ba matsalar lafiya ba ce kawai, matakin gaggawa ce ga ci gaban tattalin arziki. Zazzabin cizon sauro yana rage yawan aiki, yana kara kashe kudin kiwon lafiya daga aljihu da kuma habaka kalubalen talauci. Nijeriya na asarar kudaden shiga duk shekara daga zazzabin cizon sauro wanda ya zarce dala biliyan 1.1, babban abin tunatarwa kan muhimmancin tattalin arziki na kawar da cutar.”

A cewarsa, kawar da zazzabin cizon sauro wani muhimmin bangare ne na tsarin sake zuba jari na sashen lafiya na Nijeriya don kawo sauyi a fannin kiwon lafiya, daidai da sabon ajandar da gwamnatin yanzu ke da shi.

Ya kuma bayyana muhimmancin shugabannin gargajiya da na addini don samar da goyon baya daga tushe da kuma tasiri wajen sauya halayya.

Karamin ministan lafiya da walwalar jama’a, Dakta Iziak Salako, ya tabbatar da kungiyar masu ba da shawara a matsayin gungun kwararru da za su ba da shawarwari masu inganci don taimakawa kasar nan wajen rage matsalar zazzabin cizon sauro da ba za a amince da ita ba tare da samar da sahihin hanyoyin da za a bi a Nijeriya.

“Domin mu samu nasara, kamfanoni masu zaman kansu da abokan huldar kasa da kasa da ma’aikatan kiwon lafiya da kuma al’ummomin da muke yi wa hidima dole ne mu hada kai,” in ji Salako.

Nijeriya
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Amurka Ta Yi Alƙawarin Sa Ido Sosai A Zaɓen Nijeriya Na 2027
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Sautin Muryar Da Aka Fallasa Kan El-Rufai Ya Haifar Da Zazzafar Muhawara
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Ci-ma-zaunen Ƴan Siyasa Ne Ke Tunanin Yin Maguɗi A Zaɓen 2027 – Makarfi
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    An Samu Ruɗani Kan Rashin Bayyana Jerin Ƴan Takarar Jam’iyyun Siyasa Na Zaɓen 2027

MASU ALAKA

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu
Labarai

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga
Manyan Labarai

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi
Labarai

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
Next Post
“Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 492 Duk Shekara Kan Noƙe Haraji”

“Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 492 Duk Shekara Kan Noƙe Haraji”

LABARAI MASU NASABA

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

Sakamakon Binciken Masana Na Kasar Da Ake Fitarwa Kyauta Yana Kara Jan Hankalin Duniya

July 14, 2026
Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

Cinikin Waje Ta Kasar Sin Na Bunkasa Cikin Sauri Da Kwanciyar Hankali A Rabin Farko Na Shekara Ta 2026

July 14, 2026
An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

An Yi Tir Da Kalaman Wasu Sassan Ketare Game Da Yayata Batun Cika Shekaru Goma Da Fitar Da Abin Da Aka Kira “Hukuncin Tekun Kudancin Sin”

July 14, 2026
Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

Nijeriya Za Ta Zama Ƙasa Mai Zaman Lafiya, Ba Za A Ƙara Samun Kashe-kashen Jama’a Ba – Oluremi Tinubu

July 14, 2026
Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

Sin Ta Tsara Bunkasa Darajar Cinikayyar Kayayyaki Zuwa Yuan Tiriliyan 60 Yayin Shirin Raya Kasa Na Shekarar 2026 Zuwa 2030

July 14, 2026
Katsina: Kotu Ta Yanke Wa Hauwa’u Hukuncin Kisa Ta Hanyar Rataya Kan Taimaka Wa ’Yan Bindiga

Kotu Ta Tsare Shugaban Makaranta Da Malami Kan Zargin Lalata Da Ɗaliba Mai Shekara 6 A Gombe

July 14, 2026
An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

An Bankado Muguwar Aniyar Japan Ta Haifar Da Tashin Hankali A Tekun Kudancin Sin

July 14, 2026
Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

Layin Dogo Tsakanin Tanzaniya Da Zambiya Ya Zama Shaidar Abota Tsakanin Sin Da Afirka

July 14, 2026
Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

Nijeriya da Masar Sun Ƙulla Haɗin Gwiwa Domin Yaƙi da Miyagun Ƙwayoyi

July 14, 2026
CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

CMG Ya Gudanar Da Babban Taron Masu Kirkirar Manyan Shirye-Shirye Da Fina-Finai

July 14, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.