ADVERTISEMENT
  • English
  • Business News
Thursday, June 4, 2026
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 1.1 Duk Shekara Sakamakon Zazzabin Cizon Sauro – Ministan Lafiya

by Yusuf Shuaibu
2 years ago
Nijeriya

Ministan lafiya da walwalar jama’a, Farfesa Muhammad Pate, ya ce asarar da ake samu a duk shekara a Nijeriya sakamakon cutar zazzabin cizon sauro ya zarce dala biliyan 1.1.

Pate ya bayyana haka ne a wajen taron kaddamar da shawarwarin kawar da zazzabin cizon sauro a Nijeriya wanda ya gudana a Abuja.

  • Leicester City Ta Kori Kocinta Bayan Rashin Nasara A Hannun Chelsea 
  • Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Biyu

Wata sanarwa da mataimakin daraktan yada labarai da hulda da jama’a na ma’aikatar lafiya, Alaba Balogun, ya fitar a ranar Talata, ta bayyana cewa Pate ya bayyana cutar zazzabin cizon sauro ba wai matsalar kiwon lafiya kadai ba, amma matsalar tattalin arziki ne da ya kamata a kawar da ita.

ADVERTISEMENT

Pate ya ce wannan yunkuri mataki ne mai kwarin gwiwa na yanke hukunci tinkarar cutar da magance ta.

Ya ce, “Maleriya na ci gaba da yin illar da ba za a amince da ita ba a Nijeriya, inda kashi 27 cikin 100 na masu fama da cutar zazzabin cizon sauro a duniya da kuma kashi 31 cikin 100 na mace-macen zazzabin cizon sauro a duniya, kasarmu ce tafi kowace kasa daukar nauyin wannan cuta. A cikin 2022, yara sama da 180,000 na Nijeriya ‘yan kasa da shekaru biyar sun rasa rayukansu sakamakon zazzabin cizon sauro. Muke da kayan aikin da za mu iya magance cutar.

LABARAI MASU NASABA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

“Wannan ba matsalar lafiya ba ce kawai, matakin gaggawa ce ga ci gaban tattalin arziki. Zazzabin cizon sauro yana rage yawan aiki, yana kara kashe kudin kiwon lafiya daga aljihu da kuma habaka kalubalen talauci. Nijeriya na asarar kudaden shiga duk shekara daga zazzabin cizon sauro wanda ya zarce dala biliyan 1.1, babban abin tunatarwa kan muhimmancin tattalin arziki na kawar da cutar.”

A cewarsa, kawar da zazzabin cizon sauro wani muhimmin bangare ne na tsarin sake zuba jari na sashen lafiya na Nijeriya don kawo sauyi a fannin kiwon lafiya, daidai da sabon ajandar da gwamnatin yanzu ke da shi.

Ya kuma bayyana muhimmancin shugabannin gargajiya da na addini don samar da goyon baya daga tushe da kuma tasiri wajen sauya halayya.

Karamin ministan lafiya da walwalar jama’a, Dakta Iziak Salako, ya tabbatar da kungiyar masu ba da shawara a matsayin gungun kwararru da za su ba da shawarwari masu inganci don taimakawa kasar nan wajen rage matsalar zazzabin cizon sauro da ba za a amince da ita ba tare da samar da sahihin hanyoyin da za a bi a Nijeriya.

“Domin mu samu nasara, kamfanoni masu zaman kansu da abokan huldar kasa da kasa da ma’aikatan kiwon lafiya da kuma al’ummomin da muke yi wa hidima dole ne mu hada kai,” in ji Salako.

Nijeriya
Yusuf Shuaibu
+ postsBio
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Masana Tattalin Arziki Sun Yi Watsi Da Rahoton NBS Kan Tattalin Arziki
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Alƙawarin Wa’adi Ɗaya Na Peter Obi Ya Raba Kawunan Ƴan Arewa
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    ‘Yan Majalisar Wakilai 50 Da Suka Rasa Tikitin Takara A Zaɓen Fid Da Gwani Na APC
  • Yusuf Shuaibu
    https://hausa.leadership.ng/author/yusuf-shuaibu/
    Zaɓen Fitar Da Gwani: APC Na Fuskantar Barazanar Tawaye

MASU ALAKA

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba
Labaran Kasuwanci

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City
Wasanni

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed
Labarai

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Next Post
“Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 492 Duk Shekara Kan Noƙe Haraji”

“Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 492 Duk Shekara Kan Noƙe Haraji”

LABARAI MASU NASABA

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

Tasirin Nasarar Da Kasar Sin Ta Cimma A Fannin Kakkabe Matsanancin Talauci

June 4, 2026
Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

Sabbin Ra’ayoyin Ci Gaba: Manufofin Zamani Na Zamanantarwa

June 4, 2026
Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

Fargabar Satar Mutane Ya Sa An Rufe Makarantu A Abuja Da Mararaba

June 4, 2026
Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

Ana Gudanar Da Taron Masana Ilmin Harkokin Kasar Sin Karo Na Uku

June 4, 2026
Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

Sin: Ya Kamata Tarayyar Turai Ta Dubi Huldar Tattalin Arziki Da Ciniki Tsakaninta Da Sin Bisa Daidaito

June 4, 2026
Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

Arsenal Na Dab Da Ɗaukar Jeremy Monga Daga Leicester City

June 4, 2026
An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

An Gudanar Da Taron “Tattaunawar Magadan Garuruwa Na Duniya Na 2026” A Birnin Beijing

June 4, 2026
Atiku Ne Ya Fi Dacewa Da Tikitin Takara A ADC Amma Ya Kamata Ya Janye — Baba-Ahmed

2027: Kasancewa Ɗan Arewa Kaɗai Ba Zai Tabbatar Da Samun Ƙuri’u Ba – Baba-Ahmed

June 4, 2026
Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

Gwamnatin Tarayya Ta Mayar Da Ofishin NAGGW Zuwa Kano Domin Yaƙi Da Hamada

June 4, 2026
Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

Mambobin NYSC 4, Soja da Mutum 1 Sun Rasu A Hatsarin Mota A Adamawa

June 4, 2026

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.