• English
  • Business News
Thursday, October 9, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 1.1 Duk Shekara Sakamakon Zazzabin Cizon Sauro – Ministan Lafiya

byYusuf Shuaibu
10 months ago
Nijeriya

Ministan lafiya da walwalar jama’a, Farfesa Muhammad Pate, ya ce asarar da ake samu a duk shekara a Nijeriya sakamakon cutar zazzabin cizon sauro ya zarce dala biliyan 1.1.

Pate ya bayyana haka ne a wajen taron kaddamar da shawarwarin kawar da zazzabin cizon sauro a Nijeriya wanda ya gudana a Abuja.

  • Leicester City Ta Kori Kocinta Bayan Rashin Nasara A Hannun Chelsea 
  • Sin Ta Yi Nasarar Harba Sabbin Taurarin Dan Adam Biyu

Wata sanarwa da mataimakin daraktan yada labarai da hulda da jama’a na ma’aikatar lafiya, Alaba Balogun, ya fitar a ranar Talata, ta bayyana cewa Pate ya bayyana cutar zazzabin cizon sauro ba wai matsalar kiwon lafiya kadai ba, amma matsalar tattalin arziki ne da ya kamata a kawar da ita.

Pate ya ce wannan yunkuri mataki ne mai kwarin gwiwa na yanke hukunci tinkarar cutar da magance ta.

Ya ce, “Maleriya na ci gaba da yin illar da ba za a amince da ita ba a Nijeriya, inda kashi 27 cikin 100 na masu fama da cutar zazzabin cizon sauro a duniya da kuma kashi 31 cikin 100 na mace-macen zazzabin cizon sauro a duniya, kasarmu ce tafi kowace kasa daukar nauyin wannan cuta. A cikin 2022, yara sama da 180,000 na Nijeriya ‘yan kasa da shekaru biyar sun rasa rayukansu sakamakon zazzabin cizon sauro. Muke da kayan aikin da za mu iya magance cutar.

LABARAI MASU NASABA

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

“Wannan ba matsalar lafiya ba ce kawai, matakin gaggawa ce ga ci gaban tattalin arziki. Zazzabin cizon sauro yana rage yawan aiki, yana kara kashe kudin kiwon lafiya daga aljihu da kuma habaka kalubalen talauci. Nijeriya na asarar kudaden shiga duk shekara daga zazzabin cizon sauro wanda ya zarce dala biliyan 1.1, babban abin tunatarwa kan muhimmancin tattalin arziki na kawar da cutar.”

A cewarsa, kawar da zazzabin cizon sauro wani muhimmin bangare ne na tsarin sake zuba jari na sashen lafiya na Nijeriya don kawo sauyi a fannin kiwon lafiya, daidai da sabon ajandar da gwamnatin yanzu ke da shi.

Ya kuma bayyana muhimmancin shugabannin gargajiya da na addini don samar da goyon baya daga tushe da kuma tasiri wajen sauya halayya.

Karamin ministan lafiya da walwalar jama’a, Dakta Iziak Salako, ya tabbatar da kungiyar masu ba da shawara a matsayin gungun kwararru da za su ba da shawarwari masu inganci don taimakawa kasar nan wajen rage matsalar zazzabin cizon sauro da ba za a amince da ita ba tare da samar da sahihin hanyoyin da za a bi a Nijeriya.

“Domin mu samu nasara, kamfanoni masu zaman kansu da abokan huldar kasa da kasa da ma’aikatan kiwon lafiya da kuma al’ummomin da muke yi wa hidima dole ne mu hada kai,” in ji Salako.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace
Labarai

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Tinubu
Manyan Labarai

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa
Labarai

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Next Post
“Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 492 Duk Shekara Kan Noƙe Haraji”

“Nijeriya Na Asarar Dala Biliyan 492 Duk Shekara Kan Noƙe Haraji”

LABARAI MASU NASABA

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

Tawagar Likitocin Sin Dake Saliyo Ta Gudanar Da Tiyatar Dashen Yatsa Irinta Ta Farko

October 8, 2025
Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

Babban Yankin Sin Ya Soki Lamirin Kalaman Aware Na Jagoran Yankin Taiwan

October 8, 2025
Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

Yawan Zirga-Zirgar Jiragen Kasa Tsakanin Sin Da Turai Kan Layin Dogo Na Tsakiya Ya Zarce 3,000 A Bana

October 8, 2025
Majalisa Ta Nemi Jami’an Tsaro Su Ceto Daliban Jami’ar Gusau 30 Da Aka Sace

Kafa ‘Yansandan Jihohi Na Da Matuƙar Muhimmanci Wajen Magance Matsalar Rashin Tsaro

October 8, 2025
Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

Adadin Kudaden Da Gidajen Sinima Na Sin Suka Tara Yayin Hutun Bikin Ranar Kasa Ya Haura Yuan Biliyan 1.7

October 8, 2025
Tinubu

Tinubu Na Son A Saka Hannun Jari Da Kuɗaɗen Fansho A Ɓangaren Mai Da Iskar Gas

October 8, 2025
Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

Gwamnatin Nasarawa Za Ta Hukunta Duk Masu Amfani Da Sinadiran Kamun Kifi Acikin Ruwa

October 8, 2025
Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

Sin: Ana Sa Ran Jigilar Fasinjoji Fiye Da Miliyan 21 A Yau Ta Jiragen Kasa

October 8, 2025
Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

Kwastam Ta Kama Lita 35,000 Na Man Fetur, Tabar Wiwi Da Sauran Kayayyaki A Kebbi

October 8, 2025
Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

Sin Ta Yi Kira Ga Mambobin WTO Da Su Tinkari Yanayin Tangal-Tangal Tare

October 8, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Go to mobile version