• English
  • Business News
Wednesday, September 17, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Na Bukatar Karin Basuka – Ministan Kudi

by Khalid Idris Doya
10 months ago
in Tattalin Arziki
0
Nijeriya Na Bukatar Karin Basuka – Ministan Kudi
Share on FacebookShare on TwitterShare on WhatsAppTelegram

Ministan kudi da tsare-tsaren tattalin arziki, Wale Edun, ya ce, gwamnatin tarayya tana bukatar karin wasu basukan kudade domin ta cike gibin kasafin kudinta, duk kuwa da cewa wasu ma’aikatu da rassa da sashi-sashi sun inganta harsashen hanyoyin shigar kudinsu.

Ministan ya shaida hakan ne yayin ganawa da hadakar kwamitin majalisar dattawa na kudin da na tsare-tsaren harkokin tattalin arziki kan tsarin kashe kudade na 2025 zuwa 2027.

  • Dikko Radda Ya Bai Wa Gwarazan Hikayata Kyautar Kudi
  • Karancin Takardar Kudi: Masu POS Da Bankuna Na Wasa Da Hankulan Jama’a

Edun ya ce akwai bukatar cikin basukan muddin majalisar dattawa ta amince da hakan.

“Yunkurin da ake yi kan kudin shiga yana tafiya daidai, amma akwai bukatar a kara himma, muna bukatar karin basuka masu albarka, inganci da dourewa.

“Ba kawai don gine-gine da manyan ayyukan ba, har ma don ayyukan jin dadi da walwalar jama’a, ayyukan kiwon lafiya, ilimi da ayyuka a fannonin kiyaye tsaron jama’a don taimaka wa masu karamin karfi da masu fama da talauci,” Edun ya shaida.

Labarai Masu Nasaba

NPA Ta Fara Aiki Da Sabon Tsarin ETO A Tashar Apapa

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

A nasa bangaren, ministan kasafi da tsare-tsaren tattalin arziki, Sanata Atiku Bagudu ya tunatar da ‘yan majalisar yunkurin ciwo bashi tiriliyan 35.5 a kasafin 2024, da farko an yi nufin sanar da gibin tiriliyan 9.7.

“Duk da tsare-tsaren kudaden shiga ya zarta na wasu hukumomin samar da kudaden shiga, har yanzu akwai bukatar gwamnati ta karbo rancen kudade don gudanar da kasafin kudin yadda ya kamata, musamman ta fuskar rabe-rabe da samar da ayyukan yi ga marasa galihu.

“Muna da tsarin hangen nesa na ci gaba na dogon lokaci na 2050,” in ji Bagudu.

Kazalika, shugaban hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa (EFCC), Ola Olukoyede, ya shaida wa kwamitin cewa hukumarsa ta kwato sama da naira biliyan 197 daga watan Janairun 2024,

Ya lura cewa idan gwamnati ta yi aiki tukuru kuma ta samu tarin abubuwan da ake bukata, kasar za ta samu isassun kudaden da za ta kashe a kasafin kudin.

Babban Kwanturolan Hukumar Kwastam ta Nijeriya, Bashir Adeniyi, a cikin jawabinsa, ya bayyana cewa hukumar ta kwastam ta tara naira tiriliyan 5.352 na kudaden shiga fiye da naira tiriliyan 5.09 da aka yi niyyar yi a kasafin kudin shekarar 2024.

Ya ci gaba da cewa, naira tiriliyan 6.3 an yi niyya ne a matsayin kudaden shiga da aka yi hasashen za a samu a shekarar 2025, wanda kasha 10 daga ciki zai kasance abin da ake sa ran samun kudaden shiga a shekarar 2026 da karin kashi 10 na kasafin kudin shekarar 2027.

A nasa jawabin, babban jami’in gudanarwa na rukunin kamfanin man fetur na Nijeriya (NNPCL), Mele Kyari, ya ce kamfanin ya zarce kudaden shiga na naira tiriliyan 12.3 da aka yi hasashen za a iya samu a shekarar 2024, inda ya riga ya tara naira tiriliyan 13.1.

Har ila yau, shugaban hukumar tara haraji ta kasa FIRS, Zacch Adedeji, a nasa jawabin, ya sanar da kwamitocin hadin gwiwa cewa FIRS ta zarce kudaden shiga da aka yi niyya a sassa daban-daban na haraji.


Daga kanmu, magana ta ƙare. Kuna iya samun rahotanni da ɗumi-ɗuminsu da gamsassun ruwayoyin labarai daban da na saura kai-tsaye cikin wayoyinku. Shiga zaurenmu na WhatsApp don sanin halin da ake ciki a duniya ko yaushe

Shiga zaurenmu na WhatsApp

Tags: Kudi
ShareTweetSendShare
Previous Post

Wani Rahoto Ya Fallasa Hanyoyin Da Doka Ta Tanada Don Kare Masu Aikata Fyaɗe A Afirka

Next Post

Kidayar Jama’a Da Harkar Lafiya

Related

Rashin Tsaro Ya Sa Ƴan Gudun Hijira Mamaye Makarantun Benuwe Da Neja Da Katsina
Tattalin Arziki

NPA Ta Fara Aiki Da Sabon Tsarin ETO A Tashar Apapa

2 days ago
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

Kungiyoyi Da Abokan Arziki Na Ci Gaba Da Taya Dantsoho Murna

2 weeks ago
tallafi
Tattalin Arziki

Kudaden Ajiya Na Asusun Nijeriya Ya Karu Zuwa Dala Biliyan 41

3 weeks ago
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho

3 weeks ago
Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5
Tattalin Arziki

Dangote Zai Gina Kamfanin Taki A Habasha Kan Dala Biliyan $2.5

3 weeks ago
NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya
Tattalin Arziki

NBS Ta Bayyana Dalilin Raguwar Farashin Kaya A Nijeriya

4 weeks ago
Next Post
Kidayar Jama’a Da Harkar Lafiya

Kidayar Jama'a Da Harkar Lafiya

LABARAI MASU NASABA

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

Babban Jirgin Ruwan Kasar Sin Ya Nufi Yankin Tekun Kudancin Kasar Domin Gwaji Da Samar Da Horo

September 16, 2025
Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

Shawarwarin Sin: Ingantattun Hanyoyi Masu Sauki Na Warware Sabani

September 16, 2025
Sauye-sauyen Manufofin Gwamnati Na Iya Hana Masu HND Zuwa NYSC

An Yi Garkuwa Da Wani Mai Hidimar Ƙasa Da Ɗalibi A Jos

September 16, 2025
Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

Sin Da Amurka Sun Yi Tattaunawar Keke-da-keke Kan Batutuwan Cinikayya Da Manhajar TikTok

September 16, 2025
Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

Da Ɗumi-ɗumi: Tinubu Ya Dawo Abuja Bayan Hutun Sati 2 A Ƙasar Faransa

September 16, 2025
Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

Sin Da Ghana Na Fadada Hadin Gwiwa A Bangaren Ciniki Da Zuba Jari

September 16, 2025
Sojoji

Sojoji Sun Harbe Wasu ‘Yan Ta’adda 2 A Taraba

September 16, 2025
Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

Yawan Hatsin Da Aka Girbe A Kasar Sin Tsakanin Shekarar 2021-2025 Ya Kai Wani Sabon Matsayi

September 16, 2025
Buhari Ya Taya Amusan Murnar Lashe Zinari A Gasar Tsere Ta Duniya

Tinubu Ya Taya Amusan Da Gumel Murnar Samun Nasarori A Ɓangarori Daban-daban

September 16, 2025
Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

Sin Ta Daga Zuwa Mataki Na 10 A Jadawalin GII Na Kasashen Dake Kan Gaba A Fannin Kirkire-Kirkire

September 16, 2025
Talla

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

Welcome Back!

Login to your account below

Forgotten Password?

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.

Log In

Add New Playlist

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.