• English
  • Business News
Monday, October 20, 2025
Leadership Hausa
Read English News
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
  • Gida
  • LabaraiZafi
    • Kananan Labarai
    • Daga Kasar Sin
    • Dausayin Musulunci
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Manyan Labarai
    • Ado Da Kwalliya
    • Bakon Marubuci
  • Wasanni
  • Siyasa
  • Labaran Kasuwanci
  • Daga Birnin Sin
  • Nishadi
  • Ra’ayi Riga
  • Taskira
  • Al’ajabi
  • Al’adu
No Result
View All Result
Leadership Hausa
No Result
View All Result

Nijeriya Na Bukatar Karin Basuka – Ministan Kudi

by Khalid Idris Doya
11 months ago
Nijeriya

Ministan kudi da tsare-tsaren tattalin arziki, Wale Edun, ya ce, gwamnatin tarayya tana bukatar karin wasu basukan kudade domin ta cike gibin kasafin kudinta, duk kuwa da cewa wasu ma’aikatu da rassa da sashi-sashi sun inganta harsashen hanyoyin shigar kudinsu.

Ministan ya shaida hakan ne yayin ganawa da hadakar kwamitin majalisar dattawa na kudin da na tsare-tsaren harkokin tattalin arziki kan tsarin kashe kudade na 2025 zuwa 2027.

  • Dikko Radda Ya Bai Wa Gwarazan Hikayata Kyautar Kudi
  • Karancin Takardar Kudi: Masu POS Da Bankuna Na Wasa Da Hankulan Jama’a

Edun ya ce akwai bukatar cikin basukan muddin majalisar dattawa ta amince da hakan.

“Yunkurin da ake yi kan kudin shiga yana tafiya daidai, amma akwai bukatar a kara himma, muna bukatar karin basuka masu albarka, inganci da dourewa.

“Ba kawai don gine-gine da manyan ayyukan ba, har ma don ayyukan jin dadi da walwalar jama’a, ayyukan kiwon lafiya, ilimi da ayyuka a fannonin kiyaye tsaron jama’a don taimaka wa masu karamin karfi da masu fama da talauci,” Edun ya shaida.

LABARAI MASU NASABA

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

Zan Tabbatar Ana Tafiyar Da Ayyuka A Tashoshin Jiragen Ruwa A Afrika Ta Yamma —Dantsoho

A nasa bangaren, ministan kasafi da tsare-tsaren tattalin arziki, Sanata Atiku Bagudu ya tunatar da ‘yan majalisar yunkurin ciwo bashi tiriliyan 35.5 a kasafin 2024, da farko an yi nufin sanar da gibin tiriliyan 9.7.

“Duk da tsare-tsaren kudaden shiga ya zarta na wasu hukumomin samar da kudaden shiga, har yanzu akwai bukatar gwamnati ta karbo rancen kudade don gudanar da kasafin kudin yadda ya kamata, musamman ta fuskar rabe-rabe da samar da ayyukan yi ga marasa galihu.

“Muna da tsarin hangen nesa na ci gaba na dogon lokaci na 2050,” in ji Bagudu.

Kazalika, shugaban hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa (EFCC), Ola Olukoyede, ya shaida wa kwamitin cewa hukumarsa ta kwato sama da naira biliyan 197 daga watan Janairun 2024,

Ya lura cewa idan gwamnati ta yi aiki tukuru kuma ta samu tarin abubuwan da ake bukata, kasar za ta samu isassun kudaden da za ta kashe a kasafin kudin.

Babban Kwanturolan Hukumar Kwastam ta Nijeriya, Bashir Adeniyi, a cikin jawabinsa, ya bayyana cewa hukumar ta kwastam ta tara naira tiriliyan 5.352 na kudaden shiga fiye da naira tiriliyan 5.09 da aka yi niyyar yi a kasafin kudin shekarar 2024.

Ya ci gaba da cewa, naira tiriliyan 6.3 an yi niyya ne a matsayin kudaden shiga da aka yi hasashen za a samu a shekarar 2025, wanda kasha 10 daga ciki zai kasance abin da ake sa ran samun kudaden shiga a shekarar 2026 da karin kashi 10 na kasafin kudin shekarar 2027.

A nasa jawabin, babban jami’in gudanarwa na rukunin kamfanin man fetur na Nijeriya (NNPCL), Mele Kyari, ya ce kamfanin ya zarce kudaden shiga na naira tiriliyan 12.3 da aka yi hasashen za a iya samu a shekarar 2024, inda ya riga ya tara naira tiriliyan 13.1.

Har ila yau, shugaban hukumar tara haraji ta kasa FIRS, Zacch Adedeji, a nasa jawabin, ya sanar da kwamitocin hadin gwiwa cewa FIRS ta zarce kudaden shiga da aka yi niyya a sassa daban-daban na haraji.

ShareTweetSendShare

MASU ALAKA

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA
Tattalin Arziki

Tinubu Ya Amince A Fara Aikin Tashoshin Jiragen Ruwa Na Apapa Da Kalaba Da Fatakwal Da Warri — NPA

October 17, 2025
A Zango Mai Zuwa Za A Fara Aikin Dala Miliyan Daya A Tashar Jirgin Ruwa Ta Legas – Dantsoho
Tattalin Arziki

Zan Tabbatar Ana Tafiyar Da Ayyuka A Tashoshin Jiragen Ruwa A Afrika Ta Yamma —Dantsoho

October 17, 2025
sallah
Tattalin Arziki

Gwamnatin Tarayya Ta Bukaci’ Yan Nijeriya Su Rika Sayen Kayan Da Aka Sarrafa A Gida

October 11, 2025
Next Post
Kidayar Jama’a Da Harkar Lafiya

Kidayar Jama'a Da Harkar Lafiya

LABARAI MASU NASABA

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

Kano Derby: Barau FC Ta Doke Kano Pillars A Karon Farko A Tarihin Gamuwarsu

October 19, 2025
Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

Binciken CGTN: An Fitar Da Sakamakon Jin Ra’ayin Jama’a Dangane Da Cikakken Zama Na 4 Na Kwamitin Kolin JKS Na 20

October 19, 2025
Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

Arewa Ta Samu Kashi 56% Na Muƙaman Gwamnatin Tinubu — Shugaban FCC

October 19, 2025
Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

Xi Jinping Ya Mika Sakon Taya Cheng Li-wun Murnar Zama Shugabar Jam’iyyar KMT Ta Kasar Sin

October 19, 2025
Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

Ɗan Jarida Ibrahim Ɗan’uwa Rano Ya Shaƙi Iskar Ƴanci Bayan Tsare Shi

October 19, 2025
Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

Tie Ning Ta Halarci Bikin Bude Taron Karawa Juna Sani Na ‘Yan Majalisun Dokokin Kasashen Afirka

October 19, 2025
Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

Ƴansanda Sun Kama Ɗan Jarida A Kano Bisa Zargin Ɓata Suna

October 19, 2025
Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

Amfanin Yawan Shan Ruwa Da Kuma Illolin Rashin Yawan Sha

October 19, 2025
Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

Xinjiang Ta Janyo Karin Jari A Rubu’i Uku Na Farkon Shekarar Nan

October 19, 2025
Yadda Shagwaɓa Kananan Yara Da Kudi Ke Shafar Tarbiyyarsu

Yadda Shagwaɓa Kananan Yara Da Kudi Ke Shafar Tarbiyyarsu

October 19, 2025

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.

No Result
View All Result
  • Gida
  • Labarai
    • Manyan Labarai
    • Kananan Labarai
    • Masarautu
    • Bakon Marubuci
    • Dausayin Musulunci
    • Daga Kasar Sin
    • Nishadi
    • Noma Da Kiwo
    • Sana’a Sa’a
    • Tambarin Dimokuradiyya
    • Taskira
    • Daga Birnin Sin
    • Ado Da Kwalliya
  • Siyasa
  • Wasanni
  • Al’adu
  • Al’ajabi
  • Labaran Kasuwanci
  • Karanta cikin Turanci

© 2025 Leadership Media Group - All Right Reserved.